ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Monday, July 27, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Zargin Kashe Dadiyata: Sufeto Janar Ya Ba Da Umarnin Binciken Wasu Jami’ai

by Abubakar Sulaiman
3 months ago

Sufeto Janar na ƴansandan na ƙasa, Olatunji Rilwan Disu, ya umarci mataimakin kwamishinan ‘yansanda mai kula da sashin sa ido na rundunar ‘yansanda (PMU) da ya binciki ƙorafin da ke neman gudanar da bincike kan wasu manyan jami’an ‘yansanda biyu bisa zargin hannu a kisan fitaccen mai fafutuka kuma marubucin yanar gizo, Abubakar Idris wanda aka fi sani da Dadiyata.

Wannan umarni na ƙunshe ne cikin wata takardar tabbatar da karɓar ƙorafi daga ofishin Sufeto Janar na ‘Yansanda da ke shalƙwatar rundunar a Abuja mai ɗauke da kwanan watan 8 ga Mayu, 2026. Takardar ta tabbatar da cewa an karɓi koken da lauyoyi suka gabatar na neman “bincike mai zaman kansa cikin gaskiya” kan zargin da ake yi wa CSP Hussaini Gimba da CSP Hassan Gimba.

Wani Lauyan daga Kano, Barrister Abba A. Hikima, wanda ya gabatar da koken, ya buƙaci rundunar ‘yansanda ta binciki wasu zarge-zarge da aka ce tsohon hadimin tsohon gwamnan Zamfara, Bello Matawalle, Muhammad Musa Kamarawa, ya yi. A cikin zargin, Kamarawa ya ce jami’an sun yi barazanar kashe shi “kamar yadda suka kashe Dadiyata da Saminu S/Fada Gusau a gabana.”

ADVERTISEMENT

Dadiyata, malami kuma mai sharhi a kafafen sada zumunta, ya ɓace ne tun watan Agustan 2019 bayan wasu mutane da ba a san ko su waye ba sun sace shi daga gidansa a jihar Kaduna. Tun daga lokacin ba a sake jin ɗuriyarsa ba, lamarin da ya jawo kiraye-kirayen ƙungiyoyin kare haƙƙin bil’adama da masu fafutuka na neman cikakken bincike kan batun.

Rundunar ‘yansanda ta ce an tura koken zuwa sashin da ya dace domin ɗaukar mataki, sai dai ba ta bayyana lokacin da binciken zai fara ko za a gayyaci jami’an da ake zargi domin amsa tambayoyi ba.

LABARAI MASU NASABA

Sojojin Ruwa Sun Cafke Jirgin Ruwa Maƙare Da Ɗanyen Mai Na Sata

Arewa Ta Rasa Alƙiblarta – Dattawan Arewa

Abubakar Sulaiman
Website |  + postsBio
  • Abubakar Sulaiman
    ADC Ta Buƙaci Tinubu Ya Bai Wa Waɗanda Aka Sace A Kaiama Da Borno Kulawa
  • Abubakar Sulaiman
    Sojojin Ruwa Sun Cafke Jirgin Ruwa Maƙare Da Ɗanyen Mai Na Sata
  • Abubakar Sulaiman
    Shugaban Ƙasa Tinubu Ya Naɗa Sabon Mai Ba Shi Shawara
  • Abubakar Sulaiman
    Ƴan Bindiga Sun Yi Garkuwa Da Alƙalin Babbar Kotu A Kebbi

MASU ALAKA

Manyan Labarai

Sojojin Ruwa Sun Cafke Jirgin Ruwa Maƙare Da Ɗanyen Mai Na Sata

July 26, 2026
Arewa Ta Rasa Alƙiblarta – Dattawan Arewa
Manyan Labarai

Arewa Ta Rasa Alƙiblarta – Dattawan Arewa

July 26, 2026
Gwamna Uba Sani Ya Ƙaddamar Da Rabon Taki Kyauta Ga Manoma 150,000  A Kaduna
Manyan Labarai

Gwamna Uba Sani Ya Ƙaddamar Da Rabon Taki Kyauta Ga Manoma 150,000 A Kaduna

July 26, 2026
Next Post
A Zango Mai Zuwa Za A Fara Aikin Dala Miliyan Daya A Tashar Jirgin Ruwa Ta Legas – Dantsoho

Shugaban NPA Ya Kara Jaddada Bukatar Yi Wa Tashoshin Jiragen Ruwan Kasa Garanbawul

LABARAI MASU NASABA

Auto Draft

ADC Ta Buƙaci Tinubu Ya Bai Wa Waɗanda Aka Sace A Kaiama Da Borno Kulawa

July 27, 2026

Sojojin Ruwa Sun Cafke Jirgin Ruwa Maƙare Da Ɗanyen Mai Na Sata

July 26, 2026
Sin Za Ta Ci Gaba Da Kare Ikon Mulkin Yankuna Da Hakkoki Da Moriyarta Ta Teku

Sin Za Ta Ci Gaba Da Kare Ikon Mulkin Yankuna Da Hakkoki Da Moriyarta Ta Teku

July 26, 2026
Xi Jinping Ya Mika Sakon Murnar Cika Shekaru 61 Da Samun ‘Yancin Kai Ga Shugaban Maldives

Xi Jinping Ya Mika Sakon Murnar Cika Shekaru 61 Da Samun ‘Yancin Kai Ga Shugaban Maldives

July 26, 2026

Shugaban Ƙasa Tinubu Ya Naɗa Sabon Mai Ba Shi Shawara

July 26, 2026
Sin Ta Ayyana Shirin Ko-ta-kwana Na Samar Da Tallafin Gaggawa Ga Lardin Guangdong

Sin Ta Ayyana Shirin Ko-ta-kwana Na Samar Da Tallafin Gaggawa Ga Lardin Guangdong

July 26, 2026
Fina-finan Kasar Sin Suna Haskakawa Tare Da Samar Da Dimbin Kudaden Shiga A Zangon Nuna Fina-finai Na Lokacin Zafi Na Bana

Fina-finan Kasar Sin Suna Haskakawa Tare Da Samar Da Dimbin Kudaden Shiga A Zangon Nuna Fina-finai Na Lokacin Zafi Na Bana

July 26, 2026
Shugaban Senegal Ya Jinjinawa Kasar Sin Bisa Taimakon Gina Zaurukan Gudanar Da Wasannin Gasar Olympics Ta Matasa

Shugaban Senegal Ya Jinjinawa Kasar Sin Bisa Taimakon Gina Zaurukan Gudanar Da Wasannin Gasar Olympics Ta Matasa

July 26, 2026

Ƴan Bindiga Sun Yi Garkuwa Da Alƙalin Babbar Kotu A Kebbi

July 26, 2026
Bala Mohammed

Sadakin Budurwa ₦3,000 Na Bazawara ₦1,500: Gwamnatin Bauchi Ta Ƙaryata Batun

July 26, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.