ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Thursday, July 16, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

‘Yar Uwar Buhari Ta Bayar Da Kyautar Adaidaita Sahu Da Mashin Kan Nasarar Abba Gida-Gida A Kotu

by El-Zaharadeen Umar
3 years ago
Abba Gida-Gida

Sakamakon nasarar gwamnan jihar Kano Abba Gida-Gida wanda kotun kolin Nijeriya ta bayyana cewa shi ne halastaccen gwamna, Hajiya Ruƙayya Ahmad Dikko, ‘Yar uwa ga tsohon shugaban kasa Buhari ta raba Keke NAPPED Da sabon mashin kyauta. 

Haka ya biyo bayan wani alƙawari da ta ɗaukarwa kanta na cewa idan Allah ya ba Abba Kabir Yusuf nasara a shari’ar da suke yi tsakanin sa da ɓangaren jam’iyyar APC zata cika wannan alƙawari.

  • Kotun Koli Ta Tabbatar Da Abba Kabir Yusuf A Matsayin Zababben Gwamnan Kano
  • Shari’ar Kano: Kanawa Na Farin Ciki Kan Nasarar Abba A Kotun Koli

Hajiya Ruƙayya Ahmad Dikko dai ta kasance ‘yar uwa ta jini ga tsohon shugaba Muhammad Buhari domin da mahaifiyar ta da Alhaji Mamman Daura uwa ɗaya uba ɗaya.

ADVERTISEMENT

Kamar yadda ta shaidawa wakilinmu cewa wata rana a Kano suna tare da ‘yan uwanta waɗanda su kuma ‘yan APC ne, wata mahawara ta ɓarke a tsakanin su, inda wasu ke cewa Abba Gida-Gida ba zai kai labari ba a wannan shari’a da ake gwabzawa da shi, ita kuma Hajiya Ruƙayya Ahmad Dikko tana da fatan cewa Abba ne zai yi nasara.

Bayan duk wannan cacar baki tsakanin ta da ‘yan uwanta cikin raha da wasa ta yi alƙawarin cewa idan Allah ya ba Abba Gida-Gida nasara zata bada kyautar mashin da Keke NAPPED wanda ta cika wannan alƙawari.

LABARAI MASU NASABA

Saliba Zai Yi Jinyar Watanni 5 Bayan Raunin Da Ya Samu A Bayansa

Kotu Ta Yanke Wa Wani Hukuncin Ɗaurin Shekara 7 Kan Tallan Wiwi A Kafafen Sada Zumunta

“Hankalina ya tashi matuƙa akan wannan shari’a, na so tafiya Abuja, amma Allah bai sa na samu tikiti ba, sai kawai na dawo Daura domin yin wasu hidimomina, ina Daura akan yanke wannan hukunci, inda Allah ya ba Abba Kabir Yusuf nasara.” Inji ta

A cewar Hajiya Ruƙayya Ahmad Dikko ƙaninta wanda ke bi mata shine ya fara kawo mata labarin hukuncin Kotun Kolin Nijeriya cewa an maida wa Abba Kabir Yusuf kuri’unsa da Kotun farko ta kwace masa, sai kuma ga hukunci na cewa shi ne dai ya yi nasara.

Ta ƙara da cewa nan take na yi Sujaddar godiya ga Allah, kuma bata tsaya ɓata lokaci ba sai wajen masu sayar da mashina a garin Daura, inda ta sayi mashin na hawa akan kuɗi Naira miliyan daya da dubu hamsin da kuma Keke NAPPED miliyan biyu da dubu dari biyu da hamsin, inda nan take ta shiga banki ta tura masu kuɗadan su

“A wajan masu sayar da mashinan na ce samo mani wanda zai baiwa Mashin ɗin, sai aka yi sa a da wani mutum marar karfi kuma masoyin Abba Gida-Gida ne, na bashi mashin nan take, ita kuma NAPPED ɗin daman akwai wata mata mai ‘ya ‘ya bakwai da mijinta ya rasu ya barta, sai nasa aka kirata, na bata wannan NAPPED ɗin ‘ inji Ruƙayya Ahmed

Hajiya Ruƙayya ya ce wannan kyauta ta girgiza wannan mata, wacce ba zato-ba-tsammani ta ga an miƙa mata makullan wannan Keke NAPPED domin ta ci gaba da riƙe marayunta, abin ya yi matuƙar girgiza ta so sai.

Daga ƙarshe dai Hajiya Ruƙayya Ahmad Dikko ta bayyana bayyana jin daɗin ta da wannan nasara ta Abba Gida-Gida tare da cewa yanzu haka akwai wasu alƙawaran akan dai gwamnan jihar Kano injiniya Abba Kabir Yusuf (Abba Gida-Gida).

