Yau Litinin, cibiyar nazarin ilmin kimiyyar zamantakewa ta kasar Sin, ta kira taron manema labarai a birnin Beijing, fadar mulkin kasar Sin game da babban taron ilmin gargajiya na kasa da kasa karo na biyu.
A yayin taron, cibiyar ta sanar da cewa, taro na wannan karo da za a gudanar a birnin Athens na kasar Girka a tsakanin ranakun 9 zuwa 10 ga watan nan na Yuni, takensa shi ne, “Zantawa tsakanin zamanin gargajiya da zamanin yau: Yadda basirar gargajiya ta wayar da kanmu”.
Haka kuma, ta ce, a yayin taron, za a gayyaci masana a fanonnin nazarin ilmin gargajiya mai nasaba da ilmin wayewar kai, da al’adu, da kuma nazarin kayayyakin tarihi da dai sauransu, daga kasashen duniya daban daban, inda za a yi tattaunawa mai zurfi kan batutuwan dake shafar wayewar kai ta gargajiya.
Bugu da kari, a wannan karo, cibiyar nazarin ilmin kimiyyar zamantakewa ta kasar Sin, da ma’aikatar kula da harkokin ba da ilmi ta kasar Sin, da ma’aikatar kula da harkokin al’adu da yawon shakatawa ta kasar Sin, da ma’aikatar al’adun kasar Girka, da kwalejin kimiyya da fasaha na Athens dake Girka ne za su yi hadin gwiwar jagorantar gudanar da babban taron. (Mai Fassara: Maryam Yang)















Discussion about this post