ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Thursday, June 25, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

‘Yar Uwar Buhari Ta Bayar Da Kyautar Adaidaita Sahu Da Mashin Kan Nasarar Abba Gida-Gida A Kotu

by El-Zaharadeen Umar
2 years ago
Abba Gida-Gida

Sakamakon nasarar gwamnan jihar Kano Abba Gida-Gida wanda kotun kolin Nijeriya ta bayyana cewa shi ne halastaccen gwamna, Hajiya Ruƙayya Ahmad Dikko, ‘Yar uwa ga tsohon shugaban kasa Buhari ta raba Keke NAPPED Da sabon mashin kyauta. 

Haka ya biyo bayan wani alƙawari da ta ɗaukarwa kanta na cewa idan Allah ya ba Abba Kabir Yusuf nasara a shari’ar da suke yi tsakanin sa da ɓangaren jam’iyyar APC zata cika wannan alƙawari.

  • Kotun Koli Ta Tabbatar Da Abba Kabir Yusuf A Matsayin Zababben Gwamnan Kano
  • Shari’ar Kano: Kanawa Na Farin Ciki Kan Nasarar Abba A Kotun Koli

Hajiya Ruƙayya Ahmad Dikko dai ta kasance ‘yar uwa ta jini ga tsohon shugaba Muhammad Buhari domin da mahaifiyar ta da Alhaji Mamman Daura uwa ɗaya uba ɗaya.

ADVERTISEMENT

Kamar yadda ta shaidawa wakilinmu cewa wata rana a Kano suna tare da ‘yan uwanta waɗanda su kuma ‘yan APC ne, wata mahawara ta ɓarke a tsakanin su, inda wasu ke cewa Abba Gida-Gida ba zai kai labari ba a wannan shari’a da ake gwabzawa da shi, ita kuma Hajiya Ruƙayya Ahmad Dikko tana da fatan cewa Abba ne zai yi nasara.

Bayan duk wannan cacar baki tsakanin ta da ‘yan uwanta cikin raha da wasa ta yi alƙawarin cewa idan Allah ya ba Abba Gida-Gida nasara zata bada kyautar mashin da Keke NAPPED wanda ta cika wannan alƙawari.

LABARAI MASU NASABA

EFCC Za Ta Gurfanar Da Shugaban Miyetti Allah Kan Zargin Almundahanar Dala Miliyan 2.53

Maroko Ta Zama Ƙasa Ta Farko Daga Afirka Da Ta Tsallaka Zuwa Zagaye Na 32 A Gasar Kofin Duniya

“Hankalina ya tashi matuƙa akan wannan shari’a, na so tafiya Abuja, amma Allah bai sa na samu tikiti ba, sai kawai na dawo Daura domin yin wasu hidimomina, ina Daura akan yanke wannan hukunci, inda Allah ya ba Abba Kabir Yusuf nasara.” Inji ta

A cewar Hajiya Ruƙayya Ahmad Dikko ƙaninta wanda ke bi mata shine ya fara kawo mata labarin hukuncin Kotun Kolin Nijeriya cewa an maida wa Abba Kabir Yusuf kuri’unsa da Kotun farko ta kwace masa, sai kuma ga hukunci na cewa shi ne dai ya yi nasara.

Ta ƙara da cewa nan take na yi Sujaddar godiya ga Allah, kuma bata tsaya ɓata lokaci ba sai wajen masu sayar da mashina a garin Daura, inda ta sayi mashin na hawa akan kuɗi Naira miliyan daya da dubu hamsin da kuma Keke NAPPED miliyan biyu da dubu dari biyu da hamsin, inda nan take ta shiga banki ta tura masu kuɗadan su

“A wajan masu sayar da mashinan na ce samo mani wanda zai baiwa Mashin ɗin, sai aka yi sa a da wani mutum marar karfi kuma masoyin Abba Gida-Gida ne, na bashi mashin nan take, ita kuma NAPPED ɗin daman akwai wata mata mai ‘ya ‘ya bakwai da mijinta ya rasu ya barta, sai nasa aka kirata, na bata wannan NAPPED ɗin ‘ inji Ruƙayya Ahmed

Hajiya Ruƙayya ya ce wannan kyauta ta girgiza wannan mata, wacce ba zato-ba-tsammani ta ga an miƙa mata makullan wannan Keke NAPPED domin ta ci gaba da riƙe marayunta, abin ya yi matuƙar girgiza ta so sai.

Daga ƙarshe dai Hajiya Ruƙayya Ahmad Dikko ta bayyana bayyana jin daɗin ta da wannan nasara ta Abba Gida-Gida tare da cewa yanzu haka akwai wasu alƙawaran akan dai gwamnan jihar Kano injiniya Abba Kabir Yusuf (Abba Gida-Gida).

