ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Sunday, June 7, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Ƴan Arewa Za Su Yi Murna Idan Na Zama Shugaban Ƙasa — Peter Obi

by Abubakar Sulaiman
11 months ago
Arewa

Ɗan takarar shugaban ƙasa na jam’iyyar Labour Party a zaɓen 2023, Peter Obi, ya roƙi ‘yan Arewa da su yarda da shi, yana mai tabbatar da cewa yankin zai yi murna da shugabancinsa idan aka zaɓe sa a 2027.

Yayin wata hira da tashar Channels TV a shirin ‘Sunday Politics’, Obi ya bayyana cewa Arewa ce babban arziƙin Nijeriya saboda ɗimbin filayenta da ba a noma ba da kuma tarihin masana’antunta—duka ya yi alƙawarin farfaɗo da su idan ya zama shugaban ƙasa.

  • Shirin Tinubu Kan Kiwon Dabbobi Zai Samar Da Ayyukan Yi Miliyan 5 Ga Matasa – Jega
  • Dalilin Kwararru Na Bukatar Kafa Cibiyoyin Bincike Kan Nau’ikan Dabbobi A Nijeriya

Obi ya ce matsalolin tsaro da suka addabi wasu sassan Arewa ba za su gagare shi ba. Ya sha alwashin ɗaukar mataki kai tsaye don daƙile ta’addanci da rashin tsaro da ke addabar yankin. A cewarsa, sake dawo da zaman lafiya da farfaɗo da tattalin arziƙin Arewa na da matuƙar muhimmanci ga ci gaban ƙasa gaba ɗaya. “Idan na zama shugaban ƙasa, Arewa za ta yi murna. Na fahimci matsalarsu,” in ji shi.

ADVERTISEMENT

Ya kuma tuna da lokacin da Arewa musamman Kano ke taka rawa a masana’antu da kasuwanci. Obi ya ce Kano na da tarihin masana’antu kamar Bompai, Sharada 1 da Sharada 2, waɗanda a cewarsa za su iya komawa kamar yadda suka kasance. Obi ya bayyana cewa yana da hangen nesa da dabaru da za su inganta tattalin arziƙi da zaman lafiya a Arewa, yana mai jan hankalin yankin da ya ba shi dama domin ya cika waɗannan manufofi.

A ƙarshe, ya sake jaddada buƙatar Nijeriya da ta rungumi sabbin hanyoyi na farfaɗo da tattalin arziki da samar da shugabanni masu gaskiya da jajircewa, yana mai cewa Arewa na da duk abin da ake buƙata domin farfaɗo da ƙasa idan aka tafiyar da albarkatunta da gaskiya da hangen nesa.

LABARAI MASU NASABA

Gwamnatin Kano Ta Dakatar Da Sare Bishiyoyi A Harabar Gidan Talabijin Na Jihar

ADC Na Zawarcin Gawuna Domin Ya Yi Wa Jam’iyyar Takarar Gwamnan Kano A 2027

Arewa
Abubakar Sulaiman
Website |  + postsBio
  • Abubakar Sulaiman
    Darajar Naira Ta Sauka A Kasuwar Musayar Kuɗaɗe
  • Abubakar Sulaiman
    Hadimin El-Rufai Ya Zargi ICPC Da Hana Shi Samun Kulawar Likita
  • Abubakar Sulaiman
    Nijeriya Da Turkiyya Sun Ƙulla Yarjejeniyar Haɗin Gwuiwa Don Bunƙasa Harkar Ma’adinai
  • Abubakar Sulaiman
    Sace Ɗalibai Ya Karu A Mulkin Tinubu Fiye Da Gwamnatocin Baya – Obi

MASU ALAKA

Gwamnatin Kano Ta Dakatar Da Sare Bishiyoyi A Harabar Gidan Talabijin Na Jihar
Labarai

