ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Thursday, June 4, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Yadda ‘Yan Ta’adda Suka Tarwatsa Bikin Aure A Kaduna

by Sani Anwar and Sulaiman
2 months ago
'Yan Bindiga

Wasu ‘yan bindiga sun kai farmaki kauyen Kahir da ke Karamar Hukumar Kagarko a Jihar Kaduna, inda suka kashe mutum 13 tare da yin garkuwa da wasu mutane da ba a tantance yawan adadinsu ba.

Wani mazaunin Kagarko, Shehu Bala, wanda ya tabbatar wa wakilinmu ta wayar tarho a ranar Litinin da ta gabata, ya ce; lamarin ya faru ne da misalin karfe 11:47 na daren Lahadi.

  • Kwankwaso Ya Bayyana Dalilinsa Na Komawa Jam’iyyar ADC
  • Fadar Shugaban Ƙasa Ta Soki Jami’iyyar ADC, Ta Ce Su Fuskanci Matsalolinsu

Ya bayyana cewa, ayarin ‘yan bindigar dauke da bindigogi kirar AK 47, sun kutsa kai wajen daurin auren, inda suka bude wuta a zauren.

ADVERTISEMENT

Har ila yau, a cewar tasa, an garzaya da mutane da dama da suka samu raunukan harbin bindiga zuwa babban asibitin Kagarko, inda ya ce; an kai wasu mutum biyu da suka samu munanan raunuka zuwa Kaduna.

“Hakika, akwai abokaina guda biyu da ke cikin zauren da suka samu raunuka a yayin harin,” in ji shi.

LABARAI MASU NASABA

Fargabar Satar Mutane Ya Sa An Rufe Makarantu A Abuja Da Mararaba

Arsenal Na Dab Da Ɗaukar Jeremy Monga Daga Leicester City

“Amma ba za a iya tantance adadin wadanda aka yi garkuwa da su ba, saboda harbe-harben da aka yi.”

Wani shugaban al’umma da ya nemi a sakaya sunansa, shi ma ya tabbatar wa wakilinmu faruwar lamarin ta wayar tarho a ranar Litinin.

Kazalika, ya bayyana sunayen wasu daga cikin wadanda aka kashen da suka hada da Bako Danjuma, Williams Luka, Peter Williams, Joseph Yakubu, Bictor Peter, John Dan Asabe, Angulu Markus, Maikano Aribi, Douglas John, Ado Yakubu, Zaphaniah Alhaji, Joseph Kaddah da Francis Unguwa Doya.

Ya kara da cewa, ‘yan bindigar da suka shafe kusan sa’a guda suna gudanar da wannan ta’addanci ba tare da kawo wani daukin gaggawa ba, sun kuma mamaye wasu shaguna tare da kwashe kayan abinci da magunguna daga hannun wani masanin kimiya a cikin al’umma.

Shugaban al’ummar, ya ci gaba da cewa; tuni an binne wadanda aka kashe, koda-yake ya ce; har yanzu ba a tuntubi wadanda suka sace mutanen ba.

“Hakika, an jefa al’ummar yankin baki-daya cikin bala’i, saboda harbe-harben da ‘yan bindigar suka yi a ranar Lahadi da daddare, har wasu suka tsere cikin daji,” in ji shugaban yankin.

Haka zalika, wata majiyar ‘yansanda a sashen Kagarko ta tabbatar da yin garkuwar da kuma faruwar al’amarin, duk da cewa; ‘yansandan ba su san ainihin adadin wadanda aka sace a harin ba.

Da aka tuntubi Kakakin Rundunar ’Yansandan Jihar Kaduna, DSP Hassan Mansur, shi ma ya tabbatar da sace-sacen da kashe-kashen da aka yi, inda ya ce; rundunar za ta fitar da cikakken rahoto kan lamarin.

“Har yanzu, rundunar ba ta samu cikakken bayani kan lamarin da ya faru a unguwar ta Kahir ba, amma za a fitar da cikakken rahoto kan lamarin bayan samun cikakken bayani,” in ji shi.

Jaridar Daily Trust ta ruwaito cewa, wasu ‘yan bindiga sun yi wa al’umma kawanya, a cikinsu har da Janjala.

Mutum 14 da suka hada da dan banga da matarsa da aka yi garkuwa da su a yankin makwanni uku da suka gabata, suna hannun ‘yan bindigar.

