ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Wednesday, June 24, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Yadda Aka Gudanar Da Taron Ranar Hausa Ta Duniya A Masarautar Daura

by El-Zaharadeen Umar and Sulaiman
10 months ago
Daura

Taron ranar hausa ta duniya taro da majalisar dinkin duniya ta ware duk ranar 26 ga watan Agusta domin raya ta a duk fadin duniya.

 

To, sai a wannan karon taron ya sam u tagomashi inda masarautar Daura hadin gwiwa da gwamnatin jihar Katsina suka shirya shi domin bunkasa harshen Hausa da kuma Hausawa.

ADVERTISEMENT
  • Ranar Hausa: Masana Sun Bayyana Bunkasa Da Tasirin Harshen A Duniya
  • Shugaban NPA, Dantsoho Ya Zama Mataimakin Shugaban Kungiyar Tashoshin Ruwa Ta Duniya

Taken taron na wannan shekara ta 2025 shi ne “yin amfani da harshen Hausa wajen wanzar da zaman lafiya” kamar yadda aka bayyana tun kafin wannan rana.

 

LABARAI MASU NASABA

’Yansanda Sun Kama Wani Mutum da Harsasai 174 A Nasarawa

Sojoji Sun Kama Ɗan Fashi Da Makami A Taraba

Masu shirya taron sun dauki lokacin ana shirye-shiryen garin taron ta yi armashi da kuma nasara musamman saboda gayyato baki da aka yi daga makwabciyar kasar wato jamhuriyar Nijar.

 

Kasancewar masarautar Daura na da alaka da aka al’adun gargajiya an shirya kasaitaiccen bikin wanda ya burge mahalarta taron musamman baki.

 

Masu shirya taron sun kara da cewa dalilin da ya sa suka zabi masarautar Daura domin shirya wannan taron shine saboda kasancewar Daura tushen Hausa da al’adu hausawa.

Daura

Haka kuma an shirya wani tattaki daga Katsina domin zuwa Daura karkashin hukumar raya al’adu ta jihar Katsina inda aka shafe kwana biyu ana tafiya akan dawakai zuwa garin na Daura duk a cikin shirye-shiryen bikin ranar Hausa ta duniya.

 

Daga cikin manyan bakin da suka halarci wannan sun hada da gwamnan mulkin Soji na jihar Damagaram Kanal Muhammad Sani Massallaci ya jagoranta tare da mai martaba Sarkin Damagaram Sultan Abubakar Umar Sanda

 

An fara bude taron addu’a sannan fara baje kolin al’adu da sana’o’in Hausawa inda aka fara shakatawa da wanzamai bayan sun nuna ta so bajintar da kwanji da kuma makera wadanda suka yi wasan wuta a gaban dubun dubatar jama’ar da suka halarci taron.

 

Kazalika an yi wasan kokawa wanda shi ne ya kayayar da mahalarta taron, inda daga bisani aka shirya gagarumar daba ta hawan dawakai da ‘yan tauri da masu algaita da sauran su.

 

An shirya hawan dabar ne tamkar yadda masarautar Daura take shirya hawan Sallah ko Sallar Gani inda aka jero garuruwan Hausa bakwai da kuma kanne bakwai (tsohuwar banza bakwai)

 

Bayan kammala wannan daba da nuna al’adun gargajiya na bahaushe da hausawa an gudanar da jawabai daga manyan baki da suka halarci wannan taro na habaka harshen Hausa.

 

Sanata Ibrahim Ida Wazirin Katsina na daga cikin wadanda suka yi jawabi inda ya fara nuna mahimmancin da Majalisar dinkin Duniya ta baiwa harshen Hausa, al’adu da kuma adabin Hausawa a idun duniya.

 

Wazirin Katsina ya cigaba da bayanin cewa abu ne mai mahimmanci a fahimci cewa harshen Hausa na daga cikin manyan harsuna da ake amfani da su wajen magana, da sauran mu’amula ta yau da kullum.

