ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Thursday, September 10, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Yara ’Yan Kwadago Da Ke Kasar Amurka Wadda Ke Ikirarin Kare Hakkin Dan Adam

by CMG Hausa
4 years ago
Amurka

A karkashin hasken rana mai zafin gaske, wani yaro dan shekaru 7 da haihuwa ya dukufa kan aikin gona.

Wa zai iya alakanta batun da kasar Amurka, wadda ta fi ci gaban tattalin arziki, kuma a kullum ke daukar kanta a matsayin misali wajen kare hakkin bil Adam? Sai dai wani hoton da kungiyar ’yan kwadagon gandayen noma na kasar Amurka ta fitar ta shafin sada zumunta a bara ya tabbatar da cewa, hakan na faruwa dai a wannan kasa.

  • Japan Ba Ta Boye Yunkurinta Na Yin Fito-na-fito Da Kasar Sin Ba

Tuni yau shekaru sama da 100 da suka wuce, aka fara daukar yara ’yan kwadago aiki a mahakar kwal da gandayen noman ganyen tabar sigari da masaku na kasar. Abin bakin ciki shi ne, duk da ci gaban da ’yan Adam suka samu ta fannin wayewar kai cikin shekarun 100 da suka wuce, har yanzu ana yawan samun yara ’yan kwadago a kasar Amurka.

ADVERTISEMENT

Musamman a fannin aikin noma, yara ’yan kwadago na kasar ta Amurka sun haifar da damuwa idan aka yi la’akari da yanayin da suke ciki. Bisa kididdigar da kungiyar shirin horar da ’yan kwadagon gandayen noma ta kasar Amurka ta yi, an ce, yanzu haka akwai yara ’yan kwadago kimanin dubu 500 a kasar, kuma da yawa daga cikinsu sun fara aiki tun lokacin da suke da shekaru 8 da haihuwa, kuma suna aiki na tsawon sa’o’i 72 a kowane sati.

Har wa yau, yaran sun dade suna aiki a muhallin dake da sinadarai masu guba. Lamarin da ya sa suke yawan kamuwa da cutar sankara. Ban da haka, sabo da yadda suke aiki da na’urorin noma masu nauyi da kuma kaifi, ba tare da samun horon kariya da suka kamata ba, ya sa su kan fuskanci hadari a lokacin aiki.

LABARAI MASU NASABA

Sin Na Fatan Amurka Za Ta Dakatar Da Furta Karairayi Da Nufin Bata Mata Suna

Sin Ba Ta Taba Janyewa Wata Kasa Tsani Ba

Rahoton da jaridar “Washington Post” ta samar ya yi nuni da cewa, daga shekarar 2003 zuwa ta 2016, akwai yara ’yan kwadago 452 da suka mutu a kasar, kuma sama da rabinsu suna aiki ne a gandayen noma.

A bara, masana’antu da dama da ke jihar Wisconsin ta arewacin kasar Amurka sun fuskanci matsalar karancin ’yan kwadago. Don taimaka musu daidaita matsalar, majalisar dokokin jihar ta mai da hankalinta kan yara, inda a watan Oktoban bara, majalisar dattawa ta jihar ta zartas da shirin dokar tsawaita lokacin aiki na ’yan kwadago da ba su balaga ba.

A hakika, bisa yarjejeniyar hakkin yara ta MDD, dole ne a kare hakkin yara, amma sakamakon yadda kasar Amurka ta ki amincewa da yarjejeniyar, inda ta zama kasa daya tilo a duniya da ba ta amince da ita ba, ya sa yaran kasar ba su iya samun kariya daga yarjejeniyar.

A watan Yunin shekarar 2002, a yayin babban taron kwadago na kasa da kasa karo na 90 an tabbatar da ranar 12 ga watan Yunin kowace shekara a matsayin “ranar hana yara kwadago ta duniya”, don yin kira ga kasa da kasa da su mai da hankali a kan batun yara ’yan kwadago.