Abba Gida-Gida
El-Zaharadeen Umar
+ postsBio
  • El-Zaharadeen Umar
    https://hausa.leadership.ng/author/el-zaharadeen-umar/
    Mutum 1,000 Daga Jam’iyyar ADC Sun Koma PDP A Jihar Katsina
  • El-Zaharadeen Umar
    https://hausa.leadership.ng/author/el-zaharadeen-umar/
    Tinubu Ya Amince Da Ɗaukar Ma’aikatan Gandun Daji 1,000 Domin Matsalolin Tsaro A Katsina
  • El-Zaharadeen Umar
    https://hausa.leadership.ng/author/el-zaharadeen-umar/
    Matsalar Tsaro:Yadda Sabbin Matakan Gwamnati Ke Shafar Walwalar Al’ummar Jihar Katsina
  • El-Zaharadeen Umar
    https://hausa.leadership.ng/author/el-zaharadeen-umar/
    Garkuwa Da Mutane Na Barazana Ga Dalibai Miliyan 1.9 Masu Jarrabawar WAEC A Sassan Nijeriya

MASU ALAKA

EFCC Za Ta Gurfanar Da Shugaban Miyetti Allah Kan Zargin Almundahanar Dala Miliyan 2.53
Manyan Labarai

EFCC Za Ta Gurfanar Da Shugaban Miyetti Allah Kan Zargin Almundahanar Dala Miliyan 2.53

June 25, 2026
Maroko Ta Zama Ƙasa Ta Farko Daga Afirka Da Ta Tsallaka Zuwa Zagaye Na 32 A Gasar Kofin Duniya
Labarai

Maroko Ta Zama Ƙasa Ta Farko Daga Afirka Da Ta Tsallaka Zuwa Zagaye Na 32 A Gasar Kofin Duniya

June 25, 2026
Zan Ware 10bn Don Inganta Ilimin Matasa Idan Na Ci Zabe – Atiku
Manyan Labarai

‘Yan Nijeriya Ba Sa Bukatar ‘Yan Jarida Su Faɗa Musu Suna Jin Yunwa’ — Atiku

June 25, 2026
Next Post
AFCON 2023: Ma Su Masaukin Baki Sun Doke Guinea Bissau Da Ci 2-0

AFCON 2023: Ma Su Masaukin Baki Sun Doke Guinea Bissau Da Ci 2-0

LABARAI MASU NASABA

EFCC Za Ta Gurfanar Da Shugaban Miyetti Allah Kan Zargin Almundahanar Dala Miliyan 2.53

EFCC Za Ta Gurfanar Da Shugaban Miyetti Allah Kan Zargin Almundahanar Dala Miliyan 2.53

June 25, 2026
Maroko Ta Zama Ƙasa Ta Farko Daga Afirka Da Ta Tsallaka Zuwa Zagaye Na 32 A Gasar Kofin Duniya

Maroko Ta Zama Ƙasa Ta Farko Daga Afirka Da Ta Tsallaka Zuwa Zagaye Na 32 A Gasar Kofin Duniya

June 25, 2026
Zan Ware 10bn Don Inganta Ilimin Matasa Idan Na Ci Zabe – Atiku

‘Yan Nijeriya Ba Sa Bukatar ‘Yan Jarida Su Faɗa Musu Suna Jin Yunwa’ — Atiku

June 25, 2026
Dokar Sin Ta Gurfanar Da Masu Rajin Ballewar Kabilun Kasar Da Ke Kasashen Waje Ta Dace

Dokar Sin Ta Gurfanar Da Masu Rajin Ballewar Kabilun Kasar Da Ke Kasashen Waje Ta Dace

June 24, 2026
’Yan Kasuwa Na Kasashen Waje Sun Yaba Wa Yanayin Kasuwanci Na Sin

’Yan Kasuwa Na Kasashen Waje Sun Yaba Wa Yanayin Kasuwanci Na Sin

June 24, 2026
Yadda Uba Sani Ya Farfaɗo Da Asibitin Da Aka Yi Watsi Da Shi Tsawon Shekaru 40 – Hakimin Makarfi

Yadda Uba Sani Ya Farfaɗo Da Asibitin Da Aka Yi Watsi Da Shi Tsawon Shekaru 40 – Hakimin Makarfi

June 24, 2026
Dandalin DAVOS Na Bana: Fage Ne Da “Kirkire-Kirkiren Sin” Ya Sadu Da “Kyakkyawan Fatan Afirka”

Dandalin DAVOS Na Bana: Fage Ne Da “Kirkire-Kirkiren Sin” Ya Sadu Da “Kyakkyawan Fatan Afirka”

June 24, 2026
Binciken CGTN: Amfanarwa A Aikace Shi Ne Nagartaccen Ma’aunin Tantance Ainihin Kimar Sabbin Fasahohi

Binciken CGTN: Amfanarwa A Aikace Shi Ne Nagartaccen Ma’aunin Tantance Ainihin Kimar Sabbin Fasahohi

June 24, 2026
Kasar Sin Na Kara Zama Babban Ginshikin Ci Gaban Tattalin Arzikin Duniya Na Gaba

Kasar Sin Na Kara Zama Babban Ginshikin Ci Gaban Tattalin Arzikin Duniya Na Gaba

June 24, 2026
Tsaro: Dasuki Ya Bukaci Tinubu Ya Gyara Alaka Da Nijar Domin Kare Iyakokin Arewa-Maso-Yamma

Tsaro: Dasuki Ya Bukaci Tinubu Ya Gyara Alaka Da Nijar Domin Kare Iyakokin Arewa-Maso-Yamma

June 24, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.