 

Sanata Ibrahim Ida ya bayyana cewa yanzu an tabbatar da cewa harshen Hausa ya fi kowane harshe a Afrika yawan masu yin magana da shi da kuma yin huldodin rayuwa na yau da kullum.

 

Abdul Baki Jari na daya daga cikin wadanda suka assasa wannan rana ta ranar Hausa ta duniya wanda majalisar dinkin duniya ta amince a shekarar 2015.

 

Ya kara da cewa babban makasudin wannan taro shine domin a sada zumunci a tsakanin Hausawa da ke kasashe fiye da 25 a fadin duniya inda yanzu haka ana cigaba da irin wadannan bukukuwa.

 

Abdul Baki Jari ya nuna bukatar da ake da ita wajen gudanar da bincike akan makomar harshen Hausa da ke fuskantar kalubale a wasu kasashe.

 

Haka kuma ya nuna godiya da farin ciki da kasashe da suka halarci wannan taro musamman kasashen Camerou da Chadi da Ghana da Barkina Faso da sauran kasashen duniya wadanda aka ke tara ruwa kafin azo nan.

 

Shima da yake nasa jawabi wakilin shugaban kasar jamhuriyar Nijar kuma gwamnan jihar Damagaram Kanal Muhammad Sani Massallaci ya nuna godiya da fatan ga wadanda suka shirya wannan taro.

 

Kanal Massallaci ya bayyana cewa irin wadannan tarurruka shugaban kasar Nijar Janar Abdurrahaman Tiachni ke bukata domin ganin an hada kan hausawa wuri guda.

 

“Ya zama wajibi Hausawa su farka daga dogon barcin da suka yi, idan aka duba yanzu Hausawa sun fara barin gadon su, to ya zama dole a koma ma gado da al’adu irin wannan aka hada Iyaye da kakanni” in ji shi

 

Gwamnan Damagaram din ya yi fatan ya a rika amfani da irin wadannan tarurruka nan gaba domin kara dankon zumunci tsakanin kasashen Afrika inda nan ne Hausawa suka fi yawa.

 

Daga wadanda suka halarci wannan taro sun hada da gwamnan jihar Damagaram Kanal Muhammad Sani Massallaci da Mai martaba Sarkin Damagaram Sultan Abubakar Umar Sanda da Wazirin Katsina Sanata Ibrahim Ida da Sardaunan Kasar Hausa Mai tuta Hon. Alasan Ado Doguwa.

 

Sauran sun hada da wakilin gwamnan jihar Katsina kuma mai baiwa gwamna shawara akan harkokin masarautu Alhaji Usman Abba Jaye da sauran masu rike da masarautar da hukumomi.

Daura
El-Zaharadeen Umar
+ posts Bio
  • El-Zaharadeen Umar
    https://hausa.leadership.ng/author/el-zaharadeen-umar/
    Mutum 1,000 Daga Jam’iyyar ADC Sun Koma PDP A Jihar Katsina
  • El-Zaharadeen Umar
    https://hausa.leadership.ng/author/el-zaharadeen-umar/
    Tinubu Ya Amince Da Ɗaukar Ma’aikatan Gandun Daji 1,000 Domin Matsalolin Tsaro A Katsina
  • El-Zaharadeen Umar
    https://hausa.leadership.ng/author/el-zaharadeen-umar/
    Matsalar Tsaro:Yadda Sabbin Matakan Gwamnati Ke Shafar Walwalar Al’ummar Jihar Katsina
  • El-Zaharadeen Umar
    https://hausa.leadership.ng/author/el-zaharadeen-umar/
    Garkuwa Da Mutane Na Barazana Ga Dalibai Miliyan 1.9 Masu Jarrabawar WAEC A Sassan Nijeriya
Daura
Sulaiman
+ posts Bio
  • Sulaiman
    Ya Kamata Sin Da Birtaniya Su Yi Aiki Tare Don Ci Gaba Da Inganta Dangantakarsu
  • Sulaiman
    Firaministan Sin Ya Jaddada Muhimmancin Kara Azamar Bunkasa Kirar Kayayyakin Aikin Masana’antu Na Zamani
  • Sulaiman
    Gombe Ta Zabge Farashin Taki Da Kashi 50 Cikin 100
  • Sulaiman
    Wang Yi Ya Gana Da Babban Sakataren Majalisar Tsaron Masar Da Ministan Fadar Gwamnatin Afirka Ta Kudu A Indiya

