Wani majinyaci daga ƙaramar hukumar Ɗanmusa ta Jihar Katsina, Yusuf Umaru, ya samu tiyatar kyauta ta kimanin naira miliyan ɗaya, bayan shafe shekaru takwas yana fama da ciwo da matsalar yin fitsari.
Umaru, wanda ya bayyana haka bayan an yi masa tiyatar a asibitin ƙashi na Amadi Rimi da ke Katsina, ya ce matsalar ta jefa shi cikin raɗaɗii tare da kawo cikas ga ayyukansa na yau da kullum tsawon shekaru.
Ya ce ya daɗe yana neman magani a wasu asibitoci, amma an buƙaci ya biya kimanin naira 700,000 kuɗin tiyatar kaɗai, yayin da sauran kuɗaɗe da suka haɗa da magunguna, wasu hanyoyin jinya da kuɗin kwanciya a asibiti suka kai kimanin naira 300,000.
A cewarsa, matsalar yin fitsarin cikin sauki ta ƙara tsananta masa rayuwa, yayin da kuɗin samun kulawar likitoci ƙwararru suka gagari ƙarfinsa.
Ya ce halin da yake ciki ya sauya ne bayan an gano shi a matsayin ɗaya daga cikin waɗanda za su amfana da shirin bayar da tallafin lafiya kyauta da gidauniyar Mangal ta ɗauki nauyi a Katsina.
Umaru ya bayyana jin daɗinsa da godiyarsa ga gidauniyar, yana mai cewa tallafin ya dawo masa da fata bayan shafe shekaru yana rayuwa cikin raɗaɗi.
Ya ce tallafin ba wai kawai ya rage masa nauyin biyan kuɗin tiyata ba ne, har ma ya ba shi damar samun kulawar ƙwararrun likitocin da ya daɗe yana buƙata.
Haka kuma, wata wadda ta amfana da shirin, Khadija Abdullahi, ta ce ɗiyarta ƴar shekara biyu ta yi fama da cutar Hydrocele, wato kumburin da ke tattare da ruwa a kusa da gabanta, na tsawon kusan shekara guda.
Ta ce rashin ƙarfin tattalin arziki ya hana iyalinta samun damar biyan kuɗin tiyatar, tana mai bayyana fatan cewa shirin zai taimaka wajen dawo da lafiyar ɗiyarta.
Wata mahaifiya da ta yi magana a madadin ɗanta, Isma’il Bishir, mai shekaru 15, ta ce yaron ya daɗe yana fama da raɗaɗin matsalar duwatsun ƙoda.
Ta ce iyalinsu ba su da ƙarfin biyan kuɗin magani saboda halin da suke ciki na rashin kuɗi, lamarin da ya sa matsalar ta ƙara tsananta kafin a shawarce su da su tuntuɓi gidauniyar Mangal.
A cewarta, bayan tuntuɓar gidauniyar, an sanya wa ɗanta lokacin gudanar da tiyata.
Ta yaba wa gidauniyar bisa samar da maganin kyauta, tana mai cewa tallafin ya kawo sauki ga iyalinta bayan dogon lokaci na fama da matsalar.














