ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Friday, June 26, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

’Yansanda Sun Kama Masu Laifi 3,081 A Kano A 2025

by Sadiq Usman
6 months ago

Rundunar ’Yansandan Jihar Kano ta ce ta kama mutane 3,081 da ake zargi da aikata laifuka daban-daban a faɗin jihar a shekarar 2025.

Kwamishinan ’Yansanda na jihar, CP Ibrahim Bakori ne, ya bayyana hakan a ranar Talata yayin taron manema labarai na ƙarshen shekara da aka gudanar a hedikwatar ’yansandan da ke Bompai a Kano.

  • An Kashe Mutane 8 A Wasu Sabbin Hare-hare A Kebbi, ‘Yansanda Sun Fara Bincike
  • Kotu Ta Tisa Ƙeyar Malami Zuwa Gidan Yarin Kuje

Ya ce an yi kamen ne daga ranar 1 ga watan Janairu zuwa 30 ga watan Disamba, 2025.

ADVERTISEMENT

An gudanar da ayyukan kamen a sassan ’yansanda 78, rundunonin yankuna 11 da kuma sassan aiki na musamman guda bakwai.

Ayyukan sun haɗa da haɗin gwiwar sassan aiki, bincike da tattara bayanan sirri na rundunar.

LABARAI MASU NASABA

Gwamna Lawal Ya Yi Alƙawarin Bayar Da Ƙarin Tallafi Ga Jami’an Tsaro A Zamfara

Dangote Ya Rage Farashin Fetur Zuwa N1,125 Kan Kowace Lita

A cewarsa, mafi yawan waɗanda aka kama ’yan daba ne.

An kama kimanin 2,350 bisa laifin tayar da hankalin jama’a, satar wayoyin hannu da makamantan laifuka, musamman a cikin birnin Kano.

Sauran waɗanda aka kama sun haɗa da mutane 146 da ake zargi da fashi da makami, mutane 50 da ake zargi da garkuwa da mutane, mutane 112 da ake zargi da safarar miyagun ƙwayoyi, mutane 85 da ake zargi da satar motoci, mutane 45 da ake zargi da satar adaidaita sahu, mutane 83 da ake zargi da satar babura, mutane 154 da ake zargi da sata, da kuma mutane 36 da ake zargi da damfara.

Kwamishinan ya ce an samu waɗannan nasarori ne bayan tantance matsalar tsaro da aka yi bayan shigar ofis a ranar 17 ga watan Maris, 2025.

Tantancewar ta nuna cewa barazanar tsaro a faɗin ƙananan hukumomi 44 na jihar sun haɗa da harkar daba, shan miyagun ƙwayoyi, garkuwa da mutane, shigowar ’yan bindiga ta yankunan kan iyaka, da kuma rikicin manoma da makiyaya.

Ya ce rundunar ta ɗauki matakai daban-daban don magance matsalolin.

Matakan sun haɗa da aikin ’yansanda bisa bayanan sirri, ƙarfafa hulɗa da al’umma, haɗin gwiwa da sauran jami’an tsaro wajen sintiri a yankunan kan iyaka, horar da jami’ai, ƙarfafa sashen yaƙi da laifukan Intanet, da wayar da kan jama’a.

Bakori ya kuma ce aikin da aka ƙaddamar mai suna “Operation Kukan Kura” ya rage yawan faɗan daba da satar wayoyi.

Ya ƙara da cewa rundunar ta kuɓutar da mutane 14 da aka sace, tare da ƙwato bindigogi, makamai masu hatsari, miyagun ƙwayoyi, motocin sata da sauran kayayyakin laifi.

Kwamishinan ya yaba wa Gwamnatin Jihar Kano, sarakunan gargajiya da shugabannin addini, shugabannin al’umma da kuma kafafen yaɗa labarai bisa goyon bayan da suka bayar.

Ya tabbatar wa al’ummar jihar cewa rundunar za ta ci gaba da inganta waɗannan nasarori a shekarar 2026 ta hanyar ƙara sintiri, inganta tattara bayanan sirri da kuma ƙarfafa haɗin gwiwa da al’umma domin tabbatar da ɗorewar zaman lafiya da tsaro a jihar.