Abba Gida-Gida
El-Zaharadeen Umar
+ postsBio
  • El-Zaharadeen Umar
    https://hausa.leadership.ng/author/el-zaharadeen-umar/
    Yadda Gidauniyar Ɗahiru Mangal Ta Tallafa Wa Marasa Lafiya 30,000 A Katsina
  • El-Zaharadeen Umar
    https://hausa.leadership.ng/author/el-zaharadeen-umar/
    Ko Shirin Da Gwamnatin Jihar Katsina Ke Yi Wa Manoma Zai  Amfane Su A wannan Daminar?
  • El-Zaharadeen Umar
    https://hausa.leadership.ng/author/el-zaharadeen-umar/
    Mutum 1,000 Daga Jam’iyyar ADC Sun Koma PDP A Jihar Katsina
  • El-Zaharadeen Umar
    https://hausa.leadership.ng/author/el-zaharadeen-umar/
    Tinubu Ya Amince Da Ɗaukar Ma’aikatan Gandun Daji 1,000 Domin Matsalolin Tsaro A Katsina

MASU ALAKA

Saliba Zai Yi Jinyar Watanni 5 Bayan Raunin Da Ya Samu A Bayansa
Manyan Labarai

Saliba Zai Yi Jinyar Watanni 5 Bayan Raunin Da Ya Samu A Bayansa

July 16, 2026
Kotu Ta Yanke Wa Wani Hukuncin Ɗaurin Shekara 7 Kan Tallan Wiwi A Kafafen Sada Zumunta
Manyan Labarai

Kotu Ta Yanke Wa Wani Hukuncin Ɗaurin Shekara 7 Kan Tallan Wiwi A Kafafen Sada Zumunta

July 16, 2026
Tinubu Yana Zuba Kyawawan Ayyuka A Nijeriya – Ganduje
Manyan Labarai

Ganduje Ya Buƙaci A Yi Siyasar Aƙida Domin Inganta Dimokuraɗiyya A Nijeriya

July 16, 2026
Next Post
AFCON 2023: Ma Su Masaukin Baki Sun Doke Guinea Bissau Da Ci 2-0

AFCON 2023: Ma Su Masaukin Baki Sun Doke Guinea Bissau Da Ci 2-0

LABARAI MASU NASABA

Saliba Zai Yi Jinyar Watanni 5 Bayan Raunin Da Ya Samu A Bayansa

Saliba Zai Yi Jinyar Watanni 5 Bayan Raunin Da Ya Samu A Bayansa

July 16, 2026
Kotu Ta Yanke Wa Wani Hukuncin Ɗaurin Shekara 7 Kan Tallan Wiwi A Kafafen Sada Zumunta

Kotu Ta Yanke Wa Wani Hukuncin Ɗaurin Shekara 7 Kan Tallan Wiwi A Kafafen Sada Zumunta

July 16, 2026
Tinubu Yana Zuba Kyawawan Ayyuka A Nijeriya – Ganduje

Ganduje Ya Buƙaci A Yi Siyasar Aƙida Domin Inganta Dimokuraɗiyya A Nijeriya

July 16, 2026
Binciken CGTN: Amfanar Da Kowa Da Kowa Shi Ne Ainihin Alherin Da Fasahohin Kwaikwayon Tunanin Bil Adama Suka Kawo

Binciken CGTN: Amfanar Da Kowa Da Kowa Shi Ne Ainihin Alherin Da Fasahohin Kwaikwayon Tunanin Bil Adama Suka Kawo

July 15, 2026
Sin Ta Yi Kira Da A Kafa Tsarin Jagorantar Muhimman Ma’adinai Ga Sauyawa Zuwa Amfani Da Makamashi Mai Tsafta

Sin Ta Yi Kira Da A Kafa Tsarin Jagorantar Muhimman Ma’adinai Ga Sauyawa Zuwa Amfani Da Makamashi Mai Tsafta

July 15, 2026
Gwamna Dauda Lawal Zai Gabatar Da Jawabi A Taron Ƙasa Da Ƙasa Na Jami’ar FUE Zariya

Gwamna Dauda Lawal Zai Gabatar Da Jawabi A Taron Ƙasa Da Ƙasa Na Jami’ar FUE Zariya

July 15, 2026
Neman Raba-Gari Da Sauran Kasashe Zai Kawo Mummuann Tasiri Ga Bangarorin Da Abin Ya Shafa

Neman Raba-Gari Da Sauran Kasashe Zai Kawo Mummuann Tasiri Ga Bangarorin Da Abin Ya Shafa

July 15, 2026
Kevin Kelly: AI Na Iya Taimakawa Wajen Cimma Burin “Koyar Da Dalibai Da Kwazonsu”

Kevin Kelly: AI Na Iya Taimakawa Wajen Cimma Burin “Koyar Da Dalibai Da Kwazonsu”

July 15, 2026
Gwamna Yusuf Ya Bai Wa Masu Kula Da Akwatinan Zaɓe Na APC Filaye 1,540 Da Tallafin Miliyan 100

Gwamna Yusuf Ya Bai Wa Masu Kula Da Akwatinan Zaɓe Na APC Filaye 1,540 Da Tallafin Miliyan 100

July 15, 2026
Sabbin Ministoci

Rashin Tsaro: Majalisar Dattawa Ta Bukaci A Tura Ƙarin Sojoji da ’Yansanda Zuwa Benuwe

July 15, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.