ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Saturday, July 25, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Yunkurin Kasar Amurka Na “Neman Cin Nasara” Ya Sa Sauran Kasashe Yin Watsi Da Ita

by CGTN Hausa and Sulaiman
5 months ago
Amurka

A wani jawabin da ya yi ga majalissun dokokin kasar Amurka a kwanan baya, shugaba Donald Trump ya ce kasarsa na ta samun nasarori a duniya. Sai dai yunkurin kasar na “neman cin nasara” ya kan sanya mutanen duniya damuwa, da daukar matakai na yin watsi da kasar.

Misali, jaridar Business Day ta kasar Najeriya ta wallafa wata makala a shafinta na Intanet a kwanakin baya, wadda ta bayyana cewa, canzawar manufar harajin kwastam ta kasar Amurka ta sa ’yan kasuwar Najeriya damuwa, lamarin da ya sanya raguwar darajar kayayyakin da aka fitar da su daga Najeriya zuwa Amurka a shekarar 2025 da kimanin kaso 14%, bisa jimillar shekarar 2024. Baya ga haka, darajar kayayyakin da aka fitar da su daga Najeriya zuwa kasar Sin ta karu da kimanin 81% a cikin shekaru 3 da suka wuce. Kana ana sa ran ganin wani yanayi na gagauta karkata ga kasuwannin kasar Sin a cinikin da ’yan kasuwar Najeriya suke yi, bisa la’akari da manufar Sin ta yafe wa kasashe 53 dake nahiyar Afirka harajin kwastam, wadda za ta fara aiki a watan Mayun dake tafe.

A fannin hada-hadar kudi ma ana iya ganin yanayi na “karkata ga kasar Sin”. Misali, kamfanin dillancin labarai na Bloomberg na kasar Amurka ya ruwaito Jeremy Awori, shugaban kamfanin Ecobank, na cewar manufar harajin kwastam ta kasar Amurka dake canzawa a kai a kai ta haifar da mummunan tasiri kan kamfanonin kasashen Afirka, saboda haka bangaren Afirka na kokarin rage dogaro kan dalar Amurka, maimakonta ana karkata ga kudin Sin RMB da kudaden kasashen Afirka wajen gudanar da ciniki.

ADVERTISEMENT

Dalilin da ya sa ake samun wannan karkacewa shi ne, domin yadda aka gano bambanci. Misali, a kwanan nan, cibiyar nazarin tsare-tsaren duniya ta HORN ta kasar Kenya ta wallafa wani bayani a shafinta na Intanet, wanda ya kwatanta manufar kasar Sin ta yafewa kasashen Afirka harajin kwastam, da dokar samar da karuwar tattalin arziki da damammaki a Afirka (AGOA) ta kasar Amurka. Inda aka ce, bisa ka’idar AGOA, gwamnatin kasar Amurka za ta tantance damar kasashen Afirka na samun gatanci a kowace shekara, lamarin da ya haifar da yanayin rashin tabbas. Yayin da a nata bangare, manufar kasar Sin na da dorewa, kana ta kunshi ra’ayi kaucewa tsoma baki cikin harkokin gidan sauran kasashe, saboda haka za ta ba kamfanonin kasashe daban daban damar zuba jari hankalinsu a kwance, ta yadda za ta haifar da gudunmowa ga yunkurin nahiyar Afirka na neman ci gaban tattalin arziki mai dorewa.

To, ko da gangan kasar Sin ta yi wani abu don tabbatar da wannan yanayi na karkacewa? A’a. Kasar Sin ba ta yi komai ba, illa kokarin raya tattalin arzikinta, da ci gaba da zame wa kasashe daban daban abokiyar hulda da za su iya dogaro da ita, da neman samun nasarori tare da su. Hakika babbar manufar kasar ba ta taba canzawa ba. Ta haka, Sin tana kokarin samar da yanayi mai tabbaci ga duniya.

LABARAI MASU NASABA

Yadda Kasar Sin Ta Samar Da Ci Gaba Na Bai Daya

Sin Tana Son More Damammakin Fasahar AI a Maimakon Babakere a Wannan Bangare Da Kasashen Yamma Suka Dade Suna Yi

A nata bangare, kasar Amurka tana karbar karin harajin kwastam, duk da cewa ana takaddama a cikin gida kan wannan batu. Tana kuma neman wai “karfafa hadin gwiwa da kasashen Afirka”, yayin da take matsa musu lamba ta fakewa da batutuwan hakkin dan Adam, da addini. Kana duk da cewa tana takama wai tana “kiyaye zaman lafiya a duniya”, hakika tana kaddamar da yake-yake a duniya a kai a kai, ciki har da hare-haren da ita da Isra’ila suke kai wa kasar Iran a halin yanzu. Ko da yake tana haifar da tarin matsaloli a duniya, duk da haka kasar Amurka na tsammanin cewa tana samun nasarori. Ke nan tana neman “samun nasarori” ne bisa tushen haddasa damuwa, da hasara, da wahalhalu, da zubar da jinin mutanen sauran kasashe.

