Ana fargabar cewa ‘yan bindiga sun sace mutane 32, ciki har da mata da ƙananan yara, a wani hari da suka kai garin Kadagen Kauru da ke ƙaramar hukumar Kauru a Jihar Kaduna.
Sun kuma kashe mutum ɗaya a yayin kai harin.
- Kasar Sin Ta Kaddamar Da Wata Manhajar AI Domin Taimakawa Aikin Gona
- Jihohin Nijeriya 5 Da Matsalar Tsaro Ta Fi Ƙamari A 2025 — Rahoto
Wani mazaunin garin ya ce harin ya faru da misalin ƙarfe 12:30 na dare.
Ya bayyana cewa daga cikin waɗanda aka sace akwai mata masu juna biyu da jarirai, kuma an jikkata mutane biyu amma sun warke.
Harin ya auku ne bayan wani makamancin irinsa da aka kai maƙwabtan ƙauyuka a baya-bayan nan, inda aka sace mutane da dama.
Mazauna yankin sun ce suna rayuwa cikin fargaba saboda yawaitar hare-haren ‘yan bindiga.
Shugaban ƙaramar hukumar Kauru ya tabbatar da faruwar lamarin, ya ce ana ɗaukar matakai.
Rundunar ‘yansandan Jihar Kaduna ta ce za ta binciki lamarin.
Jihar Kaduna dai ta daɗe tana fama da matsalar tsaro, musamman a yankunan karkara.















Discussion about this post