ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Wednesday, September 9, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Yadda Aka Gudanar Da Taron Ranar Hausa Ta Duniya A Masarautar Daura

by El-Zaharadeen Umar and Sulaiman
1 year ago
Daura

Taron ranar hausa ta duniya taro da majalisar dinkin duniya ta ware duk ranar 26 ga watan Agusta domin raya ta a duk fadin duniya.

 

To, sai a wannan karon taron ya sam u tagomashi inda masarautar Daura hadin gwiwa da gwamnatin jihar Katsina suka shirya shi domin bunkasa harshen Hausa da kuma Hausawa.

ADVERTISEMENT
  • Ranar Hausa: Masana Sun Bayyana Bunkasa Da Tasirin Harshen A Duniya
  • Shugaban NPA, Dantsoho Ya Zama Mataimakin Shugaban Kungiyar Tashoshin Ruwa Ta Duniya

Taken taron na wannan shekara ta 2025 shi ne “yin amfani da harshen Hausa wajen wanzar da zaman lafiya” kamar yadda aka bayyana tun kafin wannan rana.

 

LABARAI MASU NASABA

Sojoji Sun Dakile Hare-Hare, Sun Ceto Mutane 12 A Zamfara

‘Yan Bindiga Sun Kashe 2, Sun Yi Garkuwa Da 26 A Kaduna

Masu shirya taron sun dauki lokacin ana shirye-shiryen garin taron ta yi armashi da kuma nasara musamman saboda gayyato baki da aka yi daga makwabciyar kasar wato jamhuriyar Nijar.

 

Kasancewar masarautar Daura na da alaka da aka al’adun gargajiya an shirya kasaitaiccen bikin wanda ya burge mahalarta taron musamman baki.

 

Masu shirya taron sun kara da cewa dalilin da ya sa suka zabi masarautar Daura domin shirya wannan taron shine saboda kasancewar Daura tushen Hausa da al’adu hausawa.

Daura

Haka kuma an shirya wani tattaki daga Katsina domin zuwa Daura karkashin hukumar raya al’adu ta jihar Katsina inda aka shafe kwana biyu ana tafiya akan dawakai zuwa garin na Daura duk a cikin shirye-shiryen bikin ranar Hausa ta duniya.

 

Daga cikin manyan bakin da suka halarci wannan sun hada da gwamnan mulkin Soji na jihar Damagaram Kanal Muhammad Sani Massallaci ya jagoranta tare da mai martaba Sarkin Damagaram Sultan Abubakar Umar Sanda

 

An fara bude taron addu’a sannan fara baje kolin al’adu da sana’o’in Hausawa inda aka fara shakatawa da wanzamai bayan sun nuna ta so bajintar da kwanji da kuma makera wadanda suka yi wasan wuta a gaban dubun dubatar jama’ar da suka halarci taron.

 

Kazalika an yi wasan kokawa wanda shi ne ya kayayar da mahalarta taron, inda daga bisani aka shirya gagarumar daba ta hawan dawakai da ‘yan tauri da masu algaita da sauran su.

 

An shirya hawan dabar ne tamkar yadda masarautar Daura take shirya hawan Sallah ko Sallar Gani inda aka jero garuruwan Hausa bakwai da kuma kanne bakwai (tsohuwar banza bakwai)

 

Bayan kammala wannan daba da nuna al’adun gargajiya na bahaushe da hausawa an gudanar da jawabai daga manyan baki da suka halarci wannan taro na habaka harshen Hausa.

 

Sanata Ibrahim Ida Wazirin Katsina na daga cikin wadanda suka yi jawabi inda ya fara nuna mahimmancin da Majalisar dinkin Duniya ta baiwa harshen Hausa, al’adu da kuma adabin Hausawa a idun duniya.

 

Wazirin Katsina ya cigaba da bayanin cewa abu ne mai mahimmanci a fahimci cewa harshen Hausa na daga cikin manyan harsuna da ake amfani da su wajen magana, da sauran mu’amula ta yau da kullum.

