ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Sunday, December 21, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

‘Yar Sanda Da Wata Sun Shiga Hannu Kan Sato Yara 5 Daga Sakkwato

by Sadiq
2 years ago
Sanda

Wata ’yar sanda mai mukamin ASP da wata mai taimaka mata sun shiga hannu bisa zargin sato kananan yara biyar daga Jihar Sakkwato zuwa Abuja.

Ana zargin ’yar sandar, ASP Kulu da sato yaran ciki har da jaririya ’yar makonni biyu da haihuwa.

  • ‘Yan Kasuwar Afrika Sun Gano Zarafi Mai Kyau A Canton Fair
  • Hukumar NCAA Ta Karyata Rahoton Sayen Mota Ta Fiye Da Naira Miliyan 250

’Yansandan sun kama ASP Kulu da mai taimaka mata a Abuja, lokacin da suke dawowa daga Sakkwato a cikin bas din haya mai dauke da mutane 18.

ADVERTISEMENT

Ana tsakar tafiya ne dai sauran fasinjojin suka lura cewa babu wadda ta shayar da jaririyar ‘yar makonni biyu.

Wani fasinja a motar ya ce: “A ranar Asabar 27 ga watan Afrilu muna cikin tafiya sai muka lura yaran ba sa cikin hayyacinsu kuma ba sa magana.

LABARAI MASU NASABA

Akpabio, Ganduje, Ogundoyin Sun Halarci Naɗa Seyi Tinubu Sarauta

Tashar Teku Ta Ciniki Mai ‘Yanci Ta Hainan Ta Bude Sabon Babin Hadin Gwiwar Sin Da Kasashen Afirka

“Don haka, yayin da muka sauka a Deidei, sai muka tambaye su don tabbatar da ko ’ya’yansu ne, sai suka ce eh, ’ya’yansu ne.

“Ita ’yar sandar da ke rike da jaririyar ta shaida mana cewa ba ta iya shayar da ita ne saboda tana fama da ciwon nono.

“Muna jin haka sai muka sanar da ’yansanda kuma da zuwa suka kai wadanda ake zargin ofishinsu da ke Gwagwa.

“A jiya Litinin kuma aka tura su zuwa babban ofishin ’yansanda na Abuja tare da yaran da suka sato.”

An gano ASP Kulu, tana aiki da rundunar ’yansanda a yankin Kubwa da ke Abuja.

An kuma gano cewa akwai wasu yaran da ke gidanta a Deidei, kuma shaidu sun tabbatar da ganin ta da yara da dama a makonnin da suka gabata.

Kakakin rundunar Abuja, SP Josephine Adeh ta tabbatar da faruwar lamarin, inda ta ce suna gudanar da bincike.

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

Akpabio, Ganduje, Ogundoyin Sun Halarci Naɗa Seyi Tinubu Sarauta
Manyan Labarai

Akpabio, Ganduje, Ogundoyin Sun Halarci Naɗa Seyi Tinubu Sarauta

December 21, 2025
Tashar Teku Ta Ciniki Mai ‘Yanci Ta Hainan Ta Bude Sabon Babin Hadin Gwiwar Sin Da Kasashen Afirka
Ra'ayi Riga

Tashar Teku Ta Ciniki Mai ‘Yanci Ta Hainan Ta Bude Sabon Babin Hadin Gwiwar Sin Da Kasashen Afirka

December 21, 2025
Tinubu
Manyan Labarai

Dambarwar Naɗa Muƙamai Da Soke Su A Gwamnatin Tinubu

December 21, 2025
Next Post
Wa Suka Fi Cancanta A Nada Ministocin Tinubu?

Da Dumi-Dumi: Gwamnatin Tarayya Ta Kara Wa Ma'aikata Albashi

LABARAI MASU NASABA

Yankin Rijiyoyin Mai Na Teku Mafi Girma Na Kasar Sin Ya Ba Da Rahoton Yawan Mai Da Iskar Gas Da Ya Fitar A Shekara

Yankin Rijiyoyin Mai Na Teku Mafi Girma Na Kasar Sin Ya Ba Da Rahoton Yawan Mai Da Iskar Gas Da Ya Fitar A Shekara

December 21, 2025
An Bukaci Bunkasa Fannin Kiwo A Hadin Gwiwar Sin Da Afirka

An Bukaci Bunkasa Fannin Kiwo A Hadin Gwiwar Sin Da Afirka

December 21, 2025
Akpabio, Ganduje, Ogundoyin Sun Halarci Naɗa Seyi Tinubu Sarauta

Akpabio, Ganduje, Ogundoyin Sun Halarci Naɗa Seyi Tinubu Sarauta

December 21, 2025
Tashar Teku Ta Ciniki Mai ‘Yanci Ta Hainan Ta Bude Sabon Babin Hadin Gwiwar Sin Da Kasashen Afirka

Tashar Teku Ta Ciniki Mai ‘Yanci Ta Hainan Ta Bude Sabon Babin Hadin Gwiwar Sin Da Kasashen Afirka

December 21, 2025
Tinubu

Dambarwar Naɗa Muƙamai Da Soke Su A Gwamnatin Tinubu

December 21, 2025
Zaben Fidda Gwani A APC: Sanatocin Jigawa Sun Rasa Tikitin Komawa Majalisa

APC Za Ta Gudanar Da Babban Taronta Na Kasa A Watan Maris

December 21, 2025
Mun Shirya Tsaf Domin Lashe Gasar AFCON Ta Bana – Bassey

Mun Shirya Tsaf Domin Lashe Gasar AFCON Ta Bana – Bassey

December 21, 2025
Sarakuna Na Da Rawar Takawa Wajen Kare Muhalli A Nijeriya – Ministan Muhalli

Sarakuna Na Da Rawar Takawa Wajen Kare Muhalli A Nijeriya – Ministan Muhalli

December 21, 2025
Me Ya Sa Ake Fifita Ilimin Boko A Kan Na Addini?

Me Ya Sa Ake Fifita Ilimin Boko A Kan Na Addini?

December 21, 2025
Yadda Itacen Dorawa Ke Warkar Da Cututtuka Daban-daban

Yadda Itacen Dorawa Ke Warkar Da Cututtuka Daban-daban

December 21, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.