ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Thursday, June 4, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

‘Yansanda Sun Bankado Maboyar ‘Yan Bindiga, Sun Cafke Mutum 6 A Nasarawa

by Sadiq
3 years ago
Nasarawa

Rundunar ‘yansandan Jihar Nasarawa ta ce ta kai farmaki maboyar masu garkuwa da mutane a kauyen Kiguna da ke cikin garin Lafiya, babban birnin jihar, tare da cafke wasu mutane shida.

Kwamishinan ‘yan sandan jihar, Maiyaki Muhammed-Baba, ne ya bayyana hakan a wani taron manema labarai da ya gabatar domin gabatar da nasarorin da rundunar ta samu daga farkon watan Janairu, a ranar Litinin a Lafiya.

  • Wannan Sabuwar Tashar Jirgin Ruwa Ta Shaida Wani Tunani Mai Muhimmanci
  • Sin: An Samu Karuwar Sayayyar Amfanin Gona Ta Yanar Gizo A 2022 

Muhammed-Baba ya ce, a ranar 12 ga watan Janairu da misalin karfe 4:00 na safe, jami’an ‘yan sandan da ke aiki da sashen Assakio, bisa ga bayanan da suka samu, sun kai samame maboyar tare da kama wasu mutane hudu.

ADVERTISEMENT

“An kwato AK-47 guda daya a cikin gidan, sai kuma sauran makamai da aka kwato,” in ji shi.

Kwamishinan ‘yansandan ya kuma ce a ranar 13 ga watan Janairu, jami’an ‘yansanda daga wannan sashe sun kama shugaban kungiyar masu garkuwa da mutane.

LABARAI MASU NASABA

Rikicin Manoma Da Makiyaya Ya Yi Sanadin Mutuwar Mutane 7 A Bauchi

Arsenal Na Dab Da Ɗaukar Jeremy Monga Daga Leicester City

Ya kara da cewa, tun daga farkon shekarar nan zuwa yau, ‘yansanda sun kama wasu mutane 21 da ake zargi da aikata laifuka daban-daban.

Mohammed-Baba ya bayyana wadanda ake zargin sun hada da: ‘yan fashi 16, sai wasu da ake zargin barayin shanu ne guda guda bigu da masu satar babura guda biyu.

Ya lissafa abubuwan baje kolin da aka kwato daga hannun wadanda ake zargin kamar: motoci hudu, makamai da shanu da sauransu.

Kwamishinan, ya ce za a gurfanar da wadanda ake zargin a gaban kotu bayan kammala bincike.

Sai dai ya ce galibin wadanda ake zargin sun amsa laifukan da suka aikata kuma suna taimaka wa ‘yansanda wajen gudanar da bincike.

Mohammed-Baba ya danganta nasarar da rundunar ta samu da goyon bayan jama’a da sarakunan gargajiya da sauran hukumomin tsaro da kuma kafafen yada labarai.

Don haka ya yi kira ga jama’a da su bai wa ‘yansanda sahihin bayanan da za su taimaka musu wajen rage yawaitar aikata laifuka a jihar.

MASU ALAKA

Rikicin Manoma Da Makiyaya Ya Yi Sanadin Mutuwar Mutane 7 A Bauchi
Manyan Labarai

Rikicin Manoma Da Makiyaya Ya Yi Sanadin Mutuwar Mutane 7 A Bauchi

June 4, 2026
Arsenal Na Dab Da Ɗaukar Jeremy Monga Daga Leicester City
Wasanni

Arsenal Na Dab Da Ɗaukar Jeremy Monga Daga Leicester City

June 4, 2026
Sarki Sanusi II Ya Tuɓe Rawanin Mai Unguwar Rikadawa Kan Badaƙalar Fili
Manyan Labarai

Sarki Sanusi II Ya Tuɓe Rawanin Mai Unguwar Rikadawa Kan Badaƙalar Fili

June 4, 2026
Next Post
An Gurfanar Da Manoma 3 Kan Zargin Sace Wata Mata A Abuja

An Gurfanar Da Manoma 3 Kan Zargin Sace Wata Mata A Abuja

LABARAI MASU NASABA

Takunkumin Amurka Ya Haifar Da Mummunan Tasiri Ga Tsarin Samar Da Kayan Latironi Na Duniya

Takunkumin Amurka Ya Haifar Da Mummunan Tasiri Ga Tsarin Samar Da Kayan Latironi Na Duniya

June 4, 2026
Rikicin Manoma Da Makiyaya Ya Kashe Mutane 7, Ya Jikkata 6 A Bauchi

Rikicin Manoma Da Makiyaya Ya Kashe Mutane 7, Ya Jikkata 6 A Bauchi

June 4, 2026
Rikicin Manoma Da Makiyaya Ya Yi Sanadin Mutuwar Mutane 7 A Bauchi

Rikicin Manoma Da Makiyaya Ya Yi Sanadin Mutuwar Mutane 7 A Bauchi

June 4, 2026
Mun Kaɗu Matuƙa Kan Labarin Mutuwar ‘Yan Mauludi A Hanyar Saminaka – Gwamnan Kaduna

Gwamna Sani Ya Kashe Sama Da Naira Biliyan Ɗaya Kan Tallafin Ɗalibai A Kaduna – Kwamishina

June 4, 2026
Sin Ta Ware Kudi Har Yuan Biliyan 99.9 Domin Tallafawa Kula Da Lafiyar Yara A 2026

Sin Ta Ware Kudi Har Yuan Biliyan 99.9 Domin Tallafawa Kula Da Lafiyar Yara A 2026

June 4, 2026
Tasirin Nasarar Da Kasar Sin Ta Cimma A Fannin Kakkabe Matsanancin Talauci

Tasirin Nasarar Da Kasar Sin Ta Cimma A Fannin Kakkabe Matsanancin Talauci

June 4, 2026
Sabbin Ra’ayoyin Ci Gaba: Manufofin Zamani Na Zamanantarwa

Sabbin Ra’ayoyin Ci Gaba: Manufofin Zamani Na Zamanantarwa

June 4, 2026
Fargabar Satar Mutane Ya Sa An Rufe Makarantu A Abuja Da Mararaba

Fargabar Satar Mutane Ya Sa An Rufe Makarantu A Abuja Da Mararaba

June 4, 2026
Ana Gudanar Da Taron Masana Ilmin Harkokin Kasar Sin Karo Na Uku

Ana Gudanar Da Taron Masana Ilmin Harkokin Kasar Sin Karo Na Uku

June 4, 2026
Sin: Ya Kamata Tarayyar Turai Ta Dubi Huldar Tattalin Arziki Da Ciniki Tsakaninta Da Sin Bisa Daidaito

Sin: Ya Kamata Tarayyar Turai Ta Dubi Huldar Tattalin Arziki Da Ciniki Tsakaninta Da Sin Bisa Daidaito

June 4, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.