ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Thursday, June 4, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

‘Yar Uwar Buhari Ta Bayar Da Kyautar Adaidaita Sahu Da Mashin Kan Nasarar Abba Gida-Gida A Kotu

by El-Zaharadeen Umar
2 years ago
Abba Gida-Gida

Sakamakon nasarar gwamnan jihar Kano Abba Gida-Gida wanda kotun kolin Nijeriya ta bayyana cewa shi ne halastaccen gwamna, Hajiya Ruƙayya Ahmad Dikko, ‘Yar uwa ga tsohon shugaban kasa Buhari ta raba Keke NAPPED Da sabon mashin kyauta. 

Haka ya biyo bayan wani alƙawari da ta ɗaukarwa kanta na cewa idan Allah ya ba Abba Kabir Yusuf nasara a shari’ar da suke yi tsakanin sa da ɓangaren jam’iyyar APC zata cika wannan alƙawari.

  • Kotun Koli Ta Tabbatar Da Abba Kabir Yusuf A Matsayin Zababben Gwamnan Kano
  • Shari’ar Kano: Kanawa Na Farin Ciki Kan Nasarar Abba A Kotun Koli

Hajiya Ruƙayya Ahmad Dikko dai ta kasance ‘yar uwa ta jini ga tsohon shugaba Muhammad Buhari domin da mahaifiyar ta da Alhaji Mamman Daura uwa ɗaya uba ɗaya.

ADVERTISEMENT

Kamar yadda ta shaidawa wakilinmu cewa wata rana a Kano suna tare da ‘yan uwanta waɗanda su kuma ‘yan APC ne, wata mahawara ta ɓarke a tsakanin su, inda wasu ke cewa Abba Gida-Gida ba zai kai labari ba a wannan shari’a da ake gwabzawa da shi, ita kuma Hajiya Ruƙayya Ahmad Dikko tana da fatan cewa Abba ne zai yi nasara.

Bayan duk wannan cacar baki tsakanin ta da ‘yan uwanta cikin raha da wasa ta yi alƙawarin cewa idan Allah ya ba Abba Gida-Gida nasara zata bada kyautar mashin da Keke NAPPED wanda ta cika wannan alƙawari.

LABARAI MASU NASABA

Gwamna Sani Ya Kashe Sama Da Naira Biliyan Ɗaya Kan Tallafin Ɗalibai A Kaduna – Kwamishina

Fargabar Satar Mutane Ya Sa An Rufe Makarantu A Abuja Da Mararaba

“Hankalina ya tashi matuƙa akan wannan shari’a, na so tafiya Abuja, amma Allah bai sa na samu tikiti ba, sai kawai na dawo Daura domin yin wasu hidimomina, ina Daura akan yanke wannan hukunci, inda Allah ya ba Abba Kabir Yusuf nasara.” Inji ta

A cewar Hajiya Ruƙayya Ahmad Dikko ƙaninta wanda ke bi mata shine ya fara kawo mata labarin hukuncin Kotun Kolin Nijeriya cewa an maida wa Abba Kabir Yusuf kuri’unsa da Kotun farko ta kwace masa, sai kuma ga hukunci na cewa shi ne dai ya yi nasara.

Ta ƙara da cewa nan take na yi Sujaddar godiya ga Allah, kuma bata tsaya ɓata lokaci ba sai wajen masu sayar da mashina a garin Daura, inda ta sayi mashin na hawa akan kuɗi Naira miliyan daya da dubu hamsin da kuma Keke NAPPED miliyan biyu da dubu dari biyu da hamsin, inda nan take ta shiga banki ta tura masu kuɗadan su

“A wajan masu sayar da mashinan na ce samo mani wanda zai baiwa Mashin ɗin, sai aka yi sa a da wani mutum marar karfi kuma masoyin Abba Gida-Gida ne, na bashi mashin nan take, ita kuma NAPPED ɗin daman akwai wata mata mai ‘ya ‘ya bakwai da mijinta ya rasu ya barta, sai nasa aka kirata, na bata wannan NAPPED ɗin ‘ inji Ruƙayya Ahmed

Hajiya Ruƙayya ya ce wannan kyauta ta girgiza wannan mata, wacce ba zato-ba-tsammani ta ga an miƙa mata makullan wannan Keke NAPPED domin ta ci gaba da riƙe marayunta, abin ya yi matuƙar girgiza ta so sai.

Daga ƙarshe dai Hajiya Ruƙayya Ahmad Dikko ta bayyana bayyana jin daɗin ta da wannan nasara ta Abba Gida-Gida tare da cewa yanzu haka akwai wasu alƙawaran akan dai gwamnan jihar Kano injiniya Abba Kabir Yusuf (Abba Gida-Gida).

