ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Friday, July 17, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Yadda Na Sayar Da Kadarori Na Don Ɗaukar Nauyin Ɗalibai A Ƙasashen Waje – Kwankwaso

by Sulaiman
7 months ago

Tsohon gwamnan jihar Kano kuma shugaban tafiyar Kwankwasiyya, Sanata Rabiu Musa Kwankwaso, ya tuna yadda ya sayar da kadarorinsa don ɗaukar nauyin matasa maza da mata 370 daga jihar Kano don yin karatu a kasashen waje.

 

A yayin da wadanda suka ci gajiyar shirin tallafin karatu na Kwankwasiyya suka gudanar da taron su na shekara-shekara don godiya ga wannan tallafin, Kwankwaso ya bayyana ilimi a matsayin gado mafi dorewa da kowane shugaba zai iya gadar wa al’umma.

ADVERTISEMENT
  • Mutum Biyu Sun Rasu Yayin Rikici Tsakanin Jami’an Tsaro Da Matasa A Katsina
  • Sin Za Ta Aiwatar Da Manufar Harkokin Kudi Mai Inganci A 2026

Da yake jawabi a wurin taron mai tarihi, Jagoran ya gode wa Allah Madaukakin Sarki da ya nuna masa irin wannan “rana mai tarihi ga jihar Kano da Nijeriya,” yana mai lura da cewa taron ya hada jigogi a fannin ilimin zamani da aka dauki nauyinsu tsawon kusan shekaru 25.

 

LABARAI MASU NASABA

Gasar Kofin Duniya: Da Ƙarfinmu Muka Kawo Matakin Da Muke Yanzu – Messi

Bayan Ceto Daliban Oyo: Kallo Ya Koma Borno Da Yobe

“Ina tuna yawancinku a baya. Wasu daga cikinku sun yi kama da wadanda suka fito kai tsaye daga kauyuka. A yau, ina ganin kwarin gwiwa, kwarewa har ma wasunku sun manyanta, har da furfura a kansu” in ji shi

 

A cewar wata sanarwa da Dakta Mansur Hassan ya fitar, Kwankwaso, wanda ya mulki jihar Kano tsawon shekaru takwas, ya ce taron ya jaddada muhimmancin shugabanci, dorewa da kuma saka hannun jari na dogon lokaci a fannin rayuwar dan adam.

 

Ya bayyana cewa bayan babban zaben 2019, lokacin da gwamnati ta dakatar da daukar nauyin daliban kasashen waje, shi da kansa ya ci gaba da wannan shiri ta hanyar Gidauniyar Ci Gaban Kwankwasiyya (KDF).

 

Kwankwaso ya kara da cewa, bayan malaman da gidauniyar ta dauki nauyinsu, shirin ya ci gaba da tallafa wa dalibai sama da 3,000 cikin shekaru hudu don yin karatu a kasashe 14 a Turai, Asiya, Afirka da Gabas ta Tsakiya.

 

Shirin ya samar da likitoci, injiniyoyi, matukan jirgi da kwararru a duniya. Bayanan da ake da su daga KDF, sun nuna cewa shirin ya zuwa yanzu ya samar da daruruwan likitoci da kwararru da ke aiki a asibitocin koyarwa a Nijeriya da kasashen waje; kwararrun matukan jirgi da ma’aikata a filin jiragen sama; dubban injiniyoyi, kwararru a fannin fasahar sadarwa; da kuma malamai da masu bincike, tare da sama da masu digirin digirgir 300 da aka bayyana a taron.

 

Ta kuma samar da masana magunguna, masu gine-gine, masana tattalin arziki, lauyoyi, kwararru kan manufofin jama’a da masu aikin ci gaba da ke aiki a fadin Nijeriya, Afirka, Turai, Arewacin Amurka da Gabas ta Tsakiya.

 

Kwankwaso ya bayyana cewa manufar gidauniyar ba wai kawai daukar nauyin malamai ba ne, har ma da jagorantar su, bin diddigin su da kuma hada su cikin ayyukan gwamnati, shugabanci da ci gaban kasa.

