ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Thursday, June 4, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

‘Yan Bindiga Sun Sanya Wa Wani Kauye Tarar Miliyan 10 Kan Kashe Musu Dan Uwa A Katsina

by Sadiq
4 years ago
Katsina

Rundunar ‘yansandan Jihar Katsina ta tabbatar da tarar Naira miliyan 10 da ‘yan bindiga suka ci al’ummar garin Gobirawa a karamar hukumar Faskari bisa laifin kashe daya daga cikinsu.

Kakakin ‘yansandan jihar, SP Gambo Isah, wanda ya tabbatar da wannan harajin da ‘yan bindiga suka sanya wa al’ummomin saboda kashe daya daga cikinsu da ke aiki a dazuzzukan Karamar Hukumar Faskari ta Jihar Katsina, in ji Hakimin garin.

  • Adabin Zamanin Da Na Sin (3) Wakokin Daular Tang
  • An Gano Halittar Da Ta Fi Girma A Duniya

Sai dai kuma an kama wani mai suna Surajo Madawaki mai shekaru 50 da laifin hada baki da ‘yan bindigar.

ADVERTISEMENT

A cewar sanarwar, ta samu kiran gaggawa a ranar 19 ga watan Oktoba da misalin karfe 9:00 na safe, cewa wani dan ta’adda da ke dauke AK-47 ya kai wa wani matashi mai suna Yahaya Danbai dan shekaru 35 a kauyen Gobirawa da ke karamar hukumar Faskari ta Jihar Katsina hari.

An rawaito cewar manomin ya yi jarumta ya kuma yi galaba a kan wanda ya kai masa hari, ya kwace masa makamai tare da kashe dan ta’addan.

LABARAI MASU NASABA

Arsenal Na Dab Da Ɗaukar Jeremy Monga Daga Leicester City

Sarki Sanusi II Ya Tuɓe Rawanin Mai Unguwar Rikadawa Kan Badaƙalar Fili

Ya ce bayan kashe dan bindigar, ya dauki bindigar AK-47 da aka kwato zuwa gidan Hakiminsa, wanda maimakon ya kai rahoton lamarin ga ‘yansanda, sai dai ya kira wani da ake zargin kwamandan ‘yan ta’adda ne ya mika bindigar AK-47 da aka kwato gare shi.

Bayan haka ne shugaban kungiyar ‘yan ta’addan Hamisu, ya tattara ’yan kungiyarsa, suka kewaye kauyen, suka fito da manomin, suka kashe shi nan take, tare da sanya kudin fansa na Naira miliyan 10 ga al’umma saboda kashe daya daga cikin mambobinsu.

Sanarwar ta ci gaba da cewa, tun bayan faruwar lamarin, Hakimin gundumar, Surajo Madawaki ya boye kansa, har sai da tawagar ‘yansanda suka kamo shi, kuma tuni ya amsa laifinsa, inda ya kara da cewa Maiunguwa, ya musanta dukkan zargin da ake yi masa.

MASU ALAKA

Arsenal Na Dab Da Ɗaukar Jeremy Monga Daga Leicester City
Wasanni

Arsenal Na Dab Da Ɗaukar Jeremy Monga Daga Leicester City

June 4, 2026
Sarki Sanusi II Ya Tuɓe Rawanin Mai Unguwar Rikadawa Kan Badaƙalar Fili
Manyan Labarai

Sarki Sanusi II Ya Tuɓe Rawanin Mai Unguwar Rikadawa Kan Badaƙalar Fili

June 4, 2026
Tambuwal Ya Jajanta Wa Waɗanda Harin ’Yan Bindiga Ya Shafa A Sokoto, Ya Nemi A Ƙara Tsaro
Manyan Labarai

Tambuwal Ya Jajanta Wa Waɗanda Harin ’Yan Bindiga Ya Shafa A Sokoto, Ya Nemi A Ƙara Tsaro

June 3, 2026
Next Post
CMG Ya Gudanar Da Taron Tattaunawar Hadin Gwiwarsa Da Kafofin Watsa Labaru Na Afirka Na Shekarar 2022

CMG Ya Gudanar Da Taron Tattaunawar Hadin Gwiwarsa Da Kafofin Watsa Labaru Na Afirka Na Shekarar 2022

LABARAI MASU NASABA

Ana Gudanar Da Taron Masana Ilmin Harkokin Kasar Sin Karo Na Uku

Ana Gudanar Da Taron Masana Ilmin Harkokin Kasar Sin Karo Na Uku

June 4, 2026
Sin: Ya Kamata Tarayyar Turai Ta Dubi Huldar Tattalin Arziki Da Ciniki Tsakaninta Da Sin Bisa Daidaito

Sin: Ya Kamata Tarayyar Turai Ta Dubi Huldar Tattalin Arziki Da Ciniki Tsakaninta Da Sin Bisa Daidaito

June 4, 2026
Arsenal Na Dab Da Ɗaukar Jeremy Monga Daga Leicester City

Arsenal Na Dab Da Ɗaukar Jeremy Monga Daga Leicester City

June 4, 2026
An Gudanar Da Taron “Tattaunawar Magadan Garuruwa Na Duniya Na 2026” A Birnin Beijing

An Gudanar Da Taron “Tattaunawar Magadan Garuruwa Na Duniya Na 2026” A Birnin Beijing

June 4, 2026
Atiku Ne Ya Fi Dacewa Da Tikitin Takara A ADC Amma Ya Kamata Ya Janye — Baba-Ahmed

2027: Kasancewa Ɗan Arewa Kaɗai Ba Zai Tabbatar Da Samun Ƙuri’u Ba – Baba-Ahmed

June 4, 2026
Gwamnatin Tarayya Ta Mayar Da Ofishin NAGGW Zuwa Kano Domin Yaƙi Da Hamada

Gwamnatin Tarayya Ta Mayar Da Ofishin NAGGW Zuwa Kano Domin Yaƙi Da Hamada

June 4, 2026
Mambobin NYSC 4, Soja da Mutum 1 Sun Rasu A Hatsarin Mota A Adamawa

Mambobin NYSC 4, Soja da Mutum 1 Sun Rasu A Hatsarin Mota A Adamawa

June 4, 2026
Sarki Sanusi II Ya Tuɓe Rawanin Mai Unguwar Rikadawa Kan Badaƙalar Fili

Sarki Sanusi II Ya Tuɓe Rawanin Mai Unguwar Rikadawa Kan Badaƙalar Fili

June 4, 2026
Tawagar Masanan Dakile Yaduwar Cututtuka Ta Sin Ta Isa DR Congo

Tawagar Masanan Dakile Yaduwar Cututtuka Ta Sin Ta Isa DR Congo

June 3, 2026
Uba Sani Ya Sanya Hannu Kan Sabbin Dokoki A Bangaren Sauya Fannin Wuta, Noma, Da Muhalli

Uba Sani Ya Sanya Hannu Kan Sabbin Dokoki A Bangaren Sauya Fannin Wuta, Noma, Da Muhalli

June 3, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.