MASU ALAKA

‘Yansanda Sun Kama Ɗan Bindiga Da Kuɗin Fansa Naira Miliyan 5 A Delta
Manyan Labarai

’Yansanda Sun Kama Wani Mutum da Harsasai 174 A Nasarawa

June 24, 2026
Sojoji Sun Kama Ɗan Fashi Da Makami A Taraba
Labarai

Sojoji Sun Kama Ɗan Fashi Da Makami A Taraba

June 24, 2026
An Kashe Mutum 2, 8 Sun Jikkata Yayin Rikici A Bauchi
Labarai

An Kashe Mutum 2, 8 Sun Jikkata Yayin Rikici A Bauchi

June 24, 2026
Next Post
Yaya Da Kani Sun Mutu A Cikin Ramin Masai A Kano

Yadda Aka Gudanar Da Bikin Ranar Hausa Ta Duniya A Kano

LABARAI MASU NASABA

Trump Ne Zai Jagoranci Bayar Da Kofin Duniya A Wasan Ƙarshe – Infantino

Trump Ne Zai Jagoranci Bayar Da Kofin Duniya A Wasan Ƙarshe – Infantino

June 24, 2026
‘Yansanda Sun Kama Ɗan Bindiga Da Kuɗin Fansa Naira Miliyan 5 A Delta

’Yansanda Sun Kama Wani Mutum da Harsasai 174 A Nasarawa

June 24, 2026
Sojoji Sun Kama Ɗan Fashi Da Makami A Taraba

Sojoji Sun Kama Ɗan Fashi Da Makami A Taraba

June 24, 2026
An Kashe Mutum 2, 8 Sun Jikkata Yayin Rikici A Bauchi

An Kashe Mutum 2, 8 Sun Jikkata Yayin Rikici A Bauchi

June 24, 2026
Tsohon Shugaban APC Na Kebbi Ya Rasu A Hannun ’Yan Bindiga

Tsohon Shugaban APC Na Kebbi Ya Rasu A Hannun ’Yan Bindiga

June 24, 2026
Ya Kamata Sin Da Birtaniya Su Yi Aiki Tare Don Ci Gaba Da Inganta Dangantakarsu

Ya Kamata Sin Da Birtaniya Su Yi Aiki Tare Don Ci Gaba Da Inganta Dangantakarsu

June 23, 2026
Firaministan Sin Ya Jaddada Muhimmancin Kara Azamar Bunkasa Kirar Kayayyakin Aikin Masana’antu Na Zamani

Firaministan Sin Ya Jaddada Muhimmancin Kara Azamar Bunkasa Kirar Kayayyakin Aikin Masana’antu Na Zamani

June 23, 2026
Gombe Ta Zabge Farashin Taki Da Kashi 50 Cikin 100

Gombe Ta Zabge Farashin Taki Da Kashi 50 Cikin 100

June 23, 2026
Wang Yi Ya Gana Da Babban Sakataren Majalisar Tsaron Masar Da Ministan Fadar Gwamnatin Afirka Ta Kudu A Indiya

Wang Yi Ya Gana Da Babban Sakataren Majalisar Tsaron Masar Da Ministan Fadar Gwamnatin Afirka Ta Kudu A Indiya

June 23, 2026
‘Yansanda Sun Kashe Masu Garkuwa Da Mutane 8, Sun Kubutar Da Mutane 3 A Jihar Bauchi

’Yansanda Sun Kama Mutane 57 Da Ake Zargi Da Ayyukan Ta’addanci A Adamawa

June 23, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.