Sulaiman
+ postsBio
  • Sulaiman
    Kwamitin Ba Da Shawara Kan Hadin Gwiwar Kasa Da Kasa Na Dandalin BRI Ya Yi Taronsa Na 2026
  • Sulaiman
    Wang Huning Ya Ziyarci Koriya Ta Arewa
  • Sulaiman
    Yawan Mu’amalar Kudi Tsakanin Mazauna Sin Da ’Yan Kasashen Waje Ya Hau Wani Sabon Matsayi A Tarihi
  • Sulaiman
    Xi Jinping Ya Halarci Bikin Bude Babban Taron AI Na Duniya Na 2026 Tare Da Gabatar Da Jawabi

MASU ALAKA

Gasar Kofin Duniya: Da Ƙarfinmu Muka Kawo Matakin Da Muke Yanzu – Messi
Manyan Labarai

Gasar Kofin Duniya: Da Ƙarfinmu Muka Kawo Matakin Da Muke Yanzu – Messi

July 17, 2026
Bayan Ceto Daliban Oyo: Kallo Ya Koma Borno Da Yobe
Manyan Labarai

Bayan Ceto Daliban Oyo: Kallo Ya Koma Borno Da Yobe

July 17, 2026
Batun Yawan Bashin Da Nijeriya Ke Ciyowa Daga Ketare
Manyan Labarai

Batun Yawan Bashin Da Nijeriya Ke Ciyowa Daga Ketare

July 17, 2026
Next Post
Majalisa Ta Nemi Tinubu Ya Canza Dabarun Yaƙi Da Ta’addanci Don Kawo Ƙarshen Kashe-kashe

'Yan Majalisar Wakilai Sun Nemi A Dakatar Da Aiwatar Da Dokokin Haraji

LABARAI MASU NASABA

Sake Daukar Shettima Da Tinubu Ya Yi Zai Kara Karfafa APC A Zaben 2027 –Farfesa Yerima

Sake Daukar Shettima Da Tinubu Ya Yi Zai Kara Karfafa APC A Zaben 2027 –Farfesa Yerima

July 17, 2026
Kwamitin Ba Da Shawara Kan Hadin Gwiwar Kasa Da Kasa Na Dandalin BRI Ya Yi Taronsa Na 2026

Kwamitin Ba Da Shawara Kan Hadin Gwiwar Kasa Da Kasa Na Dandalin BRI Ya Yi Taronsa Na 2026

July 17, 2026
Wang Huning Ya Ziyarci Koriya Ta Arewa

Wang Huning Ya Ziyarci Koriya Ta Arewa

July 17, 2026
Yawan Mu’amalar Kudi Tsakanin Mazauna Sin Da ’Yan Kasashen Waje Ya Hau Wani Sabon Matsayi A Tarihi

Yawan Mu’amalar Kudi Tsakanin Mazauna Sin Da ’Yan Kasashen Waje Ya Hau Wani Sabon Matsayi A Tarihi

July 17, 2026
Gasar Kofin Duniya: Da Ƙarfinmu Muka Kawo Matakin Da Muke Yanzu – Messi

Gasar Kofin Duniya: Da Ƙarfinmu Muka Kawo Matakin Da Muke Yanzu – Messi

July 17, 2026
Matatar Man Dangote Ta Dawo Sayar Da Fetur A Dala

Matatar Man Dangote Ta Dawo Sayar Da Fetur A Dala

July 17, 2026
Xi Jinping Ya Halarci Bikin Bude Babban Taron AI Na Duniya Na 2026 Tare Da Gabatar Da Jawabi

Xi Jinping Ya Halarci Bikin Bude Babban Taron AI Na Duniya Na 2026 Tare Da Gabatar Da Jawabi

July 17, 2026
Falalar Salatut Tasbihi

Falalar Salatut Tasbihi

July 17, 2026
A Baya Ba A San Jihar Kano Da Harkar Daba Ba – Tsohon Shugaban NAHCON

A Baya Ba A San Jihar Kano Da Harkar Daba Ba – Tsohon Shugaban NAHCON

July 17, 2026
Direba Ya Hallaka Ɗalibar Jami’ar Kiwon Lafiya Ta Azare, Ya Gudu

Direba Ya Hallaka Ɗalibar Jami’ar Kiwon Lafiya Ta Azare, Ya Gudu

July 17, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.