Sufeto Janar na ƴansandan na ƙasa, Olatunji Rilwan Disu, ya umarci mataimakin kwamishinan ‘yansanda mai kula da sashin sa ido na rundunar ‘yansanda (PMU) da ya binciki ƙorafin da ke neman gudanar da bincike kan wasu manyan jami’an ‘yansanda biyu bisa zargin hannu a kisan fitaccen mai fafutuka kuma marubucin yanar gizo, Abubakar Idris wanda aka fi sani da Dadiyata.
Wannan umarni na ƙunshe ne cikin wata takardar tabbatar da karɓar ƙorafi daga ofishin Sufeto Janar na ‘Yansanda da ke shalƙwatar rundunar a Abuja mai ɗauke da kwanan watan 8 ga Mayu, 2026. Takardar ta tabbatar da cewa an karɓi koken da lauyoyi suka gabatar na neman “bincike mai zaman kansa cikin gaskiya” kan zargin da ake yi wa CSP Hussaini Gimba da CSP Hassan Gimba.
Wani Lauyan daga Kano, Barrister Abba A. Hikima, wanda ya gabatar da koken, ya buƙaci rundunar ‘yansanda ta binciki wasu zarge-zarge da aka ce tsohon hadimin tsohon gwamnan Zamfara, Bello Matawalle, Muhammad Musa Kamarawa, ya yi. A cikin zargin, Kamarawa ya ce jami’an sun yi barazanar kashe shi “kamar yadda suka kashe Dadiyata da Saminu S/Fada Gusau a gabana.”
Dadiyata, malami kuma mai sharhi a kafafen sada zumunta, ya ɓace ne tun watan Agustan 2019 bayan wasu mutane da ba a san ko su waye ba sun sace shi daga gidansa a jihar Kaduna. Tun daga lokacin ba a sake jin ɗuriyarsa ba, lamarin da ya jawo kiraye-kirayen ƙungiyoyin kare haƙƙin bil’adama da masu fafutuka na neman cikakken bincike kan batun.
Rundunar ‘yansanda ta ce an tura koken zuwa sashin da ya dace domin ɗaukar mataki, sai dai ba ta bayyana lokacin da binciken zai fara ko za a gayyaci jami’an da ake zargi domin amsa tambayoyi ba.














Discussion about this post