ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Thursday, June 25, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Yadda Na Sayar Da Kadarori Na Don Ɗaukar Nauyin Ɗalibai A Ƙasashen Waje – Kwankwaso

by Sulaiman
6 months ago

Tsohon gwamnan jihar Kano kuma shugaban tafiyar Kwankwasiyya, Sanata Rabiu Musa Kwankwaso, ya tuna yadda ya sayar da kadarorinsa don ɗaukar nauyin matasa maza da mata 370 daga jihar Kano don yin karatu a kasashen waje.

 

A yayin da wadanda suka ci gajiyar shirin tallafin karatu na Kwankwasiyya suka gudanar da taron su na shekara-shekara don godiya ga wannan tallafin, Kwankwaso ya bayyana ilimi a matsayin gado mafi dorewa da kowane shugaba zai iya gadar wa al’umma.

ADVERTISEMENT
  • Mutum Biyu Sun Rasu Yayin Rikici Tsakanin Jami’an Tsaro Da Matasa A Katsina
  • Sin Za Ta Aiwatar Da Manufar Harkokin Kudi Mai Inganci A 2026

Da yake jawabi a wurin taron mai tarihi, Jagoran ya gode wa Allah Madaukakin Sarki da ya nuna masa irin wannan “rana mai tarihi ga jihar Kano da Nijeriya,” yana mai lura da cewa taron ya hada jigogi a fannin ilimin zamani da aka dauki nauyinsu tsawon kusan shekaru 25.

 

LABARAI MASU NASABA

‘Yan Nijeriya Ba Sa Bukatar ‘Yan Jarida Su Faɗa Musu Suna Jin Yunwa’ — Atiku

Zargin Ɓata Suna: Kwankwaso Ya Yi Barazanar Neman Diyyar Naira Biliyan 10 Kan Wani Malamin Coci

“Ina tuna yawancinku a baya. Wasu daga cikinku sun yi kama da wadanda suka fito kai tsaye daga kauyuka. A yau, ina ganin kwarin gwiwa, kwarewa har ma wasunku sun manyanta, har da furfura a kansu” in ji shi

 

A cewar wata sanarwa da Dakta Mansur Hassan ya fitar, Kwankwaso, wanda ya mulki jihar Kano tsawon shekaru takwas, ya ce taron ya jaddada muhimmancin shugabanci, dorewa da kuma saka hannun jari na dogon lokaci a fannin rayuwar dan adam.

 

Ya bayyana cewa bayan babban zaben 2019, lokacin da gwamnati ta dakatar da daukar nauyin daliban kasashen waje, shi da kansa ya ci gaba da wannan shiri ta hanyar Gidauniyar Ci Gaban Kwankwasiyya (KDF).

 

Kwankwaso ya kara da cewa, bayan malaman da gidauniyar ta dauki nauyinsu, shirin ya ci gaba da tallafa wa dalibai sama da 3,000 cikin shekaru hudu don yin karatu a kasashe 14 a Turai, Asiya, Afirka da Gabas ta Tsakiya.

 

Shirin ya samar da likitoci, injiniyoyi, matukan jirgi da kwararru a duniya. Bayanan da ake da su daga KDF, sun nuna cewa shirin ya zuwa yanzu ya samar da daruruwan likitoci da kwararru da ke aiki a asibitocin koyarwa a Nijeriya da kasashen waje; kwararrun matukan jirgi da ma’aikata a filin jiragen sama; dubban injiniyoyi, kwararru a fannin fasahar sadarwa; da kuma malamai da masu bincike, tare da sama da masu digirin digirgir 300 da aka bayyana a taron.

 

Ta kuma samar da masana magunguna, masu gine-gine, masana tattalin arziki, lauyoyi, kwararru kan manufofin jama’a da masu aikin ci gaba da ke aiki a fadin Nijeriya, Afirka, Turai, Arewacin Amurka da Gabas ta Tsakiya.

 

Kwankwaso ya bayyana cewa manufar gidauniyar ba wai kawai daukar nauyin malamai ba ne, har ma da jagorantar su, bin diddigin su da kuma hada su cikin ayyukan gwamnati, shugabanci da ci gaban kasa.

