ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Thursday, July 23, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

‘Yan Bindiga Sun Sace Amarya Da Ango A Katsina

by Sadiq
4 years ago
Amarya

‘Yan bindiga sun yi garkuwa da wasu sabbin ma’aurata bayan kashe jami’an sa-kai biyu a wani hari da suka kai unguwar Shola da ke birnin Katsina.

A cewar mazauna unguwar, ‘yan bindigar sun far mu su ne da misalin karfe 1:25 na dare, kuma sun shafe sa’a guda su na harbe-harbe.

  • 2023: Dan Yayan Buhari, Fatuhu Muhammed Ya Fice Daga APC
  • NDLEA Ta Cafke Tsohon Sojan Da Ke Wa ‘Yan Bindiga Safarar Miyagun Kwayoyi

Sun shaida cewa ‘yan sa-kan sun rasa rayukansu ne a kokarin hana garkuwa da ma’auranta, sannan an jikkata wasu daga cikinsu.

ADVERTISEMENT

Rahotanni na cewa dole ta sanya masu aikin sa-kai janye jiki bayan sun fahimci cewa ‘yan bindigar sun fi karfinsu.

Wani mazaunin unguwar ta Shola da ke cikin Katsina ya shaida wa manema labarai cewa :yan bindigar sun shiga unguwar ne a kan babura jiya dauke da bindigogi suna harbe-harbe.

LABARAI MASU NASABA

Rajistar Shirin Auren Gata Na Kano Kyauta Ce, In Ji Hukumar Hisbah

Sojoji Sun Daƙile ‘Yan Ta’adda Daga Karɓar Haraji A Yobe

Mutumin ya ce ‘yan bindigar sun fasa wani gida ta baya suka shiga. Al’amarin dai yayi sanadin mutuwar mutum biyu sanann mutum biyu suka jikkata.

Ya kuma ce baya ga ma’auratan akwai mutane da dama da aka sace, sai dai bai san adadinsu ba.

LEADERSHIP ta ruwaito cewa wannan ba shi ne karon farko da mahara ke aukawa unguwar Shola ba, ko a watan da ya gabata ma ‘yan bindiga sun shiga yankin.

Kakakin rundunar ‘yan sandan jihar Katsina, SP Gambo Isah, ya tabbatar da aukuwar harin, inda ya ce jami’ansu sun dukufa don kubutar da amarya da angon da aka yi awon gaba da su.

Gambo ya ce sun kubutar da wasu mutum shida da aka yi garkuwa da su a kauyen Tandama cikin karmar hukumar Danja, bayan wani samame da suka kai maboyar ‘yan bidiga.

Haka kuma, ya ce a yankin karamar hukumar Safana ma, sun yi nasarar kashe wani kasurgumin dan bindiga, Albdulkarim Faca-Faca da mutanansa bakwai a karshen mako, bayan barin wutar da wani jirgin yaki ya yi akan maboyarsu.

MASU ALAKA

Hisbah
Manyan Labarai

Rajistar Shirin Auren Gata Na Kano Kyauta Ce, In Ji Hukumar Hisbah

July 22, 2026
Sojoji Sun Daƙile ‘Yan Ta’adda Daga Karɓar Haraji A Yobe
Manyan Labarai

Sojoji Sun Daƙile ‘Yan Ta’adda Daga Karɓar Haraji A Yobe

July 22, 2026
Sojoji Sun Kashe ‘Yan Bindiga, Sun Ceto Mutane A Kaduna Da Filato
Manyan Labarai

Sojoji Sun Daƙile Yunƙurin Garkuwa Da Mutane, Sun Ceto Wasu Da Aka Sace A Zamfara, Katsina Da Kebbi

July 22, 2026
Next Post
Batun Hana Amfani Da Kayan ‘Yan Sanda Barkatai A Fina-finai

Batun Hana Amfani Da Kayan ‘Yan Sanda Barkatai A Fina-finai

LABARAI MASU NASABA

Taron AI Na Duniya: Kaya Ya Kwance A Tushen Kaba

Taron AI Na Duniya: Kaya Ya Kwance A Tushen Kaba

July 22, 2026
Inganta Makarantu: Gwamna Lawal Ya Sanya Hannu Kan Dokokin Gyaran Ilimi A Zamfara

Inganta Makarantu: Gwamna Lawal Ya Sanya Hannu Kan Dokokin Gyaran Ilimi A Zamfara

July 22, 2026
An Kaddamar Da Taron Kasa Da Kasa Na Bunkasa Hanyar Siliki Ta Dijital Na 2026

An Kaddamar Da Taron Kasa Da Kasa Na Bunkasa Hanyar Siliki Ta Dijital Na 2026

July 22, 2026
Amit Bhatia Na Tattaunawa Dangane Da Yiwuwar Sayen Kaso 30 Na Liverpool FC

Amit Bhatia Na Tattaunawa Dangane Da Yiwuwar Sayen Kaso 30 Na Liverpool FC

July 22, 2026
Asibitin Tafi Da Gidanka Na Jirgin Ruwan Sin Ya Nufi Kasashen Afrika Da Kudancin Asiya Domin Bayar Da Hidimomin Jin Kai

Asibitin Tafi Da Gidanka Na Jirgin Ruwan Sin Ya Nufi Kasashen Afrika Da Kudancin Asiya Domin Bayar Da Hidimomin Jin Kai

July 22, 2026
Iran Ta Musanta Zargin Ɓoye Makaman Nukiliya A Dutsen Kolang

Iran Ta Musanta Zargin Ɓoye Makaman Nukiliya A Dutsen Kolang

July 22, 2026
An Kafa Cibiyar Binciken Wayewar Kai Ta Duniya

An Kafa Cibiyar Binciken Wayewar Kai Ta Duniya

July 22, 2026
Kano

Gwamnatin Kano Ta Ƙaddamar Da Kwamitin Yaƙi da Shan Miyagun Ƙwayoyi

July 22, 2026
Yawan Man Fetur Da Gas Da Sin Ta Samar A 2025 Ya Kai Wani Sabon Matsayi

Yawan Man Fetur Da Gas Da Sin Ta Samar A 2025 Ya Kai Wani Sabon Matsayi

July 22, 2026
Yaya Da Kani Sun Mutu A Cikin Ramin Masai A Kano

Uba Da ‘Yarsa Sun Mutu Bayan Faɗawa Rijiya A Kano

July 22, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.