MASU ALAKA

Gwamna Lawal Ya Yi Alƙawarin Bayar Da Ƙarin Tallafi Ga Jami’an Tsaro A Zamfara
Labarai

Gwamna Lawal Ya Yi Alƙawarin Bayar Da Ƙarin Tallafi Ga Jami’an Tsaro A Zamfara

June 25, 2026
NNPCL Ya Rage Farashin Man Fetur Zuwa ₦860 Kan Kowacce Lita – IPMAN
Labarai

Dangote Ya Rage Farashin Fetur Zuwa N1,125 Kan Kowace Lita

June 25, 2026
Gwamna Yusuf Ya Naɗa Muhuyi A Matsayin Shugaban Kwamitin Yaƙi Da Miyagun Ƙwayoyi A Kano
Manyan Labarai

Gwamna Yusuf Ya Naɗa Muhuyi A Matsayin Shugaban Kwamitin Yaƙi Da Miyagun Ƙwayoyi A Kano

June 25, 2026
Next Post
Shugaba Xi Zai Gabatar Da Sakon Murnar Sabuwar Shekarar 2026

Shugaba Xi Zai Gabatar Da Sakon Murnar Sabuwar Shekarar 2026

LABARAI MASU NASABA

Sin Da Amurka Sun Amince Da Kafa Majalisar Kasuwanci

Sin Da Amurka Sun Amince Da Kafa Majalisar Kasuwanci

June 25, 2026
Mukaddashiyar Shugaban Venezuela Ta Yi Godiya Da Aniyar Sin Ta Ba Su Agaji

Mukaddashiyar Shugaban Venezuela Ta Yi Godiya Da Aniyar Sin Ta Ba Su Agaji

June 25, 2026
Shugabar Namibia Ta Kaddamar Da Dakin Baje Kolin Kimiyya Da Sinawa Suka Gina

Shugabar Namibia Ta Kaddamar Da Dakin Baje Kolin Kimiyya Da Sinawa Suka Gina

June 25, 2026
Gwamna Lawal Ya Yi Alƙawarin Bayar Da Ƙarin Tallafi Ga Jami’an Tsaro A Zamfara

Gwamna Lawal Ya Yi Alƙawarin Bayar Da Ƙarin Tallafi Ga Jami’an Tsaro A Zamfara

June 25, 2026
Salon Jagorancin Kasar Sin Na Ingiza Samar Da Ci Gaba Mai Nagarta

Salon Jagorancin Kasar Sin Na Ingiza Samar Da Ci Gaba Mai Nagarta

June 25, 2026
NNPCL Ya Rage Farashin Man Fetur Zuwa ₦860 Kan Kowacce Lita – IPMAN

Dangote Ya Rage Farashin Fetur Zuwa N1,125 Kan Kowace Lita

June 25, 2026
Adadin Injunan Samar Da Wutar Lantarki Da Sin Ya Wuce Kilowatts Awa Biliyan 4, Wato Ya Kai Ga Matsayi Na Farko A Duniya

Adadin Injunan Samar Da Wutar Lantarki Da Sin Ya Wuce Kilowatts Awa Biliyan 4, Wato Ya Kai Ga Matsayi Na Farko A Duniya

June 25, 2026
Gwamna Yusuf Ya Naɗa Muhuyi A Matsayin Shugaban Kwamitin Yaƙi Da Miyagun Ƙwayoyi A Kano

Gwamna Yusuf Ya Naɗa Muhuyi A Matsayin Shugaban Kwamitin Yaƙi Da Miyagun Ƙwayoyi A Kano

June 25, 2026
Wani Gidan Adana Kayan Tarihi Na Sin Ya Fitar Da Rahoton Yadda Dakarun Japan Suka Rika Zubawa Mutane Jinin Dabbobi Yayin Yakin Duniya Na Biyu

Wani Gidan Adana Kayan Tarihi Na Sin Ya Fitar Da Rahoton Yadda Dakarun Japan Suka Rika Zubawa Mutane Jinin Dabbobi Yayin Yakin Duniya Na Biyu

June 25, 2026
Wang Yi Ya Yi Kira Da A Gaggauta Bude Mashigin Hormuz

Wang Yi Ya Yi Kira Da A Gaggauta Bude Mashigin Hormuz

June 25, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.