Sarkin Kano na 16, Muhammadu Sanusi II, ya zargi ‘yan siyasan Nijeriya da zagon kasa ga ci gaban kasar ta hanyar daukar mukaman gwamnati a matsayin gadon gidansu a maimakon amanar jama’a.
Da yake jawabi a ranar Laraba a yayin taro karo na 15 mai taken, “ya Isa haka” da ya gudana a jihar Legas, Sanusi II ya ce manyan ‘yan siyasa a fadin Nijeriya, suna ci gaba da yin zagon kasa ga ci gaban kasa saboda suna fifita kansu, iyalansu da abokan huldarsu fiye da kasar da ‘yan kasarta.
- Nazarin CGTN: Fahimtar Matsayin Sin Cikin Yanayin Tattalin Arzikin Duniya Na Da Muhimmanci
- Katsina Ta Amince Da Bayar Da Alawus Na Naira 30,000 Duk Wata Ga Malaman Karkara
Ya yi takaicin cewa, gazawar Nijeriya a wasu wurare ba haka nan take ba, face sakamakon shugabanci na son kai.
A cewarsa, “mukaman gwamnati na su ne, da iyalansu, da mutanen da ke kusa da su, babu ruwansu da ‘yan kasar. Amma mukaman gwamnati na ‘yan kasa ne.”
Sarki Sanusi na II ya yi kira ga matasan Nijeriya da su yi watsi da tsarin da ‘yan siyasa marasa kishin kasa suka kafa na amfani da “kabilanci, rikice-rikicen addini, da kuma son kai,” a maimakon haka, su hada kai don gina kasa da za ta cika mafarkanta.
Ya jaddada cewa, ikon kasa yana hannun ‘yan kasa ne, ba ‘yan siyasa ba, ya kara da cewa, kowane mutum yana da rawar da zai taka a hakkinsa don tallafawa Nijeriya.
ADVERTISEMENT














