ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Sunday, June 14, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Yunkurin Kasar Amurka Na “Neman Cin Nasara” Ya Sa Sauran Kasashe Yin Watsi Da Ita

by CGTN Hausa and Sulaiman
3 months ago
Amurka

A wani jawabin da ya yi ga majalissun dokokin kasar Amurka a kwanan baya, shugaba Donald Trump ya ce kasarsa na ta samun nasarori a duniya. Sai dai yunkurin kasar na “neman cin nasara” ya kan sanya mutanen duniya damuwa, da daukar matakai na yin watsi da kasar.

Misali, jaridar Business Day ta kasar Najeriya ta wallafa wata makala a shafinta na Intanet a kwanakin baya, wadda ta bayyana cewa, canzawar manufar harajin kwastam ta kasar Amurka ta sa ’yan kasuwar Najeriya damuwa, lamarin da ya sanya raguwar darajar kayayyakin da aka fitar da su daga Najeriya zuwa Amurka a shekarar 2025 da kimanin kaso 14%, bisa jimillar shekarar 2024. Baya ga haka, darajar kayayyakin da aka fitar da su daga Najeriya zuwa kasar Sin ta karu da kimanin 81% a cikin shekaru 3 da suka wuce. Kana ana sa ran ganin wani yanayi na gagauta karkata ga kasuwannin kasar Sin a cinikin da ’yan kasuwar Najeriya suke yi, bisa la’akari da manufar Sin ta yafe wa kasashe 53 dake nahiyar Afirka harajin kwastam, wadda za ta fara aiki a watan Mayun dake tafe.

A fannin hada-hadar kudi ma ana iya ganin yanayi na “karkata ga kasar Sin”. Misali, kamfanin dillancin labarai na Bloomberg na kasar Amurka ya ruwaito Jeremy Awori, shugaban kamfanin Ecobank, na cewar manufar harajin kwastam ta kasar Amurka dake canzawa a kai a kai ta haifar da mummunan tasiri kan kamfanonin kasashen Afirka, saboda haka bangaren Afirka na kokarin rage dogaro kan dalar Amurka, maimakonta ana karkata ga kudin Sin RMB da kudaden kasashen Afirka wajen gudanar da ciniki.

ADVERTISEMENT

Dalilin da ya sa ake samun wannan karkacewa shi ne, domin yadda aka gano bambanci. Misali, a kwanan nan, cibiyar nazarin tsare-tsaren duniya ta HORN ta kasar Kenya ta wallafa wani bayani a shafinta na Intanet, wanda ya kwatanta manufar kasar Sin ta yafewa kasashen Afirka harajin kwastam, da dokar samar da karuwar tattalin arziki da damammaki a Afirka (AGOA) ta kasar Amurka. Inda aka ce, bisa ka’idar AGOA, gwamnatin kasar Amurka za ta tantance damar kasashen Afirka na samun gatanci a kowace shekara, lamarin da ya haifar da yanayin rashin tabbas. Yayin da a nata bangare, manufar kasar Sin na da dorewa, kana ta kunshi ra’ayi kaucewa tsoma baki cikin harkokin gidan sauran kasashe, saboda haka za ta ba kamfanonin kasashe daban daban damar zuba jari hankalinsu a kwance, ta yadda za ta haifar da gudunmowa ga yunkurin nahiyar Afirka na neman ci gaban tattalin arziki mai dorewa.

To, ko da gangan kasar Sin ta yi wani abu don tabbatar da wannan yanayi na karkacewa? A’a. Kasar Sin ba ta yi komai ba, illa kokarin raya tattalin arzikinta, da ci gaba da zame wa kasashe daban daban abokiyar hulda da za su iya dogaro da ita, da neman samun nasarori tare da su. Hakika babbar manufar kasar ba ta taba canzawa ba. Ta haka, Sin tana kokarin samar da yanayi mai tabbaci ga duniya.

LABARAI MASU NASABA

Wannan Hakki Na Tushe Yana Da Matukar Muhimmanci

Hadin Gwiwar Noma Tsakanin Sin Da Afirka: Daga “Sari Ka Ba Ni” Zuwa ” Zamanintar Da Kansu Tare”

A nata bangare, kasar Amurka tana karbar karin harajin kwastam, duk da cewa ana takaddama a cikin gida kan wannan batu. Tana kuma neman wai “karfafa hadin gwiwa da kasashen Afirka”, yayin da take matsa musu lamba ta fakewa da batutuwan hakkin dan Adam, da addini. Kana duk da cewa tana takama wai tana “kiyaye zaman lafiya a duniya”, hakika tana kaddamar da yake-yake a duniya a kai a kai, ciki har da hare-haren da ita da Isra’ila suke kai wa kasar Iran a halin yanzu. Ko da yake tana haifar da tarin matsaloli a duniya, duk da haka kasar Amurka na tsammanin cewa tana samun nasarori. Ke nan tana neman “samun nasarori” ne bisa tushen haddasa damuwa, da hasara, da wahalhalu, da zubar da jinin mutanen sauran kasashe.

