Tsohon Mataimakin Shugaban Ƙasa kuma ɗan takarar shugaban ƙasa na jam’iyyar ADC, Atiku Abubakar, ya naɗa jigo a jam’iyyar, Kenneth Okonkwo, a matsayin kakakin yaƙin neman zaɓensa.
Naɗin Okonkwo ya zo ne cikin yanayi mai ɗaukar hankali, kasancewar makonni kaɗan da suka gabata ya fito fili ya soki jam’iyyar kan zaɓin wanda za a tsayar a matsayin mataimakin ɗan takarar shugaban ƙasa a babban zaɓen shekarar 2027 mai zuwa.
Da yake sanar da naɗin a cikin wata sanarwa da ya wallafa a shafinsa na X a ranar Alhamis, Okonkwo ya bayyana godiyarsa ga Atiku bisa amincewar da ya nuna masa.
Ya ce, “Ina bai wa Allah ɗaukaka gaba ɗaya bisa naɗa ni da Mai Girma Atiku Abubakar ya yi a matsayin kakakinsa. Ina gode wa HE AA bisa wannan babbar amincewa da ya nuna a gare ni.”














