Wasu ‘yan bindiga sun kai farmaki kauyen Kahir da ke Karamar Hukumar Kagarko a Jihar Kaduna, inda suka kashe mutum 13 tare da yin garkuwa da wasu mutane da ba a tantance yawan adadinsu ba.
Wani mazaunin Kagarko, Shehu Bala, wanda ya tabbatar wa wakilinmu ta wayar tarho a ranar Litinin da ta gabata, ya ce; lamarin ya faru ne da misalin karfe 11:47 na daren Lahadi.
- Kwankwaso Ya Bayyana Dalilinsa Na Komawa Jam’iyyar ADC
- Fadar Shugaban Ƙasa Ta Soki Jami’iyyar ADC, Ta Ce Su Fuskanci Matsalolinsu
Ya bayyana cewa, ayarin ‘yan bindigar dauke da bindigogi kirar AK 47, sun kutsa kai wajen daurin auren, inda suka bude wuta a zauren.
Har ila yau, a cewar tasa, an garzaya da mutane da dama da suka samu raunukan harbin bindiga zuwa babban asibitin Kagarko, inda ya ce; an kai wasu mutum biyu da suka samu munanan raunuka zuwa Kaduna.
“Hakika, akwai abokaina guda biyu da ke cikin zauren da suka samu raunuka a yayin harin,” in ji shi.
“Amma ba za a iya tantance adadin wadanda aka yi garkuwa da su ba, saboda harbe-harben da aka yi.”
Wani shugaban al’umma da ya nemi a sakaya sunansa, shi ma ya tabbatar wa wakilinmu faruwar lamarin ta wayar tarho a ranar Litinin.
Kazalika, ya bayyana sunayen wasu daga cikin wadanda aka kashen da suka hada da Bako Danjuma, Williams Luka, Peter Williams, Joseph Yakubu, Bictor Peter, John Dan Asabe, Angulu Markus, Maikano Aribi, Douglas John, Ado Yakubu, Zaphaniah Alhaji, Joseph Kaddah da Francis Unguwa Doya.
Ya kara da cewa, ‘yan bindigar da suka shafe kusan sa’a guda suna gudanar da wannan ta’addanci ba tare da kawo wani daukin gaggawa ba, sun kuma mamaye wasu shaguna tare da kwashe kayan abinci da magunguna daga hannun wani masanin kimiya a cikin al’umma.
Shugaban al’ummar, ya ci gaba da cewa; tuni an binne wadanda aka kashe, koda-yake ya ce; har yanzu ba a tuntubi wadanda suka sace mutanen ba.
“Hakika, an jefa al’ummar yankin baki-daya cikin bala’i, saboda harbe-harben da ‘yan bindigar suka yi a ranar Lahadi da daddare, har wasu suka tsere cikin daji,” in ji shugaban yankin.
Haka zalika, wata majiyar ‘yansanda a sashen Kagarko ta tabbatar da yin garkuwar da kuma faruwar al’amarin, duk da cewa; ‘yansandan ba su san ainihin adadin wadanda aka sace a harin ba.
Da aka tuntubi Kakakin Rundunar ’Yansandan Jihar Kaduna, DSP Hassan Mansur, shi ma ya tabbatar da sace-sacen da kashe-kashen da aka yi, inda ya ce; rundunar za ta fitar da cikakken rahoto kan lamarin.
“Har yanzu, rundunar ba ta samu cikakken bayani kan lamarin da ya faru a unguwar ta Kahir ba, amma za a fitar da cikakken rahoto kan lamarin bayan samun cikakken bayani,” in ji shi.
Jaridar Daily Trust ta ruwaito cewa, wasu ‘yan bindiga sun yi wa al’umma kawanya, a cikinsu har da Janjala.
Mutum 14 da suka hada da dan banga da matarsa da aka yi garkuwa da su a yankin makwanni uku da suka gabata, suna hannun ‘yan bindigar.















Discussion about this post