 

Sanata Ibrahim Ida ya bayyana cewa yanzu an tabbatar da cewa harshen Hausa ya fi kowane harshe a Afrika yawan masu yin magana da shi da kuma yin huldodin rayuwa na yau da kullum.

 

Abdul Baki Jari na daya daga cikin wadanda suka assasa wannan rana ta ranar Hausa ta duniya wanda majalisar dinkin duniya ta amince a shekarar 2015.

 

Ya kara da cewa babban makasudin wannan taro shine domin a sada zumunci a tsakanin Hausawa da ke kasashe fiye da 25 a fadin duniya inda yanzu haka ana cigaba da irin wadannan bukukuwa.

 

Abdul Baki Jari ya nuna bukatar da ake da ita wajen gudanar da bincike akan makomar harshen Hausa da ke fuskantar kalubale a wasu kasashe.

 

Haka kuma ya nuna godiya da farin ciki da kasashe da suka halarci wannan taro musamman kasashen Camerou da Chadi da Ghana da Barkina Faso da sauran kasashen duniya wadanda aka ke tara ruwa kafin azo nan.

 

Shima da yake nasa jawabi wakilin shugaban kasar jamhuriyar Nijar kuma gwamnan jihar Damagaram Kanal Muhammad Sani Massallaci ya nuna godiya da fatan ga wadanda suka shirya wannan taro.

 

Kanal Massallaci ya bayyana cewa irin wadannan tarurruka shugaban kasar Nijar Janar Abdurrahaman Tiachni ke bukata domin ganin an hada kan hausawa wuri guda.

 

“Ya zama wajibi Hausawa su farka daga dogon barcin da suka yi, idan aka duba yanzu Hausawa sun fara barin gadon su, to ya zama dole a koma ma gado da al’adu irin wannan aka hada Iyaye da kakanni” in ji shi

 

Gwamnan Damagaram din ya yi fatan ya a rika amfani da irin wadannan tarurruka nan gaba domin kara dankon zumunci tsakanin kasashen Afrika inda nan ne Hausawa suka fi yawa.

 

Daga wadanda suka halarci wannan taro sun hada da gwamnan jihar Damagaram Kanal Muhammad Sani Massallaci da Mai martaba Sarkin Damagaram Sultan Abubakar Umar Sanda da Wazirin Katsina Sanata Ibrahim Ida da Sardaunan Kasar Hausa Mai tuta Hon. Alasan Ado Doguwa.

 

Sauran sun hada da wakilin gwamnan jihar Katsina kuma mai baiwa gwamna shawara akan harkokin masarautu Alhaji Usman Abba Jaye da sauran masu rike da masarautar da hukumomi.

Daura
El-Zaharadeen Umar
+ posts Bio
  • El-Zaharadeen Umar
    https://hausa.leadership.ng/author/el-zaharadeen-umar/
    Cutar Mashako:Yadda Yara Ke Mutuwar Bazata A Jihohin Katsina Da Kano
  • El-Zaharadeen Umar
    https://hausa.leadership.ng/author/el-zaharadeen-umar/
    Mauludin Annabi (SAW): Shugaba Tinubu Ya Nemi A Yi Addu’o’in Nasara Kan Matsalar Tsaro
  • El-Zaharadeen Umar
    https://hausa.leadership.ng/author/el-zaharadeen-umar/
    Shekaru 8 Cikin Raɗaɗi: Wani Bawan Allah Ya Samu Tiyata Kyauta Daga Gidauniyar Mangal
  • El-Zaharadeen Umar
    https://hausa.leadership.ng/author/el-zaharadeen-umar/
    Tinubu Ya Nemi Malamai Su Taimaka Wajen Yaƙi Da Ƴan Ta’adda
Daura
Sulaiman
+ posts Bio
  • Sulaiman
    Sojoji Sun Dakile Hare-Hare, Sun Ceto Mutane 12 A Zamfara
  • Sulaiman
    Batun AI Zai Fi Daukar Hankali A Bikin Baje Kolin Fasahar Zamani Ta Duniya Karo Na 5
  • Sulaiman
    Cinikin Wajen Sin Ya Ci Gaba Da Samun Bunkasa Cikin Sauri A Watanni Takwas Na Farkon Bana
  • Sulaiman
    ‘Yan Bindiga Sun Kashe 2, Sun Yi Garkuwa Da 26 A Kaduna

