ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Wednesday, June 10, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

‘Yan Majalisa Na Amsar Cin Hanci Har Naira Miliyan 3 Kafin Su Gabatar Da Wani Ƙudiri – Kamfani.

by Sulaiman
10 months ago
Kamfani

Ɗan majalisar wakilai, Hon. Ibrahim Usman Auyo, mai wakiltar mazabar Hadejia, Auyo, da Kafin Hausa ta jihar Jigawa, ya yi zargin cewa, wasu ‘yan majalisar tarayya suna karbar cin hancin Naira miliyan 1 zuwa miliyan 3 kafin su gabatar da wani kudiri a wasu lokuta, ko kuma korafe-korafe a lokacin zaman majalisar.

 

Auyo, wanda aka fi sani da ‘Kamfani,’ ya bayyana hakan ne a wani faifan bidiyo da ya karade shafukan sada zumunta inda ya yi magana da harshen Hausa a lokacin da yake mayar da martani kan suka daga ‘yan mazabarsa.

ADVERTISEMENT
  • Sin Ta Kara Yawan Tallafinta Ga Hukumar Kula Da ‘Yan Gudun Hijirar Falasdinu
  • ’Yansanda Sun Kama Mutum 2 Da Bindigogi Da Alburusai A Filato

Ya musanta ikirarin cewa, wasu ‘yan majalisar suna rubuta kudiri ne saboda bukatun kansu ba na jama’arsu ba, amma ya tabbatar da cewa, akwai masu amsar cin hanci kafin su gabatar da wani kudiri a zauren majalisar.

 

LABARAI MASU NASABA

‘Yan Bindiga Sun Yi Kwanton-Ɓauna, Sun Kashe Sojoji 7 A Kaduna

Hauhawar Farashi Da Rashin Tsaro Ne Manyan Ƙalubalen Nijeriya — Gwamnatin Tarayya

A yayin da yake martani kan suka da ake yi masa na rashin gabatar da kudirori a gaban majalisar, ya bayyana cewa, “tun da na je Majalisar, ba bu wani dan mazabata da ya rubuto min wani kudiri ko bukata da zan gabatar a gaban Majalisa, duk zarge-zargen karya ne suke yi min, kuma idan har akwai, wani ya fito ya kalubalance ni,” inji shi.

 

“Hatta gabatar da kudirori da korafe-korafe a majalisar, wasu sai sun amso cin hancin kimanin naira miliyan 1, ko naira miliyan 2, ko naira miliyan 3, domin karantawa a zauren majalisar, bayan an karanta kudirin, kuma dole sai sun bibiyi ‘yan majalisa sama da 360 domin su goyi bayan a amince da kudirin.”

 

Dan majalisar ya kuma yi watsi da zarge-zargen da ake masa na cewa, ya yi watsi da shirye-shiryen tallafawa matasa a mazabarsa, inda ya ce galibin ayyukan da yake yi suna amfanar da matasa kai tsaye.

Kamfani
Sulaiman
+ postsBio
  • Sulaiman
    Wang Yi Ya Bukaci A Inganta Fahimtar Juna Ta Hanyar Tattaunawa Tsakanin Mabambantan Wayewar Kai
  • Sulaiman
    2027: ADC Ta Fara Sulhunta Mambobinta Da Ba Su Gamsu Da Zaɓen Fidda Gwani Ba A Kaduna
  • Sulaiman
    Bangaren Sin Ya Yi Kira Da a Dukufa Wajen Neman Mafita Ta Siyasa A Rikicin Ukraine
  • Sulaiman
    ‘Yan Bindiga Sun Kashe Jami’in Tsaro, Sun Yi Garkuwa Da Mutane Da Dama A Sokoto

MASU ALAKA

Sojoji Sun Kashe ‘Yan Bindiga, Sun Ceto Mutane A Kaduna Da Filato
Manyan Labarai

‘Yan Bindiga Sun Yi Kwanton-Ɓauna, Sun Kashe Sojoji 7 A Kaduna

June 10, 2026
Hauhawar Farashi Da Rashin Tsaro Ne Manyan Ƙalubalen Nijeriya — Gwamnatin Tarayya
Manyan Labarai

