ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Wednesday, September 9, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Yunkurin Kasar Amurka Na “Neman Cin Nasara” Ya Sa Sauran Kasashe Yin Watsi Da Ita

by CGTN Hausa and Sulaiman
6 months ago
Amurka

A wani jawabin da ya yi ga majalissun dokokin kasar Amurka a kwanan baya, shugaba Donald Trump ya ce kasarsa na ta samun nasarori a duniya. Sai dai yunkurin kasar na “neman cin nasara” ya kan sanya mutanen duniya damuwa, da daukar matakai na yin watsi da kasar.

Misali, jaridar Business Day ta kasar Najeriya ta wallafa wata makala a shafinta na Intanet a kwanakin baya, wadda ta bayyana cewa, canzawar manufar harajin kwastam ta kasar Amurka ta sa ’yan kasuwar Najeriya damuwa, lamarin da ya sanya raguwar darajar kayayyakin da aka fitar da su daga Najeriya zuwa Amurka a shekarar 2025 da kimanin kaso 14%, bisa jimillar shekarar 2024. Baya ga haka, darajar kayayyakin da aka fitar da su daga Najeriya zuwa kasar Sin ta karu da kimanin 81% a cikin shekaru 3 da suka wuce. Kana ana sa ran ganin wani yanayi na gagauta karkata ga kasuwannin kasar Sin a cinikin da ’yan kasuwar Najeriya suke yi, bisa la’akari da manufar Sin ta yafe wa kasashe 53 dake nahiyar Afirka harajin kwastam, wadda za ta fara aiki a watan Mayun dake tafe.

A fannin hada-hadar kudi ma ana iya ganin yanayi na “karkata ga kasar Sin”. Misali, kamfanin dillancin labarai na Bloomberg na kasar Amurka ya ruwaito Jeremy Awori, shugaban kamfanin Ecobank, na cewar manufar harajin kwastam ta kasar Amurka dake canzawa a kai a kai ta haifar da mummunan tasiri kan kamfanonin kasashen Afirka, saboda haka bangaren Afirka na kokarin rage dogaro kan dalar Amurka, maimakonta ana karkata ga kudin Sin RMB da kudaden kasashen Afirka wajen gudanar da ciniki.

ADVERTISEMENT

Dalilin da ya sa ake samun wannan karkacewa shi ne, domin yadda aka gano bambanci. Misali, a kwanan nan, cibiyar nazarin tsare-tsaren duniya ta HORN ta kasar Kenya ta wallafa wani bayani a shafinta na Intanet, wanda ya kwatanta manufar kasar Sin ta yafewa kasashen Afirka harajin kwastam, da dokar samar da karuwar tattalin arziki da damammaki a Afirka (AGOA) ta kasar Amurka. Inda aka ce, bisa ka’idar AGOA, gwamnatin kasar Amurka za ta tantance damar kasashen Afirka na samun gatanci a kowace shekara, lamarin da ya haifar da yanayin rashin tabbas. Yayin da a nata bangare, manufar kasar Sin na da dorewa, kana ta kunshi ra’ayi kaucewa tsoma baki cikin harkokin gidan sauran kasashe, saboda haka za ta ba kamfanonin kasashe daban daban damar zuba jari hankalinsu a kwance, ta yadda za ta haifar da gudunmowa ga yunkurin nahiyar Afirka na neman ci gaban tattalin arziki mai dorewa.

To, ko da gangan kasar Sin ta yi wani abu don tabbatar da wannan yanayi na karkacewa? A’a. Kasar Sin ba ta yi komai ba, illa kokarin raya tattalin arzikinta, da ci gaba da zame wa kasashe daban daban abokiyar hulda da za su iya dogaro da ita, da neman samun nasarori tare da su. Hakika babbar manufar kasar ba ta taba canzawa ba. Ta haka, Sin tana kokarin samar da yanayi mai tabbaci ga duniya.

LABARAI MASU NASABA

Taswirar Duniya Mai Adalci: Afirka Ta Ki A Sake “Rage” Girmanta

Duk Runtsi, Akwai Mai Ba Da Kulawa Ta Musamman A Kasar Sin

A nata bangare, kasar Amurka tana karbar karin harajin kwastam, duk da cewa ana takaddama a cikin gida kan wannan batu. Tana kuma neman wai “karfafa hadin gwiwa da kasashen Afirka”, yayin da take matsa musu lamba ta fakewa da batutuwan hakkin dan Adam, da addini. Kana duk da cewa tana takama wai tana “kiyaye zaman lafiya a duniya”, hakika tana kaddamar da yake-yake a duniya a kai a kai, ciki har da hare-haren da ita da Isra’ila suke kai wa kasar Iran a halin yanzu. Ko da yake tana haifar da tarin matsaloli a duniya, duk da haka kasar Amurka na tsammanin cewa tana samun nasarori. Ke nan tana neman “samun nasarori” ne bisa tushen haddasa damuwa, da hasara, da wahalhalu, da zubar da jinin mutanen sauran kasashe.

