Game da ziyarar jagoran yankin Taiwan na kasar Sin Lai Ching-te a kasar Eswatini, kakakin ma’aikatar harkokin wajen kasar Sin Lin Jian ya bayyana a gun taron manema labaru da aka gudanar a yau Laraba 6 ga wannan wata cewa, ‘yan awaren yankin Taiwan ba za su cimma nasara ba, an kuma kalubalance su da su gyara kuskurensu cikin hanzari.
Lin Jian ya bayyana cewa, a kwanakin baya, Lai Ching-te ya yi watsi da ra’ayoyin kin amincewa daga bangarori daban daban, inda a asirce ya tashi ta jirgin sama zuwa kasar Eswatini, ya kuma shiga kasar bisa hadin gwiwa da Eswatini, wadda ta boye bayanan fasinjojin dake cikin jirgin.Kazalika, a kan hanyarsa ta komawa gida, wasu kasashen da abin ya shafa sun kin amincewa da ratsawar jirgin saman dake dauke da shi, amma Lai Ching-te ya ratsa a asirce ba tare da samun izini ba.
Lai Ching-te, ya bijirewa ikon mallakar kasa, da na kare sararin saman kasashen da abin ya shafa, wanda hakan ke da matukar hadari. Ziyararsa ta irin wannan hanya ta shaida cewa, aikin ‘yan aware na yankin Taiwan rufa-rufa ce, kana sassan kasa da kasa na adawa da hakan.
Game da batun harba makaman kaddamar da hari da kasar Japan ta yi zuwa wata kasar waje, kakakin ya yi nuni da cewa, hakan ya kara nanata cewa, masu ra’ayin rikau na kasar Japan, suna kokarin gaggauta aiwatar da yunkurin matakan soja, da sabawa ka’idojin tabbatar da tsaron kasa, da dokokin duniya, da kuma dokokin kasar baki daya. Wadannan matakai na kasar Japan sun sabawa na kiyaye tsaron kasa kadai. (Zainab Zhang)















Discussion about this post