ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Monday, July 27, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Ƴan Bindiga Sun Kashe Ƴansanda 5 A Bauchi

by Abubakar Sulaiman
8 months ago
Bauchi

Ƴan bindiga sun hallaka jami’an ƴansanda biyar tare da jikkata biyu a wani harin kwantan ɓauna da ya afku a ƙauyen Sabon Sara, cikin ƙaramar hukumar Darazo ta Jihar Bauchi. Wani ganau ya tabbatar cewa harin ya faru ne yayin da jami’an ke gudanar da sintirin domin daƙile rikicin manoma da makiyaya a yankin.

Jami’an da suka rasa rayukansu sun haɗa da DSP Ahmad Muhammad na sashin bincike (SID), da ASP Mustapha Muhammad na 10 PMF, da Sufeto Amarhel Yunusa na 10 PMF, da Sufeto Idris Ahmed na 10 PMF, da Kufural Isah Muazu na AKU. Biyu daga cikin jami’an, Sufeto Isah Musa da Sufeto Yusuf Gambo daga sashin SID, sun samu munanan raunuka bayan harin.

  • ‘Yansanda Sun Kama Mutane 4 Kan Zargin Fashi Da Makami A Bauchi
  • An Damke Mutum 11 Da Ake Zargi Da Kisan Wani Matashi A Bauchi

Kakakin rundunar ƴansanda ta jihar, CSP Ahmed Mohammed Wakil, ya ce an samu rahoton ɓullar wasu da ake zargin na ɗauke da makamai a yankin a ranar 22 ga Nuwamban 2025. Bayan rahoton, an tura tawagar haɗin gwuiwa wacce ta ƙunshi RRS, da 10 PMF, da AKU, da SID da jami’an sintiri don gudanar da aikin a asirce. Sai dai yayin sintirin ne aka yi musu kwantan ɓauna, lamarin da ya haddasa musayar wuta mai tsanani tsakanin ɓarayin dajin da jami’an tsaro.

ADVERTISEMENT

Rundunar ta tura ƙarin jami’ai domin ceto waɗanda suka shiga harin tare da kwashe gawarwaki da waɗanda suka jikkata zuwa babban asibitin Darazo. Wakil ya tabbatar da cewa nan gaba kaɗan za a cafko waɗanda suka aikata wannan ɗanyen aiki, tare da sake shiri wajen kare rayuka da dukiyoyin jama’a.

Kwamishinan ƴansanda na jihar, CP Sani-Omolori Aliyu, ya kai ziyarar gani da ido zuwa wurin faruwar lamarin, inda ya miƙa saƙon ta’aziyya ga iyalan waɗanda suka mutu, tare da sake jaddada ƙudirin rundunar wajen ci gaba da kare al’umma daga barazanar ƴan bindiga.

LABARAI MASU NASABA

Kuri’u Za Su Yi Tasiri A Zaɓen 2027, In Ji INEC

Sojojin Ruwa Sun Cafke Jirgin Ruwa Maƙare Da Ɗanyen Mai Na Sata

Bauchi
Abubakar Sulaiman
Website |  + postsBio
  • Abubakar Sulaiman
    ADC Ta Buƙaci Tinubu Ya Bai Wa Waɗanda Aka Sace A Kaiama Da Borno Kulawa
  • Abubakar Sulaiman
    Sojojin Ruwa Sun Cafke Jirgin Ruwa Maƙare Da Ɗanyen Mai Na Sata
  • Abubakar Sulaiman
    Shugaban Ƙasa Tinubu Ya Naɗa Sabon Mai Ba Shi Shawara
  • Abubakar Sulaiman
    Ƴan Bindiga Sun Yi Garkuwa Da Alƙalin Babbar Kotu A Kebbi

MASU ALAKA

Rashin Tsaro Na Barazana Ga Zaben 2027 —Rahotanni
Manyan Labarai

Kuri’u Za Su Yi Tasiri A Zaɓen 2027, In Ji INEC

July 27, 2026
Bauchi
Manyan Labarai

Sojojin Ruwa Sun Cafke Jirgin Ruwa Maƙare Da Ɗanyen Mai Na Sata

July 26, 2026
Arewa Ta Rasa Alƙiblarta – Dattawan Arewa
Manyan Labarai

Arewa Ta Rasa Alƙiblarta – Dattawan Arewa

July 26, 2026
Next Post
Tinubu Ya Umarci A Janye Ƴansandan Da Ke Tsaron Manyan Mutane

Tinubu Ya Umarci A Janye Ƴansandan Da Ke Tsaron Manyan Mutane

LABARAI MASU NASABA

Rashin Tsaro Na Barazana Ga Zaben 2027 —Rahotanni

Kuri’u Za Su Yi Tasiri A Zaɓen 2027, In Ji INEC

July 27, 2026
Auto Draft

ADC Ta Buƙaci Tinubu Ya Bai Wa Waɗanda Aka Sace A Kaiama Da Borno Kulawa

July 27, 2026
Bauchi

Sojojin Ruwa Sun Cafke Jirgin Ruwa Maƙare Da Ɗanyen Mai Na Sata

July 26, 2026
Sin Za Ta Ci Gaba Da Kare Ikon Mulkin Yankuna Da Hakkoki Da Moriyarta Ta Teku

Sin Za Ta Ci Gaba Da Kare Ikon Mulkin Yankuna Da Hakkoki Da Moriyarta Ta Teku

July 26, 2026
Xi Jinping Ya Mika Sakon Murnar Cika Shekaru 61 Da Samun ‘Yancin Kai Ga Shugaban Maldives

Xi Jinping Ya Mika Sakon Murnar Cika Shekaru 61 Da Samun ‘Yancin Kai Ga Shugaban Maldives

July 26, 2026
Bauchi

Shugaban Ƙasa Tinubu Ya Naɗa Sabon Mai Ba Shi Shawara

July 26, 2026
Sin Ta Ayyana Shirin Ko-ta-kwana Na Samar Da Tallafin Gaggawa Ga Lardin Guangdong

Sin Ta Ayyana Shirin Ko-ta-kwana Na Samar Da Tallafin Gaggawa Ga Lardin Guangdong

July 26, 2026
Fina-finan Kasar Sin Suna Haskakawa Tare Da Samar Da Dimbin Kudaden Shiga A Zangon Nuna Fina-finai Na Lokacin Zafi Na Bana

Fina-finan Kasar Sin Suna Haskakawa Tare Da Samar Da Dimbin Kudaden Shiga A Zangon Nuna Fina-finai Na Lokacin Zafi Na Bana

July 26, 2026
Shugaban Senegal Ya Jinjinawa Kasar Sin Bisa Taimakon Gina Zaurukan Gudanar Da Wasannin Gasar Olympics Ta Matasa

Shugaban Senegal Ya Jinjinawa Kasar Sin Bisa Taimakon Gina Zaurukan Gudanar Da Wasannin Gasar Olympics Ta Matasa

July 26, 2026
Bauchi

Ƴan Bindiga Sun Yi Garkuwa Da Alƙalin Babbar Kotu A Kebbi

July 26, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.