ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Thursday, June 25, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Yadda Sin Da Kasashen Afirka Ke Rungumar Juna Na Samar Da Damammaki Ga Afirka Ta Fannin Bunkasa Harkokin Yawon Shakatawa 

by Sulaiman and CGTN Hausa
4 months ago
Sin

Lokacin da ministar harkokin yawon shakatawa ta kasar Afirka ta Kudu Madam Patricia de Lille ta kwatanta da kasuwar kasar Sin a matsayin “babban injin” da zai ingiza bunkasuwar harkokin yawon shakatawa a kasarta, lallai gaskiyar al’amarin ta bayyana ke nan, wato kasashen Afirka na kokarin janyo baki masu yawon shakatawa daga kasar Sin. Daga ranar 23 zuwa 25 ga wata, hukumar kula da harkokin yawon shakatawa ta kasar Afirka ta Kudu ta kira taron da ake ma lakabin “Meetings Africa 2026”a birnin Johannesburg, taron da ya samu halartar wakilan kasashen Afirka sama da 20, wadanda suka tattauna batun ta yaya za su janyo baki masu yawon shakatawa daga kasar Sin.

A bana ake cika shekaru 70 da fara kulla huldar diflomasiyya a tsakanin Sin da kasashen Afirka, haka kuma shekara ce da sassan biyu suka tabbatar a matsayin shekarar cudanyar al’umma da musayar al’adu a tsakaninsu. Don haka, taron da aka kira ba kawai yana shafar harkokin yawon shakatawa ba ne, har ma mataki ne na kara karfafa dangantakar da ke tsakanin Sin da kasashen Afirka. Don kara jawo baki masu yawon shakatawa daga kasar Sin, kasar Afirka ta Kudu ta kaddamar da tsarin ETA ga bakin, wanda zai yi matukar rage lokacin da ake dauka wajen samun biza, sa’an nan, sassan kula da harkokin yawon shakatawa na kasar sun fara samar da kwasa-kwasai na koyar da Sinanci ga ma’aikatansu, don daidaita matsaloli da ka iya bulla ta fannin mu’amala da bakin. Kasar Gabon a nata bangaren, ta dauki matakan saukaka harkokin samun biza ga al’ummar Sinawa, baya ga dukufa a kan inganta zirga-zirga da otel-otel ga baki daga kasar Sin. Har wa yau, in mun lura, sama da kasashen Afirka 20 ne suka dauki matakai na soke bukatar neman biza ga al’ummar kasar Sin ko kuma ba su biza a lokacin da suka shiga kasar.

A sa’i daya kuma, karin baki masu yawon shakatawa na kasar Sin na mai da nahiyar Afirka a matsayin wurin da suke mafarkin zuwa don yawon shakatawa. Li Qiaoyang wanda ya fito daga lardin Shandong da ke gabashin kasar Sin, ya taba zuwa kasashen Afirka don yawon bude ido har sau biyu, kasashen da suka yi matukar burge shi. Ya ce, “Irin yanayin halittu da al’adu na musamman na Afirka abin burgewa ne matuka, kuma matasan kasar Sin da yawa na sha’awar zuwa.” A wannan shekara kuma, yana shirin zuwa kasar Tanzania. Baki masu yawon shakatawa irinsu Li Qiaoyang suna da yawa, kuma alkaluman kamfanonin samar da hidimomin yawon shakatawa na kasar Sin sun tabbatar da hakan. Kamfanin GZL da ke birnin Guangzhou na kudancin kasar Sin ya bayyana cewa, a cikin ’yan watannin baya, yawan shawartar harkokin yawon shakatawa zuwa kasashen Afirka ya karu da kimanin kaso 50% zuwa 60%.

ADVERTISEMENT

A yayin da kasashen Afirka ke daukar jerin matakai na jawo baki daga kasar Sin don neman cin gajiyar babbar kasuwar kasar Sin, ga baki masu yawon shakatawa na kasar Sin kuma, sai a ce “Nesa ta zo kusa”. Irin yadda Sin da kasashen Afirka ke rungumar juna ya shaida yadda suke gina al’umma mai kyakkyawar makoma ta bai-daya a tsakaninsu, kuma irin yadda suke musayar al’adu da juna zai karfafa fahimtar juna da dankon zumunci a tsakanin al’ummunsu. Daidai kamar yadda Rod Rembendambya, babban kwamishinan kasar Gabon a Afirka ta Kudu ya ce, zuwan baki daga kasar Sin ba ma kawai zai samar da damar inganta otel-otel da ma sauran manyan ababen more rayuwa a wurin ba, hatta ma da mu’amala da musayar al’adu a tsakanin al’ummomin kasashen biyu.

A lokacin da Sin da Afirka ke murnar cika shekaru 70 da fara kulla huldar diplomasiyya a tsakaninsu, da ma shagulgulan murnar shekarar cudanyar al’umma da musayar al’adu a tsakaninsu, karin baki masu yawon shakatawa na kasar Sin na zuwa kasashen Afirka, wadanda a yayin da suke yawon bude ido, za su kara samun fahimtar kasashen Afirka. Bisa ga irin mu’amala da juna, huldar zumunta za ta kara shiga zukatan al’ummominsu.

