ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Sunday, July 5, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Yunkurin Kasar Amurka Na “Neman Cin Nasara” Ya Sa Sauran Kasashe Yin Watsi Da Ita

by CGTN Hausa and Sulaiman
4 months ago
Amurka

A wani jawabin da ya yi ga majalissun dokokin kasar Amurka a kwanan baya, shugaba Donald Trump ya ce kasarsa na ta samun nasarori a duniya. Sai dai yunkurin kasar na “neman cin nasara” ya kan sanya mutanen duniya damuwa, da daukar matakai na yin watsi da kasar.

Misali, jaridar Business Day ta kasar Najeriya ta wallafa wata makala a shafinta na Intanet a kwanakin baya, wadda ta bayyana cewa, canzawar manufar harajin kwastam ta kasar Amurka ta sa ’yan kasuwar Najeriya damuwa, lamarin da ya sanya raguwar darajar kayayyakin da aka fitar da su daga Najeriya zuwa Amurka a shekarar 2025 da kimanin kaso 14%, bisa jimillar shekarar 2024. Baya ga haka, darajar kayayyakin da aka fitar da su daga Najeriya zuwa kasar Sin ta karu da kimanin 81% a cikin shekaru 3 da suka wuce. Kana ana sa ran ganin wani yanayi na gagauta karkata ga kasuwannin kasar Sin a cinikin da ’yan kasuwar Najeriya suke yi, bisa la’akari da manufar Sin ta yafe wa kasashe 53 dake nahiyar Afirka harajin kwastam, wadda za ta fara aiki a watan Mayun dake tafe.

A fannin hada-hadar kudi ma ana iya ganin yanayi na “karkata ga kasar Sin”. Misali, kamfanin dillancin labarai na Bloomberg na kasar Amurka ya ruwaito Jeremy Awori, shugaban kamfanin Ecobank, na cewar manufar harajin kwastam ta kasar Amurka dake canzawa a kai a kai ta haifar da mummunan tasiri kan kamfanonin kasashen Afirka, saboda haka bangaren Afirka na kokarin rage dogaro kan dalar Amurka, maimakonta ana karkata ga kudin Sin RMB da kudaden kasashen Afirka wajen gudanar da ciniki.

ADVERTISEMENT

Dalilin da ya sa ake samun wannan karkacewa shi ne, domin yadda aka gano bambanci. Misali, a kwanan nan, cibiyar nazarin tsare-tsaren duniya ta HORN ta kasar Kenya ta wallafa wani bayani a shafinta na Intanet, wanda ya kwatanta manufar kasar Sin ta yafewa kasashen Afirka harajin kwastam, da dokar samar da karuwar tattalin arziki da damammaki a Afirka (AGOA) ta kasar Amurka. Inda aka ce, bisa ka’idar AGOA, gwamnatin kasar Amurka za ta tantance damar kasashen Afirka na samun gatanci a kowace shekara, lamarin da ya haifar da yanayin rashin tabbas. Yayin da a nata bangare, manufar kasar Sin na da dorewa, kana ta kunshi ra’ayi kaucewa tsoma baki cikin harkokin gidan sauran kasashe, saboda haka za ta ba kamfanonin kasashe daban daban damar zuba jari hankalinsu a kwance, ta yadda za ta haifar da gudunmowa ga yunkurin nahiyar Afirka na neman ci gaban tattalin arziki mai dorewa.

To, ko da gangan kasar Sin ta yi wani abu don tabbatar da wannan yanayi na karkacewa? A’a. Kasar Sin ba ta yi komai ba, illa kokarin raya tattalin arzikinta, da ci gaba da zame wa kasashe daban daban abokiyar hulda da za su iya dogaro da ita, da neman samun nasarori tare da su. Hakika babbar manufar kasar ba ta taba canzawa ba. Ta haka, Sin tana kokarin samar da yanayi mai tabbaci ga duniya.

LABARAI MASU NASABA

Ga “Itacen Kuka” Na Kasar Sin

Shekaru 105 Na Jam’iyyar Kwaminis Ta Kasar Sin: Darussa Ga Kasashe Masu Tasowa Daga Kwarewar Ci Gaban Kasar Sin

A nata bangare, kasar Amurka tana karbar karin harajin kwastam, duk da cewa ana takaddama a cikin gida kan wannan batu. Tana kuma neman wai “karfafa hadin gwiwa da kasashen Afirka”, yayin da take matsa musu lamba ta fakewa da batutuwan hakkin dan Adam, da addini. Kana duk da cewa tana takama wai tana “kiyaye zaman lafiya a duniya”, hakika tana kaddamar da yake-yake a duniya a kai a kai, ciki har da hare-haren da ita da Isra’ila suke kai wa kasar Iran a halin yanzu. Ko da yake tana haifar da tarin matsaloli a duniya, duk da haka kasar Amurka na tsammanin cewa tana samun nasarori. Ke nan tana neman “samun nasarori” ne bisa tushen haddasa damuwa, da hasara, da wahalhalu, da zubar da jinin mutanen sauran kasashe.

