ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Saturday, June 27, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Ƴan Bindiga Sun Kashe Ƴansanda 5 A Bauchi

by Abubakar Sulaiman
7 months ago
Bauchi

Ƴan bindiga sun hallaka jami’an ƴansanda biyar tare da jikkata biyu a wani harin kwantan ɓauna da ya afku a ƙauyen Sabon Sara, cikin ƙaramar hukumar Darazo ta Jihar Bauchi. Wani ganau ya tabbatar cewa harin ya faru ne yayin da jami’an ke gudanar da sintirin domin daƙile rikicin manoma da makiyaya a yankin.

Jami’an da suka rasa rayukansu sun haɗa da DSP Ahmad Muhammad na sashin bincike (SID), da ASP Mustapha Muhammad na 10 PMF, da Sufeto Amarhel Yunusa na 10 PMF, da Sufeto Idris Ahmed na 10 PMF, da Kufural Isah Muazu na AKU. Biyu daga cikin jami’an, Sufeto Isah Musa da Sufeto Yusuf Gambo daga sashin SID, sun samu munanan raunuka bayan harin.

  • ‘Yansanda Sun Kama Mutane 4 Kan Zargin Fashi Da Makami A Bauchi
  • An Damke Mutum 11 Da Ake Zargi Da Kisan Wani Matashi A Bauchi

Kakakin rundunar ƴansanda ta jihar, CSP Ahmed Mohammed Wakil, ya ce an samu rahoton ɓullar wasu da ake zargin na ɗauke da makamai a yankin a ranar 22 ga Nuwamban 2025. Bayan rahoton, an tura tawagar haɗin gwuiwa wacce ta ƙunshi RRS, da 10 PMF, da AKU, da SID da jami’an sintiri don gudanar da aikin a asirce. Sai dai yayin sintirin ne aka yi musu kwantan ɓauna, lamarin da ya haddasa musayar wuta mai tsanani tsakanin ɓarayin dajin da jami’an tsaro.

ADVERTISEMENT

Rundunar ta tura ƙarin jami’ai domin ceto waɗanda suka shiga harin tare da kwashe gawarwaki da waɗanda suka jikkata zuwa babban asibitin Darazo. Wakil ya tabbatar da cewa nan gaba kaɗan za a cafko waɗanda suka aikata wannan ɗanyen aiki, tare da sake shiri wajen kare rayuka da dukiyoyin jama’a.

Kwamishinan ƴansanda na jihar, CP Sani-Omolori Aliyu, ya kai ziyarar gani da ido zuwa wurin faruwar lamarin, inda ya miƙa saƙon ta’aziyya ga iyalan waɗanda suka mutu, tare da sake jaddada ƙudirin rundunar wajen ci gaba da kare al’umma daga barazanar ƴan bindiga.

LABARAI MASU NASABA

TCN Ta Sanar Da Ɗaukewar Wutar Lantarki A Kano Da Wasu Jihohi Huɗu

Yadda Aka Kama Manyan Kwamandojin Boko Haram 7 Suna Dawowa Daga Aikin Hajji

Bauchi
Abubakar Sulaiman
Website |  + postsBio
  • Abubakar Sulaiman
    2027: Jam’iyyun Siyasa Sun Yi Maraba Da Hukuncin Kotu Kan Dakatar Da Jadawalin INEC
  • Abubakar Sulaiman
    ADC Ta Yi Allah-Wadai Da Soke Rajistar NDC, Ta Yi Gargaɗi Kan Barazanar Dimokuraɗiyya
  • Abubakar Sulaiman
    TCN Ta Sanar Da Ɗaukewar Wutar Lantarki A Kano Da Wasu Jihohi Huɗu
  • Abubakar Sulaiman
    Magoya Bayan Pantami Sun Zargi Ana Musgunawa Gombawa Motors A Gombe