LABARAI MASU NASABA

Dandalin DAVOS Na Bana: Fage Ne Da “Kirkire-Kirkiren Sin” Ya Sadu Da “Kyakkyawan Fatan Afirka”

Sin Na Daukar hakikanan Matakan Gina Kyakkaywar Makomar Al’ummun Sin Da Afirka Ta Bai Daya

 

 

 

Sin
Sulaiman
+ posts Bio
  • Sulaiman
    Ƙungiyar NPCF Ta Yi Barazanar Janye Goyon Bayanta Ga Tinubu
  • Sulaiman
    Firaministan Sin Ya Halarci Taron Tattaunawa Da Wakilan ‘Yan Kasuwa Mahalarta Dandalin Tattalin Arzikin Duniya Na DAVOS
  • Sulaiman
    An Fara Gasar Tseren Dawakai Ta ‘Renewed Hope’ da Sabon Salo A Kano
  • Sulaiman
    Dokar Sin Ta Gurfanar Da Masu Rajin Ballewar Kabilun Kasar Da Ke Kasashen Waje Ta Dace
Sin
CGTN Hausa
+ posts Bio
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    Firaministan Sin Ya Halarci Taron Tattaunawa Da Wakilan ‘Yan Kasuwa Mahalarta Dandalin Tattalin Arzikin Duniya Na DAVOS
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    Dokar Sin Ta Gurfanar Da Masu Rajin Ballewar Kabilun Kasar Da Ke Kasashen Waje Ta Dace
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    ’Yan Kasuwa Na Kasashen Waje Sun Yaba Wa Yanayin Kasuwanci Na Sin
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    Dandalin DAVOS Na Bana: Fage Ne Da “Kirkire-Kirkiren Sin” Ya Sadu Da “Kyakkyawan Fatan Afirka”

MASU ALAKA

Dandalin DAVOS Na Bana: Fage Ne Da “Kirkire-Kirkiren Sin” Ya Sadu Da “Kyakkyawan Fatan Afirka”
Ra'ayi Riga

Dandalin DAVOS Na Bana: Fage Ne Da “Kirkire-Kirkiren Sin” Ya Sadu Da “Kyakkyawan Fatan Afirka”

June 24, 2026
Sin Na Daukar hakikanan Matakan Gina Kyakkaywar Makomar Al’ummun Sin Da Afirka Ta Bai Daya
Ra'ayi Riga

Sin Na Daukar hakikanan Matakan Gina Kyakkaywar Makomar Al’ummun Sin Da Afirka Ta Bai Daya

June 19, 2026
A Yi Watsi Da Wannan “Mummunan Teburi”
Ra'ayi Riga

A Yi Watsi Da Wannan “Mummunan Teburi”

June 18, 2026
Next Post
Ramadan: Lokutan Buda-Baki Da Sahur Na Azumi Na 2

Ramadan: Lokutan Buda-Baki Da Sahur Na Azumi Na 9

LABARAI MASU NASABA

Ƙungiyar NPCF Ta Yi Barazanar Janye Goyon Bayanta Ga Tinubu

Ƙungiyar NPCF Ta Yi Barazanar Janye Goyon Bayanta Ga Tinubu

June 25, 2026
Firaministan Sin Ya Halarci Taron Tattaunawa Da Wakilan ‘Yan Kasuwa Mahalarta Dandalin Tattalin Arzikin Duniya Na DAVOS

Firaministan Sin Ya Halarci Taron Tattaunawa Da Wakilan ‘Yan Kasuwa Mahalarta Dandalin Tattalin Arzikin Duniya Na DAVOS

June 25, 2026
Sojoji Sun Kama Mai Kai Wa Ƴan Ta’adda Kayan Aiki A Zamfara

Sojoji Sun Kama Mai Kai Wa Ƴan Ta’adda Kayan Aiki A Zamfara

June 25, 2026
Kotu Ta Ɗege Shari’ar Ganduje Da Wasu Mutum 7 Zuwa 14 Ga Oktoba 2026

Kotu Ta Ɗege Shari’ar Ganduje Da Wasu Mutum 7 Zuwa 14 Ga Oktoba 2026

June 25, 2026
An Fara Gasar Tseren Dawakai Ta ‘Renewed Hope’ da Sabon Salo A Kano

An Fara Gasar Tseren Dawakai Ta ‘Renewed Hope’ da Sabon Salo A Kano

June 25, 2026
APC Ta Dage Yakin Zaben Shugaban Kasarta A Kano

An Dakatar Da Shugaban APC Na Kebbi Da Kwamishina Kan Zaɓen Cike Gurbin Zuru

June 25, 2026
Ndume Ya Bayyana Dalilin Da Ya Sa Yake Goyon Bayan Ƙudirin Kafa ‘Yansandan Jihohi

Ndume Ya Bayyana Dalilin Da Ya Sa Yake Goyon Bayan Ƙudirin Kafa ‘Yansandan Jihohi

June 25, 2026
EFCC Za Ta Gurfanar Da Shugaban Miyetti Allah Kan Zargin Almundahanar Dala Miliyan 2.53

EFCC Za Ta Gurfanar Da Shugaban Miyetti Allah Kan Zargin Almundahanar Dala Miliyan 2.53

June 25, 2026
Maroko Ta Zama Ƙasa Ta Farko Daga Afirka Da Ta Tsallaka Zuwa Zagaye Na 32 A Gasar Kofin Duniya

Maroko Ta Zama Ƙasa Ta Farko Daga Afirka Da Ta Tsallaka Zuwa Zagaye Na 32 A Gasar Kofin Duniya

June 25, 2026
Zan Ware 10bn Don Inganta Ilimin Matasa Idan Na Ci Zabe – Atiku

‘Yan Nijeriya Ba Sa Bukatar ‘Yan Jarida Su Faɗa Musu Suna Jin Yunwa — Atiku

June 25, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.