ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Thursday, June 4, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Yadda Na Sayar Da Kadarori Na Don Ɗaukar Nauyin Ɗalibai A Ƙasashen Waje – Kwankwaso

by Sulaiman
5 months ago

Tsohon gwamnan jihar Kano kuma shugaban tafiyar Kwankwasiyya, Sanata Rabiu Musa Kwankwaso, ya tuna yadda ya sayar da kadarorinsa don ɗaukar nauyin matasa maza da mata 370 daga jihar Kano don yin karatu a kasashen waje.

 

A yayin da wadanda suka ci gajiyar shirin tallafin karatu na Kwankwasiyya suka gudanar da taron su na shekara-shekara don godiya ga wannan tallafin, Kwankwaso ya bayyana ilimi a matsayin gado mafi dorewa da kowane shugaba zai iya gadar wa al’umma.

ADVERTISEMENT
  • Mutum Biyu Sun Rasu Yayin Rikici Tsakanin Jami’an Tsaro Da Matasa A Katsina
  • Sin Za Ta Aiwatar Da Manufar Harkokin Kudi Mai Inganci A 2026

Da yake jawabi a wurin taron mai tarihi, Jagoran ya gode wa Allah Madaukakin Sarki da ya nuna masa irin wannan “rana mai tarihi ga jihar Kano da Nijeriya,” yana mai lura da cewa taron ya hada jigogi a fannin ilimin zamani da aka dauki nauyinsu tsawon kusan shekaru 25.

 

LABARAI MASU NASABA

Arsenal Na Dab Da Ɗaukar Jeremy Monga Daga Leicester City

Sarki Sanusi II Ya Tuɓe Rawanin Mai Unguwar Rikadawa Kan Badaƙalar Fili

“Ina tuna yawancinku a baya. Wasu daga cikinku sun yi kama da wadanda suka fito kai tsaye daga kauyuka. A yau, ina ganin kwarin gwiwa, kwarewa har ma wasunku sun manyanta, har da furfura a kansu” in ji shi

 

A cewar wata sanarwa da Dakta Mansur Hassan ya fitar, Kwankwaso, wanda ya mulki jihar Kano tsawon shekaru takwas, ya ce taron ya jaddada muhimmancin shugabanci, dorewa da kuma saka hannun jari na dogon lokaci a fannin rayuwar dan adam.

 

Ya bayyana cewa bayan babban zaben 2019, lokacin da gwamnati ta dakatar da daukar nauyin daliban kasashen waje, shi da kansa ya ci gaba da wannan shiri ta hanyar Gidauniyar Ci Gaban Kwankwasiyya (KDF).

 

Kwankwaso ya kara da cewa, bayan malaman da gidauniyar ta dauki nauyinsu, shirin ya ci gaba da tallafa wa dalibai sama da 3,000 cikin shekaru hudu don yin karatu a kasashe 14 a Turai, Asiya, Afirka da Gabas ta Tsakiya.

 

Shirin ya samar da likitoci, injiniyoyi, matukan jirgi da kwararru a duniya. Bayanan da ake da su daga KDF, sun nuna cewa shirin ya zuwa yanzu ya samar da daruruwan likitoci da kwararru da ke aiki a asibitocin koyarwa a Nijeriya da kasashen waje; kwararrun matukan jirgi da ma’aikata a filin jiragen sama; dubban injiniyoyi, kwararru a fannin fasahar sadarwa; da kuma malamai da masu bincike, tare da sama da masu digirin digirgir 300 da aka bayyana a taron.

 

Ta kuma samar da masana magunguna, masu gine-gine, masana tattalin arziki, lauyoyi, kwararru kan manufofin jama’a da masu aikin ci gaba da ke aiki a fadin Nijeriya, Afirka, Turai, Arewacin Amurka da Gabas ta Tsakiya.

 

Kwankwaso ya bayyana cewa manufar gidauniyar ba wai kawai daukar nauyin malamai ba ne, har ma da jagorantar su, bin diddigin su da kuma hada su cikin ayyukan gwamnati, shugabanci da ci gaban kasa.