MASU ALAKA

TCN Ta Sanar Da Ɗaukewar Wutar Lantarki A Kano Da Wasu Jihohi Huɗu
Manyan Labarai

TCN Ta Sanar Da Ɗaukewar Wutar Lantarki A Kano Da Wasu Jihohi Huɗu

June 27, 2026
Yadda Aka Kama Manyan Kwamandojin Boko Haram 7 Suna Dawowa Daga Aikin Hajji
Manyan Labarai

Yadda Aka Kama Manyan Kwamandojin Boko Haram 7 Suna Dawowa Daga Aikin Hajji

June 27, 2026
NDC Ta Ce Za Ta Ɗaukaka Ƙara Kan Hukuncin Soke Rajistarta
Manyan Labarai

NDC Ta Ce Za Ta Ɗaukaka Ƙara Kan Hukuncin Soke Rajistarta

June 26, 2026
Next Post
Tinubu Ya Umarci A Janye Ƴansandan Da Ke Tsaron Manyan Mutane

Tinubu Ya Umarci A Janye Ƴansandan Da Ke Tsaron Manyan Mutane

LABARAI MASU NASABA

Sace Ɗalibai: Gwamnatin Oyo Ta Sanya Dokar Hana Fita A Ƙananan Hukumomi 10

Sace Ɗalibai: Gwamnatin Oyo Ta Sanya Dokar Hana Fita A Ƙananan Hukumomi 10

June 27, 2026
Sin Ta Yi Maraba Da Yarjejeniyar Fahimtar Juna Da Aka Cimma Tsakanin Amurka Da Iran

Iran Ta Jaddada Cewa Ba Ta Da Wani Shiri Na Bada Damar Binciken Wuraren Nukiliyarta

June 27, 2026
Ribar Manyan Kamfanonin Sin Ta Karu Da Kashi 18.8% Cikin Watanni Biyar Na Farkon Bana

Ribar Manyan Kamfanonin Sin Ta Karu Da Kashi 18.8% Cikin Watanni Biyar Na Farkon Bana

June 27, 2026
Yaushe Za A Gane Kungiyar Da Za Ta Lashe Gasar Premier?

An Raba Jadawalin Gasar Premier Ta Ingila Ta Kakar Wasan 2026/2027

June 27, 2026
Tsarin Kirkire-Kirkire Na Sin Na Kara Kuzari Ga Makomar Masana’antun Duniya

Tsarin Kirkire-Kirkire Na Sin Na Kara Kuzari Ga Makomar Masana’antun Duniya

June 27, 2026
Kofin Duniya

Daga 1930 Zuwa 2026: Yadda Aka Buga Wasa Na Dubu Ɗaya A Gasar Kofin Duniya

June 27, 2026
Wakilin Sin: Kar A Bari Sabon Nau’in Ra’ayin Nuna Karfin Soja Ya Haifar Da Karin Tasiri

Wakilin Sin: Kar A Bari Sabon Nau’in Ra’ayin Nuna Karfin Soja Ya Haifar Da Karin Tasiri

June 27, 2026
Manoma Sun Nemi Tinubu Ya Kara Yawan Tallafin Noma 

Ko Shirin Da Gwamnatin Jihar Katsina Ke Yi Wa Manoma Zai  Amfane Su A wannan Daminar?

June 27, 2026
CDC Ta Afirka Ta Yaba Da Goyon Bayan Da Sin Ta Bayar Da Hadin Gwiwa Mai Karfi Wajen Yaki Da Ebola

CDC Ta Afirka Ta Yaba Da Goyon Bayan Da Sin Ta Bayar Da Hadin Gwiwa Mai Karfi Wajen Yaki Da Ebola

June 27, 2026
Firaministan Guinea Ya Yabi Kasar Sin Bisa Shawarwarin Da Ta Gabatar

Firaministan Guinea Ya Yabi Kasar Sin Bisa Shawarwarin Da Ta Gabatar

June 27, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.