ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Friday, September 11, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Yadda Na Sayar Da Kadarori Na Don Ɗaukar Nauyin Ɗalibai A Ƙasashen Waje – Kwankwaso

by Sulaiman
9 months ago

Tsohon gwamnan jihar Kano kuma shugaban tafiyar Kwankwasiyya, Sanata Rabiu Musa Kwankwaso, ya tuna yadda ya sayar da kadarorinsa don ɗaukar nauyin matasa maza da mata 370 daga jihar Kano don yin karatu a kasashen waje.

 

A yayin da wadanda suka ci gajiyar shirin tallafin karatu na Kwankwasiyya suka gudanar da taron su na shekara-shekara don godiya ga wannan tallafin, Kwankwaso ya bayyana ilimi a matsayin gado mafi dorewa da kowane shugaba zai iya gadar wa al’umma.

ADVERTISEMENT
  • Mutum Biyu Sun Rasu Yayin Rikici Tsakanin Jami’an Tsaro Da Matasa A Katsina
  • Sin Za Ta Aiwatar Da Manufar Harkokin Kudi Mai Inganci A 2026

Da yake jawabi a wurin taron mai tarihi, Jagoran ya gode wa Allah Madaukakin Sarki da ya nuna masa irin wannan “rana mai tarihi ga jihar Kano da Nijeriya,” yana mai lura da cewa taron ya hada jigogi a fannin ilimin zamani da aka dauki nauyinsu tsawon kusan shekaru 25.

 

LABARAI MASU NASABA

Sojoji Sun Ceto Fasinjoji Uku Da ‘Yan Bindiga Suka Harba A Filato

Amurka Ta Bai Wa Nijeriya Sabbin Kayan Yaƙi Domin Yaƙi Da Ta’addanci

“Ina tuna yawancinku a baya. Wasu daga cikinku sun yi kama da wadanda suka fito kai tsaye daga kauyuka. A yau, ina ganin kwarin gwiwa, kwarewa har ma wasunku sun manyanta, har da furfura a kansu” in ji shi

 

A cewar wata sanarwa da Dakta Mansur Hassan ya fitar, Kwankwaso, wanda ya mulki jihar Kano tsawon shekaru takwas, ya ce taron ya jaddada muhimmancin shugabanci, dorewa da kuma saka hannun jari na dogon lokaci a fannin rayuwar dan adam.

 

Ya bayyana cewa bayan babban zaben 2019, lokacin da gwamnati ta dakatar da daukar nauyin daliban kasashen waje, shi da kansa ya ci gaba da wannan shiri ta hanyar Gidauniyar Ci Gaban Kwankwasiyya (KDF).

 

Kwankwaso ya kara da cewa, bayan malaman da gidauniyar ta dauki nauyinsu, shirin ya ci gaba da tallafa wa dalibai sama da 3,000 cikin shekaru hudu don yin karatu a kasashe 14 a Turai, Asiya, Afirka da Gabas ta Tsakiya.

 

Shirin ya samar da likitoci, injiniyoyi, matukan jirgi da kwararru a duniya. Bayanan da ake da su daga KDF, sun nuna cewa shirin ya zuwa yanzu ya samar da daruruwan likitoci da kwararru da ke aiki a asibitocin koyarwa a Nijeriya da kasashen waje; kwararrun matukan jirgi da ma’aikata a filin jiragen sama; dubban injiniyoyi, kwararru a fannin fasahar sadarwa; da kuma malamai da masu bincike, tare da sama da masu digirin digirgir 300 da aka bayyana a taron.

 

Ta kuma samar da masana magunguna, masu gine-gine, masana tattalin arziki, lauyoyi, kwararru kan manufofin jama’a da masu aikin ci gaba da ke aiki a fadin Nijeriya, Afirka, Turai, Arewacin Amurka da Gabas ta Tsakiya.

 

Kwankwaso ya bayyana cewa manufar gidauniyar ba wai kawai daukar nauyin malamai ba ne, har ma da jagorantar su, bin diddigin su da kuma hada su cikin ayyukan gwamnati, shugabanci da ci gaban kasa.