Abba Gida-Gida
El-Zaharadeen Umar
+ postsBio
  • El-Zaharadeen Umar
    https://hausa.leadership.ng/author/el-zaharadeen-umar/
    Batun Kammala Aikin Gina Gidaje 250 Na “Renewed Hope” Ya Bar Baya Da Kura A Jihar Katsina
  • El-Zaharadeen Umar
    https://hausa.leadership.ng/author/el-zaharadeen-umar/
    Yusuf Buhari Ya Halarci Zaɓen Fidda Gwani Na Sanatan Shiyyar Daura
  • El-Zaharadeen Umar
    https://hausa.leadership.ng/author/el-zaharadeen-umar/
    Mace Ta Doke Namiji A Zaɓen Fidda Gwani Na Majalisar Tarayya A Katsina
  • El-Zaharadeen Umar
    https://hausa.leadership.ng/author/el-zaharadeen-umar/
    Gayyato Jakadun Kasashen Waje 17 Ya Kara Wa Bukukuwan Sallah Armashi A Katsina

MASU ALAKA

Mun Kaɗu Matuƙa Kan Labarin Mutuwar ‘Yan Mauludi A Hanyar Saminaka – Gwamnan Kaduna
Labarai

Gwamna Sani Ya Kashe Sama Da Naira Biliyan Ɗaya Kan Tallafin Ɗalibai A Kaduna – Kwamishina

June 4, 2026
Fargabar Satar Mutane Ya Sa An Rufe Makarantu A Abuja Da Mararaba
Labaran Kasuwanci

Fargabar Satar Mutane Ya Sa An Rufe Makarantu A Abuja Da Mararaba

June 4, 2026
Arsenal Na Dab Da Ɗaukar Jeremy Monga Daga Leicester City
Wasanni

Arsenal Na Dab Da Ɗaukar Jeremy Monga Daga Leicester City

June 4, 2026
Next Post
AFCON 2023: Ma Su Masaukin Baki Sun Doke Guinea Bissau Da Ci 2-0

AFCON 2023: Ma Su Masaukin Baki Sun Doke Guinea Bissau Da Ci 2-0

LABARAI MASU NASABA

Mun Kaɗu Matuƙa Kan Labarin Mutuwar ‘Yan Mauludi A Hanyar Saminaka – Gwamnan Kaduna

Gwamna Sani Ya Kashe Sama Da Naira Biliyan Ɗaya Kan Tallafin Ɗalibai A Kaduna – Kwamishina

June 4, 2026
Sin Ta Ware Kudi Har Yuan Biliyan 99.9 Domin Tallafawa Kula Da Lafiyar Yara A 2026

Sin Ta Ware Kudi Har Yuan Biliyan 99.9 Domin Tallafawa Kula Da Lafiyar Yara A 2026

June 4, 2026
Tasirin Nasarar Da Kasar Sin Ta Cimma A Fannin Kakkabe Matsanancin Talauci

Tasirin Nasarar Da Kasar Sin Ta Cimma A Fannin Kakkabe Matsanancin Talauci

June 4, 2026
Sabbin Ra’ayoyin Ci Gaba: Manufofin Zamani Na Zamanantarwa

Sabbin Ra’ayoyin Ci Gaba: Manufofin Zamani Na Zamanantarwa

June 4, 2026
Fargabar Satar Mutane Ya Sa An Rufe Makarantu A Abuja Da Mararaba

Fargabar Satar Mutane Ya Sa An Rufe Makarantu A Abuja Da Mararaba

June 4, 2026
Ana Gudanar Da Taron Masana Ilmin Harkokin Kasar Sin Karo Na Uku

Ana Gudanar Da Taron Masana Ilmin Harkokin Kasar Sin Karo Na Uku

June 4, 2026
Sin: Ya Kamata Tarayyar Turai Ta Dubi Huldar Tattalin Arziki Da Ciniki Tsakaninta Da Sin Bisa Daidaito

Sin: Ya Kamata Tarayyar Turai Ta Dubi Huldar Tattalin Arziki Da Ciniki Tsakaninta Da Sin Bisa Daidaito

June 4, 2026
Arsenal Na Dab Da Ɗaukar Jeremy Monga Daga Leicester City

Arsenal Na Dab Da Ɗaukar Jeremy Monga Daga Leicester City

June 4, 2026
An Gudanar Da Taron “Tattaunawar Magadan Garuruwa Na Duniya Na 2026” A Birnin Beijing

An Gudanar Da Taron “Tattaunawar Magadan Garuruwa Na Duniya Na 2026” A Birnin Beijing

June 4, 2026
Atiku Ne Ya Fi Dacewa Da Tikitin Takara A ADC Amma Ya Kamata Ya Janye — Baba-Ahmed

2027: Kasancewa Ɗan Arewa Kaɗai Ba Zai Tabbatar Da Samun Ƙuri’u Ba – Baba-Ahmed

June 4, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.