Ban san irin sakamakon da kasar Amurka za ta samu a karshe ba, amma na san tabbas sauran kasashe za su yi watsi da ita, don gujewa mummunan tasirin da take haifar wa duniya. (Bello Wang)

 

Amurka
CGTN Hausa
+ posts Bio
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    Muhallin Halittu Da Aka Yi Gado A Kasar Sin Sun Samu Ci Gaba Ta Fuskar Ba Su Kariya
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    Sin Ta Zama Abin Koyi Na Sauyi Da Ci Gaba Ga Kasashe Da Dama, In Ji Shalva Papuashvili
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    Kasar Sin Na Adawa Da Matakin Amurka Na Amfani Da Tsaron Kasa Wajen Danne Wasu Kamfanonin Sinawa
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    Wannan Hakki Na Tushe Yana Da Matukar Muhimmanci
Amurka
Sulaiman
+ posts Bio
  • Sulaiman
    Muhallin Halittu Da Aka Yi Gado A Kasar Sin Sun Samu Ci Gaba Ta Fuskar Ba Su Kariya
  • Sulaiman
    Sake Jan Damarar Soja Da Japan Ke Yi Karin Alama Ce Mai Hadari
  • Sulaiman
    Shugaban Majalisar Bayar Da Shawara Kan Harkokin Siyasa Ta Kasar Sin Ya Yi Kira Da A Raya Dangantakar Gabobi Biyu Na Mashigin Tekun Taiwan Cikin Lumana
  • Sulaiman
    Sin Ta Zama Abin Koyi Na Sauyi Da Ci Gaba Ga Kasashe Da Dama, In Ji Shalva Papuashvili

MASU ALAKA

Wannan Hakki Na Tushe Yana Da Matukar Muhimmanci
Ra'ayi Riga

Wannan Hakki Na Tushe Yana Da Matukar Muhimmanci

June 13, 2026
Hadin Gwiwar Noma Tsakanin Sin Da Afirka: Daga “Sari Ka Ba Ni” Zuwa ” Zamanintar Da Kansu Tare”
Ra'ayi Riga

Hadin Gwiwar Noma Tsakanin Sin Da Afirka: Daga “Sari Ka Ba Ni” Zuwa ” Zamanintar Da Kansu Tare”

June 12, 2026
Cudanyar Al’Adu Tana Tabbatar Da Kyakkyawar Makomar Sin Da Afirka 
Ra'ayi Riga

Cudanyar Al’Adu Tana Tabbatar Da Kyakkyawar Makomar Sin Da Afirka 

June 10, 2026
Next Post
Ramadan: Lokutan Buda-Baki Da Sahur Na Azumi Na 2

Ramadan: Lokutan Buda-Baki Da Sahur Na Azumi Na 13

Discussion about this post

LABARAI MASU NASABA

Cututtukan Da Aka Fi Fama Da Su Lokacin Damina Da Yadda Za A Kauce Musu (1)

Cututtukan Da Aka Fi Fama Da Su Lokacin Damina Da Yadda Za A Kauce Musu (1)

June 13, 2026
Talauci Ya Sake Karuwa Da Kashi 63 Duk Da Sauye-sauyen Tattalin Arzikin Da Gwamnati Ta Yi – IMF

Talauci Ya Sake Karuwa Da Kashi 63 Duk Da Sauye-sauyen Tattalin Arzikin Da Gwamnati Ta Yi – IMF

June 13, 2026
Muhallin Halittu Da Aka Yi Gado A Kasar Sin Sun Samu Ci Gaba Ta Fuskar Ba Su Kariya

Muhallin Halittu Da Aka Yi Gado A Kasar Sin Sun Samu Ci Gaba Ta Fuskar Ba Su Kariya

June 13, 2026
Gwamnonin Arewa-maso-yamma Sun Kaddamar Da Shirin Rage Radadin Talauci A Yankin

Gwamnonin Arewa-maso-yamma Sun Kaddamar Da Shirin Rage Radadin Talauci A Yankin

June 13, 2026

Sake Jan Damarar Soja Da Japan Ke Yi Karin Alama Ce Mai Hadari

June 13, 2026
NANS Ta Kafa Kwamitin Ganin Yadda Ake Tafiyar Da Ayyukan TETFund

NANS Ta Kafa Kwamitin Ganin Yadda Ake Tafiyar Da Ayyukan TETFund

June 13, 2026
Shugaban Majalisar Bayar Da Shawara Kan Harkokin Siyasa Ta Kasar Sin Ya Yi Kira Da A Raya Dangantakar Gabobi Biyu Na Mashigin Tekun Taiwan Cikin Lumana

Shugaban Majalisar Bayar Da Shawara Kan Harkokin Siyasa Ta Kasar Sin Ya Yi Kira Da A Raya Dangantakar Gabobi Biyu Na Mashigin Tekun Taiwan Cikin Lumana

June 13, 2026
Ghana Za Ta Kai Ƙarar Canada Kotu Kan Hana Thomas Partey Shiga Ƙasar

Ghana Za Ta Kai Ƙarar Canada Kotu Kan Hana Thomas Partey Shiga Ƙasar

June 13, 2026
Sin Ta Zama Abin Koyi Na Sauyi Da Ci Gaba Ga Kasashe Da Dama, In Ji Shalva Papuashvili

Sin Ta Zama Abin Koyi Na Sauyi Da Ci Gaba Ga Kasashe Da Dama, In Ji Shalva Papuashvili

June 13, 2026
Garkuwa Da Mutane Na Barazana Ga Dalibai Miliyan 1.9 Masu Jarrabawar WAEC A Sassan Nijeriya

Garkuwa Da Mutane Na Barazana Ga Dalibai Miliyan 1.9 Masu Jarrabawar WAEC A Sassan Nijeriya

June 13, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.