Ban san irin sakamakon da kasar Amurka za ta samu a karshe ba, amma na san tabbas sauran kasashe za su yi watsi da ita, don gujewa mummunan tasirin da take haifar wa duniya. (Bello Wang)

 

Amurka
CGTN Hausa
+ posts Bio
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    Batun AI Zai Fi Daukar Hankali A Bikin Baje Kolin Fasahar Zamani Ta Duniya Karo Na 5
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    Cinikin Wajen Sin Ya Ci Gaba Da Samun Bunkasa Cikin Sauri A Watanni Takwas Na Farkon Bana
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    Binciken CGTN Ya Nuna Gamsuwa Da Yadda Baje Kolin CIFTIS Ke Shaida Karfin Gwiwar Sin A Fannin Kara Fadada Bude Kofa Bisa Babban Matsayi
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    Sin Za Ta Yi Aiki Tare Da Sassa Daban Daban Domin Mayar Da Fasahar AI Wata Dama Ta Cin Gajiya Mai Dorewa
Amurka
Sulaiman
+ posts Bio
  • Sulaiman
    Batun AI Zai Fi Daukar Hankali A Bikin Baje Kolin Fasahar Zamani Ta Duniya Karo Na 5
  • Sulaiman
    Cinikin Wajen Sin Ya Ci Gaba Da Samun Bunkasa Cikin Sauri A Watanni Takwas Na Farkon Bana
  • Sulaiman
    ‘Yan Bindiga Sun Kashe 2, Sun Yi Garkuwa Da 26 A Kaduna
  • Sulaiman
    Binciken CGTN Ya Nuna Gamsuwa Da Yadda Baje Kolin CIFTIS Ke Shaida Karfin Gwiwar Sin A Fannin Kara Fadada Bude Kofa Bisa Babban Matsayi

MASU ALAKA

Taswirar Duniya Mai Adalci: Afirka Ta Ki A Sake “Rage” Girmanta
Ra'ayi Riga

Taswirar Duniya Mai Adalci: Afirka Ta Ki A Sake “Rage” Girmanta

September 8, 2026
Duk Runtsi, Akwai Mai Ba Da Kulawa Ta Musamman A Kasar Sin
Ra'ayi Riga

Duk Runtsi, Akwai Mai Ba Da Kulawa Ta Musamman A Kasar Sin

September 4, 2026
Samun Rarar Kudin Ciniki Ba “Laifi” Ba Ne, Hadin Gwiwa Da Cin Moriya Tare Ita Ce Mafita Ga Kowa
Ra'ayi Riga

Samun Rarar Kudin Ciniki Ba “Laifi” Ba Ne, Hadin Gwiwa Da Cin Moriya Tare Ita Ce Mafita Ga Kowa

September 2, 2026
Next Post
Ramadan: Lokutan Buda-Baki Da Sahur Na Azumi Na 2

Ramadan: Lokutan Buda-Baki Da Sahur Na Azumi Na 13

LABARAI MASU NASABA

Batun AI Zai Fi Daukar Hankali A Bikin Baje Kolin Fasahar Zamani Ta Duniya Karo Na 5

Batun AI Zai Fi Daukar Hankali A Bikin Baje Kolin Fasahar Zamani Ta Duniya Karo Na 5

September 8, 2026
Gwamna Radda Ya Samu Goyon Bayan APC A Katsina Gabanin Zaɓen 2027

Gwamna Radda Ya Samu Goyon Bayan APC A Katsina Gabanin Zaɓen 2027

September 8, 2026
Cinikin Wajen Sin Ya Ci Gaba Da Samun Bunkasa Cikin Sauri A Watanni Takwas Na Farkon Bana

Cinikin Wajen Sin Ya Ci Gaba Da Samun Bunkasa Cikin Sauri A Watanni Takwas Na Farkon Bana

September 8, 2026
'Yan Bindiga

‘Yan Bindiga Sun Kashe 2, Sun Yi Garkuwa Da 26 A Kaduna

September 8, 2026
Binciken CGTN Ya Nuna Gamsuwa Da Yadda Baje Kolin CIFTIS Ke Shaida Karfin Gwiwar Sin A Fannin Kara Fadada Bude Kofa Bisa Babban Matsayi

Binciken CGTN Ya Nuna Gamsuwa Da Yadda Baje Kolin CIFTIS Ke Shaida Karfin Gwiwar Sin A Fannin Kara Fadada Bude Kofa Bisa Babban Matsayi

September 8, 2026
Yadda Taron Tattalin Arziki Da Zuba Jari Na Kwana Biyu Ya Gudana A Katsina

Gwamna Radda Ya Gabatar Da Kasafin N828.6bn Na 2027

September 8, 2026
Sin Za Ta Yi Aiki Tare Da Sassa Daban Daban Domin Mayar Da Fasahar AI Wata Dama Ta Cin Gajiya Mai Dorewa

Sin Za Ta Yi Aiki Tare Da Sassa Daban Daban Domin Mayar Da Fasahar AI Wata Dama Ta Cin Gajiya Mai Dorewa

September 8, 2026
Gwamnan Kebbi Ya Bayyana Shirin Sake Duba Albashin Malaman Firamare

Gwamna Idris Ya Rushe Majalisar Shugabannin Hukumar Zaɓe Ta Kebbi

September 8, 2026
Han Zheng Ya Halarci Baje Kolin CIFIT Karo Na 26 Tare Da Gabatar Da Jawabi

Han Zheng Ya Halarci Baje Kolin CIFIT Karo Na 26 Tare Da Gabatar Da Jawabi

September 8, 2026
Wani Soja Ya Kashe Kansa Bayan Kashe Matarsa A Jihar Neja

Kano Za Ta Kafa Sansanonin Sojoji A Ƙananan Hukumomin Da Ke Fuskantar Barazanar Tsaro

September 8, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.