Lokacin da ministar harkokin yawon shakatawa ta kasar Afirka ta Kudu Madam Patricia de Lille ta kwatanta da kasuwar kasar Sin a matsayin “babban injin” da zai ingiza bunkasuwar harkokin yawon shakatawa a kasarta, lallai gaskiyar al’amarin ta bayyana ke nan, wato kasashen Afirka na kokarin janyo baki masu yawon shakatawa daga kasar Sin. Daga ranar 23 zuwa 25 ga wata, hukumar kula da harkokin yawon shakatawa ta kasar Afirka ta Kudu ta kira taron da ake ma lakabin “Meetings Africa 2026”a birnin Johannesburg, taron da ya samu halartar wakilan kasashen Afirka sama da 20, wadanda suka tattauna batun ta yaya za su janyo baki masu yawon shakatawa daga kasar Sin.
A bana ake cika shekaru 70 da fara kulla huldar diflomasiyya a tsakanin Sin da kasashen Afirka, haka kuma shekara ce da sassan biyu suka tabbatar a matsayin shekarar cudanyar al’umma da musayar al’adu a tsakaninsu. Don haka, taron da aka kira ba kawai yana shafar harkokin yawon shakatawa ba ne, har ma mataki ne na kara karfafa dangantakar da ke tsakanin Sin da kasashen Afirka. Don kara jawo baki masu yawon shakatawa daga kasar Sin, kasar Afirka ta Kudu ta kaddamar da tsarin ETA ga bakin, wanda zai yi matukar rage lokacin da ake dauka wajen samun biza, sa’an nan, sassan kula da harkokin yawon shakatawa na kasar sun fara samar da kwasa-kwasai na koyar da Sinanci ga ma’aikatansu, don daidaita matsaloli da ka iya bulla ta fannin mu’amala da bakin. Kasar Gabon a nata bangaren, ta dauki matakan saukaka harkokin samun biza ga al’ummar Sinawa, baya ga dukufa a kan inganta zirga-zirga da otel-otel ga baki daga kasar Sin. Har wa yau, in mun lura, sama da kasashen Afirka 20 ne suka dauki matakai na soke bukatar neman biza ga al’ummar kasar Sin ko kuma ba su biza a lokacin da suka shiga kasar.
A sa’i daya kuma, karin baki masu yawon shakatawa na kasar Sin na mai da nahiyar Afirka a matsayin wurin da suke mafarkin zuwa don yawon shakatawa. Li Qiaoyang wanda ya fito daga lardin Shandong da ke gabashin kasar Sin, ya taba zuwa kasashen Afirka don yawon bude ido har sau biyu, kasashen da suka yi matukar burge shi. Ya ce, “Irin yanayin halittu da al’adu na musamman na Afirka abin burgewa ne matuka, kuma matasan kasar Sin da yawa na sha’awar zuwa.” A wannan shekara kuma, yana shirin zuwa kasar Tanzania. Baki masu yawon shakatawa irinsu Li Qiaoyang suna da yawa, kuma alkaluman kamfanonin samar da hidimomin yawon shakatawa na kasar Sin sun tabbatar da hakan. Kamfanin GZL da ke birnin Guangzhou na kudancin kasar Sin ya bayyana cewa, a cikin ’yan watannin baya, yawan shawartar harkokin yawon shakatawa zuwa kasashen Afirka ya karu da kimanin kaso 50% zuwa 60%.
A yayin da kasashen Afirka ke daukar jerin matakai na jawo baki daga kasar Sin don neman cin gajiyar babbar kasuwar kasar Sin, ga baki masu yawon shakatawa na kasar Sin kuma, sai a ce “Nesa ta zo kusa”. Irin yadda Sin da kasashen Afirka ke rungumar juna ya shaida yadda suke gina al’umma mai kyakkyawar makoma ta bai-daya a tsakaninsu, kuma irin yadda suke musayar al’adu da juna zai karfafa fahimtar juna da dankon zumunci a tsakanin al’ummunsu. Daidai kamar yadda Rod Rembendambya, babban kwamishinan kasar Gabon a Afirka ta Kudu ya ce, zuwan baki daga kasar Sin ba ma kawai zai samar da damar inganta otel-otel da ma sauran manyan ababen more rayuwa a wurin ba, hatta ma da mu’amala da musayar al’adu a tsakanin al’ummomin kasashen biyu.
A lokacin da Sin da Afirka ke murnar cika shekaru 70 da fara kulla huldar diplomasiyya a tsakaninsu, da ma shagulgulan murnar shekarar cudanyar al’umma da musayar al’adu a tsakaninsu, karin baki masu yawon shakatawa na kasar Sin na zuwa kasashen Afirka, wadanda a yayin da suke yawon bude ido, za su kara samun fahimtar kasashen Afirka. Bisa ga irin mu’amala da juna, huldar zumunta za ta kara shiga zukatan al’ummominsu.















Discussion about this post