Ban san irin sakamakon da kasar Amurka za ta samu a karshe ba, amma na san tabbas sauran kasashe za su yi watsi da ita, don gujewa mummunan tasirin da take haifar wa duniya. (Bello Wang)

 

Amurka
CGTN Hausa
+ posts Bio
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    Dakarun Tsaron Teku Na Sin Na Ci Gaba Da Sintirin Wanzar Da Doka A Yankunan Ruwa Na Gabashin Tsibirin Taiwan
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    Wasu Matasa Amurkawa Sun Ziyarci Sin Don Kara Fahimtar Kasar
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    Wakilin CMG Ya Zanta Da Mataimakin Shugaban Kasar Afirka Ta Kudu
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    Tawaga Ta Biyu Ta Kwararrun Kasar Sin Ta Sauka A Jamhuriyar Dimokaradiyyar Congo Domin Karfafa Yaki Da Cutar Ebola
Amurka
Sulaiman
+ posts Bio
  • Sulaiman
    Dakarun Tsaron Teku Na Sin Na Ci Gaba Da Sintirin Wanzar Da Doka A Yankunan Ruwa Na Gabashin Tsibirin Taiwan
  • Sulaiman
    Wasu Matasa Amurkawa Sun Ziyarci Sin Don Kara Fahimtar Kasar
  • Sulaiman
    Wakilin CMG Ya Zanta Da Mataimakin Shugaban Kasar Afirka Ta Kudu
  • Sulaiman
    Gwamnatin Zamfara Ta Jinjina Wa Shugaban NAHCON Kan Nasarar Aikin Hajjin 2026

MASU ALAKA

Ga “Itacen Kuka” Na Kasar Sin
Ra'ayi Riga

Ga “Itacen Kuka” Na Kasar Sin

July 1, 2026
Shekaru 105 Na Jam’iyyar Kwaminis Ta Kasar Sin: Darussa Ga Kasashe Masu Tasowa Daga Kwarewar Ci Gaban Kasar Sin
Ra'ayi Riga

Shekaru 105 Na Jam’iyyar Kwaminis Ta Kasar Sin: Darussa Ga Kasashe Masu Tasowa Daga Kwarewar Ci Gaban Kasar Sin

June 30, 2026
Dandalin DAVOS Na Bana: Fage Ne Da “Kirkire-Kirkiren Sin” Ya Sadu Da “Kyakkyawan Fatan Afirka”
Ra'ayi Riga

Dandalin DAVOS Na Bana: Fage Ne Da “Kirkire-Kirkiren Sin” Ya Sadu Da “Kyakkyawan Fatan Afirka”

June 24, 2026
Next Post
Ramadan: Lokutan Buda-Baki Da Sahur Na Azumi Na 2

Ramadan: Lokutan Buda-Baki Da Sahur Na Azumi Na 13

LABARAI MASU NASABA

Dakarun Tsaron Teku Na Sin Na Ci Gaba Da Sintirin Wanzar Da Doka A Yankunan Ruwa Na Gabashin Tsibirin Taiwan

Dakarun Tsaron Teku Na Sin Na Ci Gaba Da Sintirin Wanzar Da Doka A Yankunan Ruwa Na Gabashin Tsibirin Taiwan

July 4, 2026
Wasu Matasa Amurkawa Sun Ziyarci Sin Don Kara Fahimtar Kasar

Wasu Matasa Amurkawa Sun Ziyarci Sin Don Kara Fahimtar Kasar

July 4, 2026
Wakilin CMG Ya Zanta Da Mataimakin Shugaban Kasar Afirka Ta Kudu

Wakilin CMG Ya Zanta Da Mataimakin Shugaban Kasar Afirka Ta Kudu

July 4, 2026
CAF Ta Gayyaci Ƙasashen Afirka Su Nemi Ɗaukar Nauyin Gasar AFCON Ta 2028, 2032 da 2036

CAF Ta Gayyaci Ƙasashen Afirka Su Nemi Ɗaukar Nauyin Gasar AFCON Ta 2028, 2032 da 2036

July 4, 2026
Gwamnatin Zamfara Ta Jinjina Wa Shugaban NAHCON Kan Nasarar Aikin Hajjin 2026

Gwamnatin Zamfara Ta Jinjina Wa Shugaban NAHCON Kan Nasarar Aikin Hajjin 2026

July 4, 2026
Tawaga Ta Biyu Ta Kwararrun Kasar Sin Ta Sauka A Jamhuriyar Dimokaradiyyar Congo Domin Karfafa Yaki Da Cutar Ebola

Tawaga Ta Biyu Ta Kwararrun Kasar Sin Ta Sauka A Jamhuriyar Dimokaradiyyar Congo Domin Karfafa Yaki Da Cutar Ebola

July 4, 2026
Yadda Gidauniyar Ɗahiru Mangal Ta Tallafa Wa Marasa Lafiya 30,000 A Katsina

Yadda Gidauniyar Ɗahiru Mangal Ta Tallafa Wa Marasa Lafiya 30,000 A Katsina

July 4, 2026
Babban Dan Majalissar Dokokin Kasar Sin Ya Halarci Jana’izar Marigayi Jagoran Addini Na Iran

Babban Dan Majalissar Dokokin Kasar Sin Ya Halarci Jana’izar Marigayi Jagoran Addini Na Iran

July 4, 2026
Akwai Barazanar Ƙaruwar Yunwa A Arewacin Nijeriya – Peter Obi

Akwai Barazanar Ƙaruwar Yunwa A Arewacin Nijeriya – Peter Obi

July 4, 2026
Pakistan Ta Kashe Mutum 36 A Hare-haren Da Ta Kai Kan Iyakarta Da Afghanistan

Pakistan Ta Kashe Mutum 36 A Hare-haren Da Ta Kai Kan Iyakarta Da Afghanistan

July 4, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.