MASU ALAKA

Sojoji
Manyan Labarai

Sojoji Sun Dakile Hare-Hare, Sun Ceto Mutane 12 A Zamfara

September 9, 2026
'Yan Bindiga
Labarai

‘Yan Bindiga Sun Kashe 2, Sun Yi Garkuwa Da 26 A Kaduna

September 8, 2026
Yadda Taron Tattalin Arziki Da Zuba Jari Na Kwana Biyu Ya Gudana A Katsina
Labarai

Gwamna Radda Ya Gabatar Da Kasafin N828.6bn Na 2027

September 8, 2026
Next Post
Yaya Da Kani Sun Mutu A Cikin Ramin Masai A Kano

Yadda Aka Gudanar Da Bikin Ranar Hausa Ta Duniya A Kano

LABARAI MASU NASABA

Sojoji

Sojoji Sun Dakile Hare-Hare, Sun Ceto Mutane 12 A Zamfara

September 9, 2026
Batun AI Zai Fi Daukar Hankali A Bikin Baje Kolin Fasahar Zamani Ta Duniya Karo Na 5

Batun AI Zai Fi Daukar Hankali A Bikin Baje Kolin Fasahar Zamani Ta Duniya Karo Na 5

September 8, 2026
Gwamna Radda Ya Samu Goyon Bayan APC A Katsina Gabanin Zaɓen 2027

Gwamna Radda Ya Samu Goyon Bayan APC A Katsina Gabanin Zaɓen 2027

September 8, 2026
Cinikin Wajen Sin Ya Ci Gaba Da Samun Bunkasa Cikin Sauri A Watanni Takwas Na Farkon Bana

Cinikin Wajen Sin Ya Ci Gaba Da Samun Bunkasa Cikin Sauri A Watanni Takwas Na Farkon Bana

September 8, 2026
'Yan Bindiga

‘Yan Bindiga Sun Kashe 2, Sun Yi Garkuwa Da 26 A Kaduna

September 8, 2026
Binciken CGTN Ya Nuna Gamsuwa Da Yadda Baje Kolin CIFTIS Ke Shaida Karfin Gwiwar Sin A Fannin Kara Fadada Bude Kofa Bisa Babban Matsayi

Binciken CGTN Ya Nuna Gamsuwa Da Yadda Baje Kolin CIFTIS Ke Shaida Karfin Gwiwar Sin A Fannin Kara Fadada Bude Kofa Bisa Babban Matsayi

September 8, 2026
Yadda Taron Tattalin Arziki Da Zuba Jari Na Kwana Biyu Ya Gudana A Katsina

Gwamna Radda Ya Gabatar Da Kasafin N828.6bn Na 2027

September 8, 2026
Sin Za Ta Yi Aiki Tare Da Sassa Daban Daban Domin Mayar Da Fasahar AI Wata Dama Ta Cin Gajiya Mai Dorewa

Sin Za Ta Yi Aiki Tare Da Sassa Daban Daban Domin Mayar Da Fasahar AI Wata Dama Ta Cin Gajiya Mai Dorewa

September 8, 2026
Gwamnan Kebbi Ya Bayyana Shirin Sake Duba Albashin Malaman Firamare

Gwamna Idris Ya Rushe Majalisar Shugabannin Hukumar Zaɓe Ta Kebbi

September 8, 2026
Han Zheng Ya Halarci Baje Kolin CIFIT Karo Na 26 Tare Da Gabatar Da Jawabi

Han Zheng Ya Halarci Baje Kolin CIFIT Karo Na 26 Tare Da Gabatar Da Jawabi

September 8, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.