Shugaban hukumar kula da Tashoshin Jiragen Ruwa na Kasa Abubakar Dakta Dantsoho, ya bukaci da a gaggauta yiwa Tashoshin Jiragen Ruwa na kasar garanbawul domin a mayar da su, zuwa na zamani.
Dantsoho ya kuma yi gargadi da cewa, rashin yin hakan, zai iya sanya wa Nijeriya ta rasa samun cikakkiyar damar amfana da hada-hadar kasuwanci, ta nahiyar Afirka wato AfCFT.
Shugaban ya bayyana haka ne a taron shekara-shekara na kungiyar ‘yanjarida da ke dauko rahotannin da suka shafi fannin zirga-zirgar Jiragen Ruwa da ya gudana a jihar Legas.
Taken taron shi ne, ‘Tabbatar da an inganta Tashoshin Jiragen ta hanyar amfani da fasahar zamani.
Dantsoho ya jaddada mahimmancin da a yiwa Tashoshin Jiragen Ruwan kasar garanbawul, inda ya yi nuni da cewa, hakan abu ne da ya zama wajibi ba wai wani zabi ba, musamman domin a kara bunkasa fannin tattalin arzikin kasar nan, duba da cewa, Nijeriya na da dimbin albarkatun ruwa, musamman ganin cewa, ita ce a kan gaba wajen hada-hadar sufurin Jiragen Ruwa a Gashi da kuma a Afirka ta Tsakiya , akwai matukar bukatar.
Rashin yiwa Tashoshin Jiragen Ruwan kasar garanbawul, zai sanya a bar kasar a baya a fagen gudanar da gasar sufurin Jiragen a fadin duniya.
A cewarsa, zamantar da Tashoshin zai kara taimaka wa, wajen habaka fannin tattalin arzikin kasar nan.
Shugaban ya kuma zayyano wasu daga cikin sauye-sauye da hukumar ta samar a Tashoshin Jiragen Ruwan kasar .musamman na daga darajar Tashoshin Jiragen Ruwa na Apapa da na Tin Can Island, inda aka sanya masu kayan aiki, bisa nufin kara habaka ayyukan su da kuma rage cunkoso da ake samu, na zirga-zirgar Jiragen Ruwa.
Ya kara da cewa, akwai kuma aikin kananan bunkasa Tashoshin Jiragen Ruwa na Lekki wanda hakan ya kara bunkasa hada-hadar kasuwanci na kasar.















Discussion about this post