ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Wednesday, September 9, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Ƴan Bindiga Sun Kashe Ƴansanda 5 A Bauchi

by Abubakar Sulaiman
10 months ago
Bauchi

Ƴan bindiga sun hallaka jami’an ƴansanda biyar tare da jikkata biyu a wani harin kwantan ɓauna da ya afku a ƙauyen Sabon Sara, cikin ƙaramar hukumar Darazo ta Jihar Bauchi. Wani ganau ya tabbatar cewa harin ya faru ne yayin da jami’an ke gudanar da sintirin domin daƙile rikicin manoma da makiyaya a yankin.

Jami’an da suka rasa rayukansu sun haɗa da DSP Ahmad Muhammad na sashin bincike (SID), da ASP Mustapha Muhammad na 10 PMF, da Sufeto Amarhel Yunusa na 10 PMF, da Sufeto Idris Ahmed na 10 PMF, da Kufural Isah Muazu na AKU. Biyu daga cikin jami’an, Sufeto Isah Musa da Sufeto Yusuf Gambo daga sashin SID, sun samu munanan raunuka bayan harin.

  • ‘Yansanda Sun Kama Mutane 4 Kan Zargin Fashi Da Makami A Bauchi
  • An Damke Mutum 11 Da Ake Zargi Da Kisan Wani Matashi A Bauchi

Kakakin rundunar ƴansanda ta jihar, CSP Ahmed Mohammed Wakil, ya ce an samu rahoton ɓullar wasu da ake zargin na ɗauke da makamai a yankin a ranar 22 ga Nuwamban 2025. Bayan rahoton, an tura tawagar haɗin gwuiwa wacce ta ƙunshi RRS, da 10 PMF, da AKU, da SID da jami’an sintiri don gudanar da aikin a asirce. Sai dai yayin sintirin ne aka yi musu kwantan ɓauna, lamarin da ya haddasa musayar wuta mai tsanani tsakanin ɓarayin dajin da jami’an tsaro.

ADVERTISEMENT

Rundunar ta tura ƙarin jami’ai domin ceto waɗanda suka shiga harin tare da kwashe gawarwaki da waɗanda suka jikkata zuwa babban asibitin Darazo. Wakil ya tabbatar da cewa nan gaba kaɗan za a cafko waɗanda suka aikata wannan ɗanyen aiki, tare da sake shiri wajen kare rayuka da dukiyoyin jama’a.

Kwamishinan ƴansanda na jihar, CP Sani-Omolori Aliyu, ya kai ziyarar gani da ido zuwa wurin faruwar lamarin, inda ya miƙa saƙon ta’aziyya ga iyalan waɗanda suka mutu, tare da sake jaddada ƙudirin rundunar wajen ci gaba da kare al’umma daga barazanar ƴan bindiga.

LABARAI MASU NASABA

Hormuz: Iran Ta Kai Muggan Hare-hare Kan Sansanin Amurka A Jordan

Sojoji Sun Dakile Hare-Hare, Sun Ceto Mutane 12 A Zamfara

Bauchi
Abubakar Sulaiman
Website |  + postsBio
  • Abubakar Sulaiman
    Iyalin El-Rufai Sun Bai Ministan Tsaro Wa’adin Kwana 7 Kan Zargin Rikicin Kudancin Kaduna
  • Abubakar Sulaiman
    Atiku Ya Zargi Gwamnatin Tarayya Da Cin Bashi Kamar Mashayin Da Kuɗi Ya Ƙarewa
  • Abubakar Sulaiman
    Boko Haram Ta Kai Hari Adamawa, Ana Fargabar Mutuwar Mutane 11
  • Abubakar Sulaiman
    Ƴan Bindiga Sun Kai Hari Sokoto, Sun Kashe Mutane 7, Sun Yi Garkuwa Da 12

MASU ALAKA

Iran Ta Musanta Ikirarin Trump Tare Da Zafafa Hare-hare Kan Isra’ila
Manyan Labarai

Hormuz: Iran Ta Kai Muggan Hare-hare Kan Sansanin Amurka A Jordan

September 9, 2026
Sojoji
Manyan Labarai

Sojoji Sun Dakile Hare-Hare, Sun Ceto Mutane 12 A Zamfara

September 9, 2026
Ballon D'or
Manyan Labarai

Ballon d’Or: Messi, Yamal, Da Mane Na Cikin ‘Yan Wasa 30 Da Aka Zaɓo

September 8, 2026
Next Post
Tinubu Ya Umarci A Janye Ƴansandan Da Ke Tsaron Manyan Mutane

Tinubu Ya Umarci A Janye Ƴansandan Da Ke Tsaron Manyan Mutane

LABARAI MASU NASABA

Yadda Jami’an ‘Yansanda Suka Yi Garkuwa Da Wani Mazaunin Abuja, Sun Kwashe Fiye Da Naira Miliyan 20 A Asusunsa

Na Sayar Da ’Ya’yana, Na Sace Wasu 19 – Wata Da Ake Zargi Da Safarar Yara

September 9, 2026
Iran Ta Musanta Ikirarin Trump Tare Da Zafafa Hare-hare Kan Isra’ila

Hormuz: Iran Ta Kai Muggan Hare-hare Kan Sansanin Amurka A Jordan

September 9, 2026
ASUU Ta Yi Barazanar Yajin Aiki A Jami’ar Jihar Sokoto

ASUU Ta Yi Barazanar Yajin Aiki A Jami’ar Jihar Sokoto

September 9, 2026
Taron PDP Na Ƙasa: Ɓangaren Wike Ya Kafa Sabon NWC A Abuja

PDP Ta Musanta Mara Wa APM Baya A Bauchi

September 9, 2026
Sojoji

Sojoji Sun Dakile Hare-Hare, Sun Ceto Mutane 12 A Zamfara

September 9, 2026
Batun AI Zai Fi Daukar Hankali A Bikin Baje Kolin Fasahar Zamani Ta Duniya Karo Na 5

Batun AI Zai Fi Daukar Hankali A Bikin Baje Kolin Fasahar Zamani Ta Duniya Karo Na 5

September 8, 2026
Gwamna Radda Ya Samu Goyon Bayan APC A Katsina Gabanin Zaɓen 2027

Gwamna Radda Ya Samu Goyon Bayan APC A Katsina Gabanin Zaɓen 2027

September 8, 2026
Cinikin Wajen Sin Ya Ci Gaba Da Samun Bunkasa Cikin Sauri A Watanni Takwas Na Farkon Bana

Cinikin Wajen Sin Ya Ci Gaba Da Samun Bunkasa Cikin Sauri A Watanni Takwas Na Farkon Bana

September 8, 2026
'Yan Bindiga

‘Yan Bindiga Sun Kashe 2, Sun Yi Garkuwa Da 26 A Kaduna

September 8, 2026
Binciken CGTN Ya Nuna Gamsuwa Da Yadda Baje Kolin CIFTIS Ke Shaida Karfin Gwiwar Sin A Fannin Kara Fadada Bude Kofa Bisa Babban Matsayi

Binciken CGTN Ya Nuna Gamsuwa Da Yadda Baje Kolin CIFTIS Ke Shaida Karfin Gwiwar Sin A Fannin Kara Fadada Bude Kofa Bisa Babban Matsayi

September 8, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.