ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Friday, June 5, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Yadda Sin Da Kasashen Afirka Ke Rungumar Juna Na Samar Da Damammaki Ga Afirka Ta Fannin Bunkasa Harkokin Yawon Shakatawa 

by Sulaiman and CGTN Hausa
3 months ago
Sin

Lokacin da ministar harkokin yawon shakatawa ta kasar Afirka ta Kudu Madam Patricia de Lille ta kwatanta da kasuwar kasar Sin a matsayin “babban injin” da zai ingiza bunkasuwar harkokin yawon shakatawa a kasarta, lallai gaskiyar al’amarin ta bayyana ke nan, wato kasashen Afirka na kokarin janyo baki masu yawon shakatawa daga kasar Sin. Daga ranar 23 zuwa 25 ga wata, hukumar kula da harkokin yawon shakatawa ta kasar Afirka ta Kudu ta kira taron da ake ma lakabin “Meetings Africa 2026”a birnin Johannesburg, taron da ya samu halartar wakilan kasashen Afirka sama da 20, wadanda suka tattauna batun ta yaya za su janyo baki masu yawon shakatawa daga kasar Sin.

A bana ake cika shekaru 70 da fara kulla huldar diflomasiyya a tsakanin Sin da kasashen Afirka, haka kuma shekara ce da sassan biyu suka tabbatar a matsayin shekarar cudanyar al’umma da musayar al’adu a tsakaninsu. Don haka, taron da aka kira ba kawai yana shafar harkokin yawon shakatawa ba ne, har ma mataki ne na kara karfafa dangantakar da ke tsakanin Sin da kasashen Afirka. Don kara jawo baki masu yawon shakatawa daga kasar Sin, kasar Afirka ta Kudu ta kaddamar da tsarin ETA ga bakin, wanda zai yi matukar rage lokacin da ake dauka wajen samun biza, sa’an nan, sassan kula da harkokin yawon shakatawa na kasar sun fara samar da kwasa-kwasai na koyar da Sinanci ga ma’aikatansu, don daidaita matsaloli da ka iya bulla ta fannin mu’amala da bakin. Kasar Gabon a nata bangaren, ta dauki matakan saukaka harkokin samun biza ga al’ummar Sinawa, baya ga dukufa a kan inganta zirga-zirga da otel-otel ga baki daga kasar Sin. Har wa yau, in mun lura, sama da kasashen Afirka 20 ne suka dauki matakai na soke bukatar neman biza ga al’ummar kasar Sin ko kuma ba su biza a lokacin da suka shiga kasar.

A sa’i daya kuma, karin baki masu yawon shakatawa na kasar Sin na mai da nahiyar Afirka a matsayin wurin da suke mafarkin zuwa don yawon shakatawa. Li Qiaoyang wanda ya fito daga lardin Shandong da ke gabashin kasar Sin, ya taba zuwa kasashen Afirka don yawon bude ido har sau biyu, kasashen da suka yi matukar burge shi. Ya ce, “Irin yanayin halittu da al’adu na musamman na Afirka abin burgewa ne matuka, kuma matasan kasar Sin da yawa na sha’awar zuwa.” A wannan shekara kuma, yana shirin zuwa kasar Tanzania. Baki masu yawon shakatawa irinsu Li Qiaoyang suna da yawa, kuma alkaluman kamfanonin samar da hidimomin yawon shakatawa na kasar Sin sun tabbatar da hakan. Kamfanin GZL da ke birnin Guangzhou na kudancin kasar Sin ya bayyana cewa, a cikin ’yan watannin baya, yawan shawartar harkokin yawon shakatawa zuwa kasashen Afirka ya karu da kimanin kaso 50% zuwa 60%.

ADVERTISEMENT

A yayin da kasashen Afirka ke daukar jerin matakai na jawo baki daga kasar Sin don neman cin gajiyar babbar kasuwar kasar Sin, ga baki masu yawon shakatawa na kasar Sin kuma, sai a ce “Nesa ta zo kusa”. Irin yadda Sin da kasashen Afirka ke rungumar juna ya shaida yadda suke gina al’umma mai kyakkyawar makoma ta bai-daya a tsakaninsu, kuma irin yadda suke musayar al’adu da juna zai karfafa fahimtar juna da dankon zumunci a tsakanin al’ummunsu. Daidai kamar yadda Rod Rembendambya, babban kwamishinan kasar Gabon a Afirka ta Kudu ya ce, zuwan baki daga kasar Sin ba ma kawai zai samar da damar inganta otel-otel da ma sauran manyan ababen more rayuwa a wurin ba, hatta ma da mu’amala da musayar al’adu a tsakanin al’ummomin kasashen biyu.

A lokacin da Sin da Afirka ke murnar cika shekaru 70 da fara kulla huldar diplomasiyya a tsakaninsu, da ma shagulgulan murnar shekarar cudanyar al’umma da musayar al’adu a tsakaninsu, karin baki masu yawon shakatawa na kasar Sin na zuwa kasashen Afirka, wadanda a yayin da suke yawon bude ido, za su kara samun fahimtar kasashen Afirka. Bisa ga irin mu’amala da juna, huldar zumunta za ta kara shiga zukatan al’ummominsu.

