Rundunar ƴan sandan jihar Adamawa ta ce ta fara bincike akan zargin sojoji sun harbi wani hamshaƙin ɗan kasuwa da a ƙaramar hukumar Mubi ta Arewa da ke jihar Adamawa
Kakakim Rundunar SP Suleiman Nguroje ya bayyana haka a wata sanarwar manema labarai da ya fitar a ranar talata.
Kamar yadda sanarwar ta bayyana an kawo rahoton faruwar al’amari ga jami’an ƴan sanda a ranar 3 ga watan Agusta 2026 daga wani mutum mai suna Muslim Abubakar da ke gudumar Yelwa, A ƙaramar hukumar Mubi ta Arewa.
Sanarwar ta cigaba da cewa ana zargin Suleiman Abubakar ya samu raunuka a lokacin wani yamutsi tsakanin da da wasu sojoji a cikin dare Litinin wayewar gari talata.
“Kawo koken ke da wuya jami’an ƴan sanda ƙarƙashin Baturen ƴan sanda na Mubi ta Arewa suka ziyarci inda wannan al’amari ya afku domin tabbatar da cewa wanda ya samu raunuka an kai shi asibiti” inji sanarwar
Rundunar kuma ta bayyana cewa wanda ya samu raunin tuni aka kai shi asibitin Mubi kafin daga baya aka maida shi zuwa wata asibiti da ke Yola.
Sai dai kwamishinan ƴan sanda na jihar Adamawa CP Kabiru Hassan ya umarci sashen bincike da su gudanar da binciken yadda al’amarin ya faru.