Sulaiman
+ postsBio
  • Sulaiman
    Ana Gudanar Da Taron Masana Ilmin Harkokin Kasar Sin Karo Na Uku
  • Sulaiman
    Sin: Ya Kamata Tarayyar Turai Ta Dubi Huldar Tattalin Arziki Da Ciniki Tsakaninta Da Sin Bisa Daidaito
  • Sulaiman
    An Gudanar Da Taron “Tattaunawar Magadan Garuruwa Na Duniya Na 2026” A Birnin Beijing
  • Sulaiman
    2027: Kasancewa Ɗan Arewa Kaɗai Ba Zai Tabbatar Da Samun Ƙuri’u Ba – Baba-Ahmed

MASU ALAKA

Arsenal Na Dab Da Ɗaukar Jeremy Monga Daga Leicester City
Wasanni

Arsenal Na Dab Da Ɗaukar Jeremy Monga Daga Leicester City

June 4, 2026
Sarki Sanusi II Ya Tuɓe Rawanin Mai Unguwar Rikadawa Kan Badaƙalar Fili
Manyan Labarai

Sarki Sanusi II Ya Tuɓe Rawanin Mai Unguwar Rikadawa Kan Badaƙalar Fili

June 4, 2026
Tambuwal Ya Jajanta Wa Waɗanda Harin ’Yan Bindiga Ya Shafa A Sokoto, Ya Nemi A Ƙara Tsaro
Manyan Labarai

Tambuwal Ya Jajanta Wa Waɗanda Harin ’Yan Bindiga Ya Shafa A Sokoto, Ya Nemi A Ƙara Tsaro

June 3, 2026
Next Post
Majalisa Ta Nemi Tinubu Ya Canza Dabarun Yaƙi Da Ta’addanci Don Kawo Ƙarshen Kashe-kashe

'Yan Majalisar Wakilai Sun Nemi A Dakatar Da Aiwatar Da Dokokin Haraji

Discussion about this post

LABARAI MASU NASABA

Ana Gudanar Da Taron Masana Ilmin Harkokin Kasar Sin Karo Na Uku

Ana Gudanar Da Taron Masana Ilmin Harkokin Kasar Sin Karo Na Uku

June 4, 2026
Sin: Ya Kamata Tarayyar Turai Ta Dubi Huldar Tattalin Arziki Da Ciniki Tsakaninta Da Sin Bisa Daidaito

Sin: Ya Kamata Tarayyar Turai Ta Dubi Huldar Tattalin Arziki Da Ciniki Tsakaninta Da Sin Bisa Daidaito

June 4, 2026
Arsenal Na Dab Da Ɗaukar Jeremy Monga Daga Leicester City

Arsenal Na Dab Da Ɗaukar Jeremy Monga Daga Leicester City

June 4, 2026
An Gudanar Da Taron “Tattaunawar Magadan Garuruwa Na Duniya Na 2026” A Birnin Beijing

An Gudanar Da Taron “Tattaunawar Magadan Garuruwa Na Duniya Na 2026” A Birnin Beijing

June 4, 2026
Atiku Ne Ya Fi Dacewa Da Tikitin Takara A ADC Amma Ya Kamata Ya Janye — Baba-Ahmed

2027: Kasancewa Ɗan Arewa Kaɗai Ba Zai Tabbatar Da Samun Ƙuri’u Ba – Baba-Ahmed

June 4, 2026
Gwamnatin Tarayya Ta Mayar Da Ofishin NAGGW Zuwa Kano Domin Yaƙi Da Hamada

Gwamnatin Tarayya Ta Mayar Da Ofishin NAGGW Zuwa Kano Domin Yaƙi Da Hamada

June 4, 2026
Mambobin NYSC 4, Soja da Mutum 1 Sun Rasu A Hatsarin Mota A Adamawa

Mambobin NYSC 4, Soja da Mutum 1 Sun Rasu A Hatsarin Mota A Adamawa

June 4, 2026
Sarki Sanusi II Ya Tuɓe Rawanin Mai Unguwar Rikadawa Kan Badaƙalar Fili

Sarki Sanusi II Ya Tuɓe Rawanin Mai Unguwar Rikadawa Kan Badaƙalar Fili

June 4, 2026
Tawagar Masanan Dakile Yaduwar Cututtuka Ta Sin Ta Isa DR Congo

Tawagar Masanan Dakile Yaduwar Cututtuka Ta Sin Ta Isa DR Congo

June 3, 2026
Uba Sani Ya Sanya Hannu Kan Sabbin Dokoki A Bangaren Sauya Fannin Wuta, Noma, Da Muhalli

Uba Sani Ya Sanya Hannu Kan Sabbin Dokoki A Bangaren Sauya Fannin Wuta, Noma, Da Muhalli

June 3, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.