Gwamnatin Kano Ta Dakatar Da Sare Bishiyoyi A Harabar Gidan Talabijin Na Jihar

June 7, 2026
ADC Na Zawarcin Gawuna Domin Ya Yi Wa Jam’iyyar Takarar Gwamnan Kano A 2027
Manyan Labarai

ADC Na Zawarcin Gawuna Domin Ya Yi Wa Jam’iyyar Takarar Gwamnan Kano A 2027

June 7, 2026
Matsalar Tsaro Da Tsadar Kayan Noma Na Barazana Ga Samar Da Abinci A Daminar Bana
Rahotonni

Matsalar Tsaro Da Tsadar Kayan Noma Na Barazana Ga Samar Da Abinci A Daminar Bana

June 6, 2026
Next Post
Zan Yaƙi Duk Wanda Ya Yi Sata Idan Na Zama Shugaban Ƙasa — Atiku

Zan Yaƙi Duk Wanda Ya Yi Sata Idan Na Zama Shugaban Ƙasa — Atiku

LABARAI MASU NASABA

Gwamnatin Kano Ta Dakatar Da Sare Bishiyoyi A Harabar Gidan Talabijin Na Jihar

Gwamnatin Kano Ta Dakatar Da Sare Bishiyoyi A Harabar Gidan Talabijin Na Jihar

June 7, 2026
ADC Na Zawarcin Gawuna Domin Ya Yi Wa Jam’iyyar Takarar Gwamnan Kano A 2027

ADC Na Zawarcin Gawuna Domin Ya Yi Wa Jam’iyyar Takarar Gwamnan Kano A 2027

June 7, 2026
Ba Zai Yiwu A Cimma Yarjejeniya Ba Tare Da Sanya Batun Lebanon Ba —Iran

Ba Zai Yiwu A Cimma Yarjejeniya Ba Tare Da Sanya Batun Lebanon Ba —Iran

June 6, 2026
Kasashen Da Darajar Kudadensu Suka Fadi Da Wadanda Nasu Suka Tashi Sanadiyyar Yakin Iran

Kasashen Da Darajar Kudadensu Suka Fadi Da Wadanda Nasu Suka Tashi Sanadiyyar Yakin Iran

June 6, 2026
An Gudanar Da Taron Tattaunawa Mai Taken “Tides And Voices” A Birnin Sanya Na Sin

An Gudanar Da Taron Tattaunawa Mai Taken “Tides And Voices” A Birnin Sanya Na Sin

June 6, 2026
Real Madrid Ce Tafi Kowacce Kungiya Daraja A Duniya

Real Madrid Ce Tafi Kowacce Kungiya Daraja A Duniya

June 6, 2026
Yawan Zirga-Zirgar Jiragen Kasa Tsakanin Sin Da Turai A Yankin Arewa Maso Gabashin Sin Ya Zarce 3,000 A Bana

Yawan Zirga-Zirgar Jiragen Kasa Tsakanin Sin Da Turai A Yankin Arewa Maso Gabashin Sin Ya Zarce 3,000 A Bana

June 6, 2026
Kofin Duniya: Sababbin Dokokin Da FIFA Ta Kawo

Kofin Duniya: Sababbin Dokokin Da FIFA Ta Kawo

June 6, 2026
Kafar CMG Ta Kulla Yerjeniyoyin Hadin Gwiwa Da Hukumomin Kasar Laos

Kafar CMG Ta Kulla Yerjeniyoyin Hadin Gwiwa Da Hukumomin Kasar Laos

June 6, 2026
Rundunar Sojan Kasar Sin Ta Sa Ido Kan Jirgin Ruwan Yakin Kasar Holland Da Ya Tsallake Mashigin Tekun Taiwan

Rundunar Sojan Kasar Sin Ta Sa Ido Kan Jirgin Ruwan Yakin Kasar Holland Da Ya Tsallake Mashigin Tekun Taiwan

June 6, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.