Sulaiman
+ postsBio
  • Sulaiman
    Dokar Sin Ta Gurfanar Da Masu Rajin Ballewar Kabilun Kasar Da Ke Kasashen Waje Ta Dace
  • Sulaiman
    ’Yan Kasuwa Na Kasashen Waje Sun Yaba Wa Yanayin Kasuwanci Na Sin
  • Sulaiman
    Yadda Uba Sani Ya Farfaɗo Da Asibitin Da Aka Yi Watsi Da Shi Tsawon Shekaru 40 – Hakimin Makarfi
  • Sulaiman
    Dandalin DAVOS Na Bana: Fage Ne Da “Kirkire-Kirkiren Sin” Ya Sadu Da “Kyakkyawan Fatan Afirka”

MASU ALAKA

Zan Ware 10bn Don Inganta Ilimin Matasa Idan Na Ci Zabe – Atiku
Manyan Labarai

‘Yan Nijeriya Ba Sa Bukatar ‘Yan Jarida Su Faɗa Musu Suna Jin Yunwa’ — Atiku

June 25, 2026
Yadda Na Sayar Da Kadarori Na Don Ɗaukar Nauyin Ɗalibai A Ƙasashen Waje – Kwankwaso
Manyan Labarai

Zargin Ɓata Suna: Kwankwaso Ya Yi Barazanar Neman Diyyar Naira Biliyan 10 Kan Wani Malamin Coci

June 24, 2026
Tinubu Ya Gaza Wajen Magance Matsalar Tsaro A Nijeriya — Atiku
Manyan Labarai

Atiku Ya Soki Tsare El-Rufai, Ya Ce Sharuɗan Belinsa Sun Yi Tsauri

June 24, 2026
Next Post
Majalisa Ta Nemi Tinubu Ya Canza Dabarun Yaƙi Da Ta’addanci Don Kawo Ƙarshen Kashe-kashe

'Yan Majalisar Wakilai Sun Nemi A Dakatar Da Aiwatar Da Dokokin Haraji

LABARAI MASU NASABA

Maroko Ta Zama Ƙasa Ta Farko Daga Afirka Da Ta Tsallaka Zuwa Zagaye Na 32 A Gasar Kofin Duniya

Maroko Ta Zama Ƙasa Ta Farko Daga Afirka Da Ta Tsallaka Zuwa Zagaye Na 32 A Gasar Kofin Duniya

June 25, 2026
Zan Ware 10bn Don Inganta Ilimin Matasa Idan Na Ci Zabe – Atiku

‘Yan Nijeriya Ba Sa Bukatar ‘Yan Jarida Su Faɗa Musu Suna Jin Yunwa’ — Atiku

June 25, 2026
Dokar Sin Ta Gurfanar Da Masu Rajin Ballewar Kabilun Kasar Da Ke Kasashen Waje Ta Dace

Dokar Sin Ta Gurfanar Da Masu Rajin Ballewar Kabilun Kasar Da Ke Kasashen Waje Ta Dace

June 24, 2026
’Yan Kasuwa Na Kasashen Waje Sun Yaba Wa Yanayin Kasuwanci Na Sin

’Yan Kasuwa Na Kasashen Waje Sun Yaba Wa Yanayin Kasuwanci Na Sin

June 24, 2026
Yadda Uba Sani Ya Farfaɗo Da Asibitin Da Aka Yi Watsi Da Shi Tsawon Shekaru 40 – Hakimin Makarfi

Yadda Uba Sani Ya Farfaɗo Da Asibitin Da Aka Yi Watsi Da Shi Tsawon Shekaru 40 – Hakimin Makarfi

June 24, 2026
Dandalin DAVOS Na Bana: Fage Ne Da “Kirkire-Kirkiren Sin” Ya Sadu Da “Kyakkyawan Fatan Afirka”

Dandalin DAVOS Na Bana: Fage Ne Da “Kirkire-Kirkiren Sin” Ya Sadu Da “Kyakkyawan Fatan Afirka”

June 24, 2026
Binciken CGTN: Amfanarwa A Aikace Shi Ne Nagartaccen Ma’aunin Tantance Ainihin Kimar Sabbin Fasahohi

Binciken CGTN: Amfanarwa A Aikace Shi Ne Nagartaccen Ma’aunin Tantance Ainihin Kimar Sabbin Fasahohi

June 24, 2026
Kasar Sin Na Kara Zama Babban Ginshikin Ci Gaban Tattalin Arzikin Duniya Na Gaba

Kasar Sin Na Kara Zama Babban Ginshikin Ci Gaban Tattalin Arzikin Duniya Na Gaba

June 24, 2026
Tsaro: Dasuki Ya Bukaci Tinubu Ya Gyara Alaka Da Nijar Domin Kare Iyakokin Arewa-Maso-Yamma

Tsaro: Dasuki Ya Bukaci Tinubu Ya Gyara Alaka Da Nijar Domin Kare Iyakokin Arewa-Maso-Yamma

June 24, 2026
Sabbin Ministoci

Kafa ‘Yansandan Jihohi: Majalisa Ta Amince Da Tsarin ‘Yar Tinƙe Wajen Kaɗa Ƙuri’a 

June 24, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.