Amma yaushe ne za a kai ga mayar da yarantar da ta kamata ga yaran kasar a matsayin “misalin kare hakkin dan Adam?” (Lubabatu Lei)

Amurka
CMG Hausa
+ postsBio
  • CMG Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cmg-hausa/
    Shugabannin Kasashen Duniya Sun Yi Wa Sin Fatan Alheri A Sabuwar Shekara
  • CMG Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cmg-hausa/
    San Francisco sabon mafarin hadin gwiwar Sin da Amurka ne
  • CMG Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cmg-hausa/
    Xi Ya Halarci Kwaya-Kwaryan Taron Shugabannin Mambobin APEC
  • CMG Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cmg-hausa/
    Shugaban Kasar Sin Ya Gabatar Da Rubutaccen Jawabi Ga Taron Jagororin Masana’antu Da Kasuwanci Na APEC

MASU ALAKA

Sin Na Fatan Amurka Za Ta Dakatar Da Furta Karairayi Da Nufin Bata Mata Suna
Daga Birnin Sin

Sin Na Fatan Amurka Za Ta Dakatar Da Furta Karairayi Da Nufin Bata Mata Suna

September 9, 2026
Sin Ba Ta Taba Janyewa Wata Kasa Tsani Ba
Daga Birnin Sin

Sin Ba Ta Taba Janyewa Wata Kasa Tsani Ba

September 9, 2026
Xi Ya Aike Da Gaisuwa Albarkacin Ranar Malamai Yana Mai Kira Da A Samar Da Matasa Masu Hazaka Domin Kara Farfado Da Kasa
Daga Birnin Sin

Xi Ya Aike Da Gaisuwa Albarkacin Ranar Malamai Yana Mai Kira Da A Samar Da Matasa Masu Hazaka Domin Kara Farfado Da Kasa

September 9, 2026
Next Post
Amurka Ba Za Ta Cimma Burinta Ba A Taron Koli Na Kasashen Nahiyar Amurka Mai Cike Da Nuna Bambanci

Amurka Ba Za Ta Cimma Burinta Ba A Taron Koli Na Kasashen Nahiyar Amurka Mai Cike Da Nuna Bambanci

LABARAI MASU NASABA

’Yansanda Sun Kama Wadda Ta Yaɗa Labarin OPay Zai Daina Aiki A Nijeriya

’Yansanda Sun Kama Wadda Ta Yaɗa Labarin OPay Zai Daina Aiki A Nijeriya

September 10, 2026
2027: ’Yansanda Sun Gargaɗi Jam’iyyun Siyasa Kan Haifar Da Rikici A Sakkwato

2027: ’Yansanda Sun Gargaɗi Jam’iyyun Siyasa Kan Haifar Da Rikici A Sakkwato

September 10, 2026
Zabe: Gwamnatin Kano Ta Taƙaita Zirga-zirgar Mutane Da Ababen Hawa

Gwamna Yusuf Ya Umarci Jami’an Tsaro Su Gano Waɗanda Suka Kashe Danshagamu

September 10, 2026
Sin Na Fatan Amurka Za Ta Dakatar Da Furta Karairayi Da Nufin Bata Mata Suna

Sin Na Fatan Amurka Za Ta Dakatar Da Furta Karairayi Da Nufin Bata Mata Suna

September 9, 2026
An Kashe Shahararren Mai Sharhin Siyasar Kano, Ibrahim Dan Shagamu

An Kashe Shahararren Mai Sharhin Siyasar Kano, Ibrahim Dan Shagamu

September 9, 2026
Sin Ba Ta Taba Janyewa Wata Kasa Tsani Ba

Sin Ba Ta Taba Janyewa Wata Kasa Tsani Ba

September 9, 2026
Xi Ya Aike Da Gaisuwa Albarkacin Ranar Malamai Yana Mai Kira Da A Samar Da Matasa Masu Hazaka Domin Kara Farfado Da Kasa

Xi Ya Aike Da Gaisuwa Albarkacin Ranar Malamai Yana Mai Kira Da A Samar Da Matasa Masu Hazaka Domin Kara Farfado Da Kasa

September 9, 2026
Ku Daure Ku Sake Zaɓar Mijina A 2027 – Remi Tinubu

Ku Daure Ku Sake Zaɓar Mijina A 2027 – Remi Tinubu

September 9, 2026
Renon Matasa A Kan Kyakkyawar Turba Ginshiki Ne Na Gina KasaBy

Renon Matasa A Kan Kyakkyawar Turba Ginshiki Ne Na Gina KasaBy

September 9, 2026
Bikin CIFTIS Zai Ingiza Bude Kofa A Kasar Sin

Bikin CIFTIS Zai Ingiza Bude Kofa A Kasar Sin

September 9, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.