ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Wednesday, September 9, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

’Yansanda Sun Kama Masu Laifi 3,081 A Kano A 2025

by Sadiq Usman
8 months ago

Rundunar ’Yansandan Jihar Kano ta ce ta kama mutane 3,081 da ake zargi da aikata laifuka daban-daban a faɗin jihar a shekarar 2025.

Kwamishinan ’Yansanda na jihar, CP Ibrahim Bakori ne, ya bayyana hakan a ranar Talata yayin taron manema labarai na ƙarshen shekara da aka gudanar a hedikwatar ’yansandan da ke Bompai a Kano.

  • An Kashe Mutane 8 A Wasu Sabbin Hare-hare A Kebbi, ‘Yansanda Sun Fara Bincike
  • Kotu Ta Tisa Ƙeyar Malami Zuwa Gidan Yarin Kuje

Ya ce an yi kamen ne daga ranar 1 ga watan Janairu zuwa 30 ga watan Disamba, 2025.

ADVERTISEMENT

An gudanar da ayyukan kamen a sassan ’yansanda 78, rundunonin yankuna 11 da kuma sassan aiki na musamman guda bakwai.

Ayyukan sun haɗa da haɗin gwiwar sassan aiki, bincike da tattara bayanan sirri na rundunar.

LABARAI MASU NASABA

Hormuz: Iran Ta Kai Muggan Hare-hare Kan Sansanin Amurka A Jordan

ASUU Ta Yi Barazanar Yajin Aiki A Jami’ar Jihar Sokoto

A cewarsa, mafi yawan waɗanda aka kama ’yan daba ne.

An kama kimanin 2,350 bisa laifin tayar da hankalin jama’a, satar wayoyin hannu da makamantan laifuka, musamman a cikin birnin Kano.

Sauran waɗanda aka kama sun haɗa da mutane 146 da ake zargi da fashi da makami, mutane 50 da ake zargi da garkuwa da mutane, mutane 112 da ake zargi da safarar miyagun ƙwayoyi, mutane 85 da ake zargi da satar motoci, mutane 45 da ake zargi da satar adaidaita sahu, mutane 83 da ake zargi da satar babura, mutane 154 da ake zargi da sata, da kuma mutane 36 da ake zargi da damfara.

Kwamishinan ya ce an samu waɗannan nasarori ne bayan tantance matsalar tsaro da aka yi bayan shigar ofis a ranar 17 ga watan Maris, 2025.

Tantancewar ta nuna cewa barazanar tsaro a faɗin ƙananan hukumomi 44 na jihar sun haɗa da harkar daba, shan miyagun ƙwayoyi, garkuwa da mutane, shigowar ’yan bindiga ta yankunan kan iyaka, da kuma rikicin manoma da makiyaya.

Ya ce rundunar ta ɗauki matakai daban-daban don magance matsalolin.

Matakan sun haɗa da aikin ’yansanda bisa bayanan sirri, ƙarfafa hulɗa da al’umma, haɗin gwiwa da sauran jami’an tsaro wajen sintiri a yankunan kan iyaka, horar da jami’ai, ƙarfafa sashen yaƙi da laifukan Intanet, da wayar da kan jama’a.

Bakori ya kuma ce aikin da aka ƙaddamar mai suna “Operation Kukan Kura” ya rage yawan faɗan daba da satar wayoyi.

Ya ƙara da cewa rundunar ta kuɓutar da mutane 14 da aka sace, tare da ƙwato bindigogi, makamai masu hatsari, miyagun ƙwayoyi, motocin sata da sauran kayayyakin laifi.

Kwamishinan ya yaba wa Gwamnatin Jihar Kano, sarakunan gargajiya da shugabannin addini, shugabannin al’umma da kuma kafafen yaɗa labarai bisa goyon bayan da suka bayar.

Ya tabbatar wa al’ummar jihar cewa rundunar za ta ci gaba da inganta waɗannan nasarori a shekarar 2026 ta hanyar ƙara sintiri, inganta tattara bayanan sirri da kuma ƙarfafa haɗin gwiwa da al’umma domin tabbatar da ɗorewar zaman lafiya da tsaro a jihar.

MASU ALAKA

Iran Ta Musanta Ikirarin Trump Tare Da Zafafa Hare-hare Kan Isra’ila
Manyan Labarai

Hormuz: Iran Ta Kai Muggan Hare-hare Kan Sansanin Amurka A Jordan

September 9, 2026
ASUU Ta Yi Barazanar Yajin Aiki A Jami’ar Jihar Sokoto
Labarai

ASUU Ta Yi Barazanar Yajin Aiki A Jami’ar Jihar Sokoto

September 9, 2026
Taron PDP Na Ƙasa: Ɓangaren Wike Ya Kafa Sabon NWC A Abuja
Labarai

PDP Ta Musanta Mara Wa APM Baya A Bauchi

September 9, 2026
Next Post
Shugaba Xi Zai Gabatar Da Sakon Murnar Sabuwar Shekarar 2026

Shugaba Xi Zai Gabatar Da Sakon Murnar Sabuwar Shekarar 2026

LABARAI MASU NASABA

Iran Ta Musanta Ikirarin Trump Tare Da Zafafa Hare-hare Kan Isra’ila

Hormuz: Iran Ta Kai Muggan Hare-hare Kan Sansanin Amurka A Jordan

September 9, 2026
ASUU Ta Yi Barazanar Yajin Aiki A Jami’ar Jihar Sokoto

ASUU Ta Yi Barazanar Yajin Aiki A Jami’ar Jihar Sokoto

September 9, 2026
Taron PDP Na Ƙasa: Ɓangaren Wike Ya Kafa Sabon NWC A Abuja

PDP Ta Musanta Mara Wa APM Baya A Bauchi

September 9, 2026
Sojoji

Sojoji Sun Dakile Hare-Hare, Sun Ceto Mutane 12 A Zamfara

September 9, 2026
Batun AI Zai Fi Daukar Hankali A Bikin Baje Kolin Fasahar Zamani Ta Duniya Karo Na 5

Batun AI Zai Fi Daukar Hankali A Bikin Baje Kolin Fasahar Zamani Ta Duniya Karo Na 5

September 8, 2026
Gwamna Radda Ya Samu Goyon Bayan APC A Katsina Gabanin Zaɓen 2027

Gwamna Radda Ya Samu Goyon Bayan APC A Katsina Gabanin Zaɓen 2027

September 8, 2026
Cinikin Wajen Sin Ya Ci Gaba Da Samun Bunkasa Cikin Sauri A Watanni Takwas Na Farkon Bana

Cinikin Wajen Sin Ya Ci Gaba Da Samun Bunkasa Cikin Sauri A Watanni Takwas Na Farkon Bana

September 8, 2026
'Yan Bindiga

‘Yan Bindiga Sun Kashe 2, Sun Yi Garkuwa Da 26 A Kaduna

September 8, 2026
Binciken CGTN Ya Nuna Gamsuwa Da Yadda Baje Kolin CIFTIS Ke Shaida Karfin Gwiwar Sin A Fannin Kara Fadada Bude Kofa Bisa Babban Matsayi

Binciken CGTN Ya Nuna Gamsuwa Da Yadda Baje Kolin CIFTIS Ke Shaida Karfin Gwiwar Sin A Fannin Kara Fadada Bude Kofa Bisa Babban Matsayi

September 8, 2026
Yadda Taron Tattalin Arziki Da Zuba Jari Na Kwana Biyu Ya Gudana A Katsina

Gwamna Radda Ya Gabatar Da Kasafin N828.6bn Na 2027

September 8, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.