Shugaban Ƙasa Bola Ahmed Tinubu ya ƙi karɓar wata tawaga ta musamman da Shugaban Afirka ta Kudu, Cyril Ramaphosa, ya aiko kan hare-haren ƙyamar baƙi da aka sake kai wa ƴan Nijeriya da sauran ƴan Afirka a Afirka ta Kudu.
Daily Trust ta ruwaito cewa a maimakon haka, Shugaban Ƙasan ya umarci wakilan da suka zo da su gana da Ministan Ƙasa na Harkokin Waje, Ambasada Sola Enikanolaiye.
Majiyoyin da suka san da lamarin sun ce tawagar, wadda Ministan Harkokin Ƙasa da Haɗin Kan Ƙasa na Afirka ta Kudu, Ronald Lamola, ke jagoranta, ta isa Abuja a ƙarshen mako ɗauke da saƙo daga Shugaba Ramaphosa.
Sai dai an umarci tawagar da ta je Ma’aikatar Harkokin Waje domin miƙa saƙon ga ministan.
Da aka tuntuɓe shi, mai bai wa Shugaban Ƙasa shawara na musamman kan yaɗa labarai da dabaru, Bayo Onanuga, ya tabbatar wa Daily Trust da faruwar lamarin.
Onanuga ya ce wakilin ya iso ranar Juma’a ba tare da sanar da gwamnatin Nijeriya tun da wuri ba, kuma ya dage sai ya gana da Shugaba Tinubu domin miƙa masa saƙon da kansa.
Ya ce jami’an Ma’aikatar Harkokin Waje sun ɗauki wannan buƙata a matsayin wadda ba ta dace ba.“Da farko dai, wakilin ya iso ranar Juma’a ba tare da sanar da gwamnatin Nijeriya tun da wuri ba. Ya dage cewa sai ya gana da Shugaban Ƙasa ranar Juma’a domin miƙa masa saƙonsa.
“Ma’aikatar Harkokin Waje ta ce wannan buƙata ba ta dace ba. Ma’aikatar ta tsara ganawar ranar Litinin. Amma Shugaba Tinubu ya nemi wakilin da ya miƙa saƙonsa ga Ministan Harkokin Waje,” in ji Onanuga.
Ya ƙara da cewa Shugaban Ƙasa ya umarci Ministan Ƙasa na Harkokin Waje, Ambasada Enikanolaiye, da ya tattauna da wakilin tare da yi masa bayani daga bisani.
A kwanakin nan, ƴan Nijeriya da sauran ƴan ƙasashen Afirka sun sake fuskantar hare-haren ƙyamar baƙi a Afirka ta Kudu.