Sulaiman
+ postsBio
  • Sulaiman
    Ding Xuexiang Ya Halarci Taron Kolin CIFTIS Tare Da Ganawa Da Manyan Jami’an Kasashen Waje
  • Sulaiman
    Sin Ce Ta Zo Ta Farko A Rahoton Yanayin Tsaron Jama’a Na Duniya
  • Sulaiman
    Sin Ta Ciri Tuta Game Da Rawar Gani Da Take Takawa A Fannin Warware Kalubalen Tsaro A Gabas Ta Tsakiya
  • Sulaiman
    Gwamnatin Tarayya Ta Gwangwaje Tawagar Kwallon Kwando Ta Mata Da Dala 100,000 Kowace

MASU ALAKA

Sojoji Sun Ceto Fasinjoji Uku Da ‘Yan Bindiga Suka Harba A Filato
Manyan Labarai

Sojoji Sun Ceto Fasinjoji Uku Da ‘Yan Bindiga Suka Harba A Filato

September 10, 2026
Amurka Ta Bai Wa Nijeriya Sabbin Kayan Yaƙi Domin Yaƙi Da Ta’addanci
Manyan Labarai

Amurka Ta Bai Wa Nijeriya Sabbin Kayan Yaƙi Domin Yaƙi Da Ta’addanci

September 10, 2026
Cutar Mashaƙo Ta Ɓarke A Kano, Katsina Da Filato
Manyan Labarai

Mashaƙo: Adadin Mutanen Da Suka Rasu Sun Kai 27 A Filato

September 10, 2026
Next Post
Majalisa Ta Nemi Tinubu Ya Canza Dabarun Yaƙi Da Ta’addanci Don Kawo Ƙarshen Kashe-kashe

'Yan Majalisar Wakilai Sun Nemi A Dakatar Da Aiwatar Da Dokokin Haraji

LABARAI MASU NASABA

Ding Xuexiang Ya Halarci Taron Kolin CIFTIS Tare Da Ganawa Da Manyan Jami’an Kasashen Waje

Ding Xuexiang Ya Halarci Taron Kolin CIFTIS Tare Da Ganawa Da Manyan Jami’an Kasashen Waje

September 10, 2026
Sin Ce Ta Zo Ta Farko A Rahoton Yanayin Tsaron Jama’a Na Duniya

Sin Ce Ta Zo Ta Farko A Rahoton Yanayin Tsaron Jama’a Na Duniya

September 10, 2026
Sin Ta Ciri Tuta Game Da Rawar Gani Da Take Takawa A Fannin Warware Kalubalen Tsaro A Gabas Ta Tsakiya

Sin Ta Ciri Tuta Game Da Rawar Gani Da Take Takawa A Fannin Warware Kalubalen Tsaro A Gabas Ta Tsakiya

September 10, 2026
Gwamnatin Tarayya Ta Gwangwaje Tawagar Kwallon Kwando Ta Mata Da Dala 100,000 Kowace

Gwamnatin Tarayya Ta Gwangwaje Tawagar Kwallon Kwando Ta Mata Da Dala 100,000 Kowace

September 10, 2026
Sin Da Amurka Na Gudanar Da Tattaunawa Dangane Da Yiwuwar Rage Harajin Ramuwar Gayya Wanda Darajarsa Ka Iya Kaiwa Dala Biliyan 30

Sin Da Amurka Na Gudanar Da Tattaunawa Dangane Da Yiwuwar Rage Harajin Ramuwar Gayya Wanda Darajarsa Ka Iya Kaiwa Dala Biliyan 30

September 10, 2026
Gwamnatin Tarayya Ta Dakatar da Shirin Ƙara Kuɗin Jarabawar WAEC da NECO

Gwamnatin Tarayya Za Ta Rika Bai Wa Ɗalibai 100MB Na Data Kyauta Kullum

September 10, 2026
Sin Da Amurka Na Wanzar Da Mu’amala Game Da Shirin Ganawar Da Manyan Shugabannin Kasashen Biyu Za Su Yi A Bana

Sin Da Amurka Na Wanzar Da Mu’amala Game Da Shirin Ganawar Da Manyan Shugabannin Kasashen Biyu Za Su Yi A Bana

September 10, 2026
Sojoji Sun Ceto Fasinjoji Uku Da ‘Yan Bindiga Suka Harba A Filato

Sojoji Sun Ceto Fasinjoji Uku Da ‘Yan Bindiga Suka Harba A Filato

September 10, 2026
Xi Zai Halarci Taron BRICS Karo Na 18 A Indiya

Xi Zai Halarci Taron BRICS Karo Na 18 A Indiya

September 10, 2026
Rodri Ya Nemi Afuwar Valencia Dangane Da Kalaman Da Yayi Akanta

Rodri Ya Nemi Afuwar Valencia Dangane Da Kalaman Da Yayi Akanta

September 10, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.