LABARAI MASU NASABA

Abokin Jibi Shi Ne Aboki

Rayukan Mutanen Kenya Na Da Muhimmanci Daidai Da Na ‘Yan Amurka

 

 

 

Sin
Sulaiman
+ posts Bio
  • Sulaiman
    Takunkumin Amurka Ya Haifar Da Mummunan Tasiri Ga Tsarin Samar Da Kayan Latironi Na Duniya
  • Sulaiman
    Gwamna Sani Ya Kashe Sama Da Naira Biliyan Ɗaya Kan Tallafin Ɗalibai A Kaduna – Kwamishina
  • Sulaiman
    Sin Ta Ware Kudi Har Yuan Biliyan 99.9 Domin Tallafawa Kula Da Lafiyar Yara A 2026
  • Sulaiman
    Tasirin Nasarar Da Kasar Sin Ta Cimma A Fannin Kakkabe Matsanancin Talauci
Sin
CGTN Hausa
+ posts Bio
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    Sin Ta Ware Kudi Har Yuan Biliyan 99.9 Domin Tallafawa Kula Da Lafiyar Yara A 2026
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    Tasirin Nasarar Da Kasar Sin Ta Cimma A Fannin Kakkabe Matsanancin Talauci
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    Sabbin Ra’ayoyin Ci Gaba: Manufofin Zamani Na Zamanantarwa
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    Ana Gudanar Da Taron Masana Ilmin Harkokin Kasar Sin Karo Na Uku

MASU ALAKA

Abokin Jibi Shi Ne Aboki
Ra'ayi Riga

Abokin Jibi Shi Ne Aboki

June 3, 2026
Rayukan Mutanen Kenya Na Da Muhimmanci Daidai Da Na ‘Yan Amurka
Ra'ayi Riga

Rayukan Mutanen Kenya Na Da Muhimmanci Daidai Da Na ‘Yan Amurka

June 1, 2026
Nagartattun Manufofin Sin Suna Janyo Hankalin Kasashen Duniya
Ra'ayi Riga

Nagartattun Manufofin Sin Suna Janyo Hankalin Kasashen Duniya

May 29, 2026
Next Post
Ramadan: Lokutan Buda-Baki Da Sahur Na Azumi Na 2

Ramadan: Lokutan Buda-Baki Da Sahur Na Azumi Na 9

Discussion about this post

LABARAI MASU NASABA

An Yi Suka Kan Mayar Da Nijeriya Jujin Jibge Kwantaina Da Ake Shigowa Da Su

An Yi Suka Kan Mayar Da Nijeriya Jujin Jibge Kwantaina Da Ake Shigowa Da Su

June 5, 2026
Dorewar Tattalin Arzikin Duniya Ya Dogara Ne Kan Ayyukan Tashoshin Jiragen Ruwa Na Afrika Ta Tsakiya, Cewar Dantsoho

Dorewar Tattalin Arzikin Duniya Ya Dogara Ne Kan Ayyukan Tashoshin Jiragen Ruwa Na Afrika Ta Tsakiya, Cewar Dantsoho

June 5, 2026
Sabon Rikicin Manoma Da Makiyaya yayi Ajalin Mutuwar Mutane 7 A Bauchi

Sabon Rikicin Manoma Da Makiyaya yayi Ajalin Mutuwar Mutane 7 A Bauchi

June 5, 2026
Babu Wani Shiri Na Kwaso ‘Yan Nijeriya Daga Falasdin Ko Isra’ila –Gwamnatin Tarayya

Mulkin Tinubu A Shekara 3:Ina Aka Fito? Ina Aka Dosa?

June 5, 2026
Hajji 2026: Mahajjata 1,905 Sun Dawo Nijeriya Daga Saudiyya

Hajji 2026: Mahajjata 1,905 Sun Dawo Nijeriya Daga Saudiyya

June 5, 2026
Har Yanzu Akwai Sauran Rina A Kaba Game Da Makomar Yara A Nijeriya

Har Yanzu Akwai Sauran Rina A Kaba Game Da Makomar Yara A Nijeriya

June 5, 2026
Matatar Dangote Ta Ƙara Yawan Man Da Take Tacewa Zuwa Ganga 700,000

Matatar Dangote Ta Ƙara Yawan Man Da Take Tacewa Zuwa Ganga 700,000

June 4, 2026
Ƴansanda Sun Daƙile Harin Ƴan Bindiga, Sun Kwato Shanu 25 A Sakkwato

Ƴansanda Sun Daƙile Harin Ƴan Bindiga, Sun Kwato Shanu 25 A Sakkwato

June 4, 2026
Takunkumin Amurka Ya Haifar Da Mummunan Tasiri Ga Tsarin Samar Da Kayan Latironi Na Duniya

Takunkumin Amurka Ya Haifar Da Mummunan Tasiri Ga Tsarin Samar Da Kayan Latironi Na Duniya

June 4, 2026
Rikicin Manoma Da Makiyaya Ya Kashe Mutane 7, Ya Jikkata 6 A Bauchi

Rikicin Manoma Da Makiyaya Ya Kashe Mutane 7, Ya Jikkata 6 A Bauchi

June 4, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.