Ban san irin sakamakon da kasar Amurka za ta samu a karshe ba, amma na san tabbas sauran kasashe za su yi watsi da ita, don gujewa mummunan tasirin da take haifar wa duniya. (Bello Wang)

 

Amurka
CGTN Hausa
+ posts Bio
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    An Zartas Da Sanarwar Chengdu A Taron Ministocin Kungiyar APEC Kan Harkar Raya Fasahohin Dijital Da AI
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    Sin Ta Kara Kamfanoni 14 Na Tarayyar Turai Cikin Jerin Wadanda Aka Hana Fitar Masu Da Kaya
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    Yadda Kasar Sin Ta Samar Da Ci Gaba Na Bai Daya
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    Wani Dalilin Da Ya Sa Al’Ummar Afirka Ke Kaunar Kasar Sin Shi Ne Yadda Take Kokarin Zuba Musu Jari
Amurka
Sulaiman
+ posts Bio
  • Sulaiman
    An Karrama Masana Ilimin Lissafi Na Kasar Sin Da Lambobin Yabo Na Fields Medal
  • Sulaiman
    Ta Da Zaune Tsaye Da Philippines Ta Yi A Teku Ba Zai Lalata Dangantakar Hadin Gwiwar Sin Da ASEAN Ba
  • Sulaiman
    An Zartas Da Sanarwar Chengdu A Taron Ministocin Kungiyar APEC Kan Harkar Raya Fasahohin Dijital Da AI
  • Sulaiman
    Sin Ta Kara Kamfanoni 14 Na Tarayyar Turai Cikin Jerin Wadanda Aka Hana Fitar Masu Da Kaya

MASU ALAKA

Yadda Kasar Sin Ta Samar Da Ci Gaba Na Bai Daya
Ra'ayi Riga

Yadda Kasar Sin Ta Samar Da Ci Gaba Na Bai Daya

July 24, 2026
Sin Tana Son More Damammakin Fasahar AI a Maimakon Babakere a Wannan Bangare Da Kasashen Yamma Suka Dade Suna Yi
Ra'ayi Riga

Sin Tana Son More Damammakin Fasahar AI a Maimakon Babakere a Wannan Bangare Da Kasashen Yamma Suka Dade Suna Yi

July 24, 2026
Me Ya Sa Ra’ayin Duniya Ke Karkata Zuwa Sin Yayin da Tasirin Amurka Ke Faduwa?
Ra'ayi Riga

Me Ya Sa Ra’ayin Duniya Ke Karkata Zuwa Sin Yayin da Tasirin Amurka Ke Faduwa?

July 23, 2026
Next Post
Ramadan: Lokutan Buda-Baki Da Sahur Na Azumi Na 2

Ramadan: Lokutan Buda-Baki Da Sahur Na Azumi Na 13

LABARAI MASU NASABA

Amurka

Obasanjo Da Atiku Sun Sake Musayar Zafafan Kalaman Zargin Juna

July 25, 2026
Manufofin Tattalin Arzikin Gwamnatin Tinubu Sun Lalata Rayukan Al’ummar Nijeriya —ADC

Manufofin Tattalin Arzikin Gwamnatin Tinubu Sun Lalata Rayukan Al’ummar Nijeriya —ADC

July 25, 2026
An Karrama Masana Ilimin Lissafi Na Kasar Sin Da Lambobin Yabo Na Fields Medal

An Karrama Masana Ilimin Lissafi Na Kasar Sin Da Lambobin Yabo Na Fields Medal

July 24, 2026
Ta Da Zaune Tsaye Da Philippines Ta Yi A Teku Ba Zai Lalata Dangantakar Hadin Gwiwar Sin Da ASEAN Ba

Ta Da Zaune Tsaye Da Philippines Ta Yi A Teku Ba Zai Lalata Dangantakar Hadin Gwiwar Sin Da ASEAN Ba

July 24, 2026
Jadawalin INEC:Kotun Daukaka Kara Ta Kassara Fatan Jam’iyyu Da ‘Yan Siyasa

Jadawalin INEC:Kotun Daukaka Kara Ta Kassara Fatan Jam’iyyu Da ‘Yan Siyasa

July 24, 2026
An Zartas Da Sanarwar Chengdu A Taron Ministocin Kungiyar APEC Kan Harkar Raya Fasahohin Dijital Da AI

An Zartas Da Sanarwar Chengdu A Taron Ministocin Kungiyar APEC Kan Harkar Raya Fasahohin Dijital Da AI

July 24, 2026
NNPP Za Ta Kwace Mulki A Jihar Imo – Kwankwaso

Jam’iyyar NDC Ta Shirya Tsaf Domin Kafa Gwamnati A 2027 —Kwankwaso

July 24, 2026
Sin Ta Kara Kamfanoni 14 Na Tarayyar Turai Cikin Jerin Wadanda Aka Hana Fitar Masu Da Kaya

Sin Ta Kara Kamfanoni 14 Na Tarayyar Turai Cikin Jerin Wadanda Aka Hana Fitar Masu Da Kaya

July 24, 2026
Kashim Shettima Ya Mayar Da Martani Kan Tsadar Rayuwa

Kyamar Baki: Shettima Ya Ja Kunnen Gwamnatin Afirka Ta Kudu

July 24, 2026
Yadda Kasar Sin Ta Samar Da Ci Gaba Na Bai Daya

Yadda Kasar Sin Ta Samar Da Ci Gaba Na Bai Daya

July 24, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.