Ɗan takarar shugaban kasa na jam’iyyar NDC, Peter Obi, ya ce zai saki Nnamdi Kanu idan aka zaɓe shi a matsayin shugaban ƙasa a 2027, yana mai cewa warware matsalar Kanu na buƙatar mafita ta siyasa fiye da amfani da ƙarfin mulki kawai.
Obi ya bayyana cewa batun Kanu ya daɗe yana jawo rarrabuwar kawuna da tashin hankali a Kudu maso Gabas, don haka gwamnati mai nagarta ya kamata ta fifita tattaunawa, da sulhu da samar da adalci domin dawo da zaman lafiya. Wannan ya yi daidai da matsayinsa na baya inda ya sha kira da a bi hanyar tattaunawa kan lamarin.
A cewarsa, Nijeriya na buƙatar shugabanci mai haɗa kan al’umma, ba wanda zai ƙara raba su ba. Ya jaddada cewa magance rikice-rikicen yankuna daban-daban na buƙatar sauraro da fahimtar ƙorafe-ƙorafen jama’a.
Kalaman Obi na zuwa ne yayin da batun tsarewar Kanu ke ci gaba da zama muhimmin batu a siyasar Nijeriya, musamman a yankin Kudu maso Gabas, inda da dama ke neman a warware lamarin ta hanyar siyasa.















Discussion about this post