Kaduna
Sani Anwar
+ posts Bio
  • Sani Anwar
    https://hausa.leadership.ng/author/sani-anwar/
    Sojoji Sun Ceto Mutum 92 Tare Da Daƙile Harin Ƴan Ta’adda A Borno
  • Sani Anwar
    https://hausa.leadership.ng/author/sani-anwar/
    Uzodimma: Babu Dimokraɗiyya Idan Babu Hamayya
  • Sani Anwar
    https://hausa.leadership.ng/author/sani-anwar/
    Alamomin Fara Ruɓewar Hannu Bayan Ɗorin Gida
  • Sani Anwar
    https://hausa.leadership.ng/author/sani-anwar/
    Ministocin Da Suka Ajiye Muƙamansu Ba Su Samu Tikitin Takara Ba
Kaduna
Sulaiman
+ posts Bio
  • Sulaiman
    Ana Gudanar Da Taron Masana Ilmin Harkokin Kasar Sin Karo Na Uku
  • Sulaiman
    Sin: Ya Kamata Tarayyar Turai Ta Dubi Huldar Tattalin Arziki Da Ciniki Tsakaninta Da Sin Bisa Daidaito
  • Sulaiman
    An Gudanar Da Taron “Tattaunawar Magadan Garuruwa Na Duniya Na 2026” A Birnin Beijing
  • Sulaiman
    2027: Kasancewa Ɗan Arewa Kaɗai Ba Zai Tabbatar Da Samun Ƙuri’u Ba – Baba-Ahmed

MASU ALAKA

Fargabar Satar Mutane Ya Sa An Rufe Makarantu A Abuja Da Mararaba
Labaran Kasuwanci

Fargabar Satar Mutane Ya Sa An Rufe Makarantu A Abuja Da Mararaba

June 4, 2026
Arsenal Na Dab Da Ɗaukar Jeremy Monga Daga Leicester City
Wasanni

Arsenal Na Dab Da Ɗaukar Jeremy Monga Daga Leicester City

June 4, 2026
Atiku Ne Ya Fi Dacewa Da Tikitin Takara A ADC Amma Ya Kamata Ya Janye — Baba-Ahmed
Labarai

2027: Kasancewa Ɗan Arewa Kaɗai Ba Zai Tabbatar Da Samun Ƙuri’u Ba – Baba-Ahmed

June 4, 2026
Next Post
Wayoyin Wutar Lantarkin Adelabu Sun Zama Tamkar Igiyoyin Shanya

Wayoyin Wutar Lantarkin Adelabu Sun Zama Tamkar Igiyoyin Shanya

Discussion about this post

LABARAI MASU NASABA

Fargabar Satar Mutane Ya Sa An Rufe Makarantu A Abuja Da Mararaba

Fargabar Satar Mutane Ya Sa An Rufe Makarantu A Abuja Da Mararaba

June 4, 2026
Ana Gudanar Da Taron Masana Ilmin Harkokin Kasar Sin Karo Na Uku

Ana Gudanar Da Taron Masana Ilmin Harkokin Kasar Sin Karo Na Uku

June 4, 2026
Sin: Ya Kamata Tarayyar Turai Ta Dubi Huldar Tattalin Arziki Da Ciniki Tsakaninta Da Sin Bisa Daidaito

Sin: Ya Kamata Tarayyar Turai Ta Dubi Huldar Tattalin Arziki Da Ciniki Tsakaninta Da Sin Bisa Daidaito

June 4, 2026
Arsenal Na Dab Da Ɗaukar Jeremy Monga Daga Leicester City

Arsenal Na Dab Da Ɗaukar Jeremy Monga Daga Leicester City

June 4, 2026
An Gudanar Da Taron “Tattaunawar Magadan Garuruwa Na Duniya Na 2026” A Birnin Beijing

An Gudanar Da Taron “Tattaunawar Magadan Garuruwa Na Duniya Na 2026” A Birnin Beijing

June 4, 2026
Atiku Ne Ya Fi Dacewa Da Tikitin Takara A ADC Amma Ya Kamata Ya Janye — Baba-Ahmed

2027: Kasancewa Ɗan Arewa Kaɗai Ba Zai Tabbatar Da Samun Ƙuri’u Ba – Baba-Ahmed

June 4, 2026
Gwamnatin Tarayya Ta Mayar Da Ofishin NAGGW Zuwa Kano Domin Yaƙi Da Hamada

Gwamnatin Tarayya Ta Mayar Da Ofishin NAGGW Zuwa Kano Domin Yaƙi Da Hamada

June 4, 2026
Mambobin NYSC 4, Soja da Mutum 1 Sun Rasu A Hatsarin Mota A Adamawa

Mambobin NYSC 4, Soja da Mutum 1 Sun Rasu A Hatsarin Mota A Adamawa

June 4, 2026
Sarki Sanusi II Ya Tuɓe Rawanin Mai Unguwar Rikadawa Kan Badaƙalar Fili

Sarki Sanusi II Ya Tuɓe Rawanin Mai Unguwar Rikadawa Kan Badaƙalar Fili

June 4, 2026
Tawagar Masanan Dakile Yaduwar Cututtuka Ta Sin Ta Isa DR Congo

Tawagar Masanan Dakile Yaduwar Cututtuka Ta Sin Ta Isa DR Congo

June 3, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.