Hauhawar Farashi Da Rashin Tsaro Ne Manyan Ƙalubalen Nijeriya — Gwamnatin Tarayya

June 10, 2026
Mazauna Kuyello A Jihar Kaduna Na Cikin Zullumin Bayyanar ‘Yan Ta’addar Ansaru
Manyan Labarai

Yadda ‘Yan Bindiga Suka Kashe Mijina Da ’Ya’yana 4 A Lokaci Ɗaya — Bazawara

June 10, 2026
Next Post
An Samu Gagarumin Ci Gaba Kan Habaka Fasahar Zamani Ta Sin Yayin Shirin Raya Kasa Na Shekaru Biyar Na 14 

An Samu Gagarumin Ci Gaba Kan Habaka Fasahar Zamani Ta Sin Yayin Shirin Raya Kasa Na Shekaru Biyar Na 14 

LABARAI MASU NASABA

Kano: Hisbah Ta Tantance Mutane 720 Waɗanda Za A Yi Wa Auren Gata

Kano: Hisbah Ta Tantance Mutane 720 Waɗanda Za A Yi Wa Auren Gata

June 10, 2026
Kotu Ta Bayar Da Umarnin Kamo Ɗan Takarar Gwamnan Bauchi Na NDC, Ibrahim Kashim

Kotu Ta Bayar Da Umarnin Kamo Ɗan Takarar Gwamnan Bauchi Na NDC, Ibrahim Kashim

June 10, 2026
Gwamnatin Jigawa Ta Dage Komawa Makaranta Saboda Kidayar Jama’a

‘Yansanda Sun Kama Masu Satar Mutane, ‘Yan Fashi A Jigawa, Sun Ƙwato Makamai

June 10, 2026
Sojoji Sun Kashe ‘Yan Bindiga, Sun Ceto Mutane A Kaduna Da Filato

‘Yan Bindiga Sun Yi Kwanton-Ɓauna, Sun Kashe Sojoji 7 A Kaduna

June 10, 2026
Hauhawar Farashi Da Rashin Tsaro Ne Manyan Ƙalubalen Nijeriya — Gwamnatin Tarayya

Hauhawar Farashi Da Rashin Tsaro Ne Manyan Ƙalubalen Nijeriya — Gwamnatin Tarayya

June 10, 2026
Mazauna Kuyello A Jihar Kaduna Na Cikin Zullumin Bayyanar ‘Yan Ta’addar Ansaru

Yadda ‘Yan Bindiga Suka Kashe Mijina Da ’Ya’yana 4 A Lokaci Ɗaya — Bazawara

June 10, 2026
Wang Yi Ya Bukaci A Inganta Fahimtar Juna Ta Hanyar Tattaunawa Tsakanin Mabambantan Wayewar Kai

Wang Yi Ya Bukaci A Inganta Fahimtar Juna Ta Hanyar Tattaunawa Tsakanin Mabambantan Wayewar Kai

June 9, 2026
ADC Ta Fara Sayar Da Fom Din Takara Kafin Babban Taron Jam’iyya

2027: ADC Ta Fara Sulhunta Mambobinta Da Ba Su Gamsu Da Zaɓen Fidda Gwani Ba A Kaduna

June 9, 2026
Bangaren Sin Ya Yi Kira Da a Dukufa Wajen Neman Mafita Ta Siyasa A Rikicin Ukraine

Bangaren Sin Ya Yi Kira Da a Dukufa Wajen Neman Mafita Ta Siyasa A Rikicin Ukraine

June 9, 2026
Ambaliyar Ruwa Ta Lalata Gidaje 14,940 A Sokoto

‘Yan Bindiga Sun Kashe Jami’in Tsaro, Sun Yi Garkuwa Da Mutane Da Dama A Sokoto

June 9, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.