ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Wednesday, September 9, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Tinubu Ya Nemi Malamai Su Taimaka Wajen Yaƙi Da Ƴan Ta’adda

by El-Zaharadeen Umar
4 weeks ago
Malamai

Shugaban ƙasa Bola Ahmad Tunibu ya yi kira ga malaman addini da shugabanin Afrika da sauran ƙasashe da su yi amfani da muryoyin su wajen yaƙi da ƴan ta’adda da masu garkuwa da mutane tare da masu amfani da addini wajen tada zaune tsaye inda ya ce babu wani aikin Allah da sai an haɗa da tada hankali.

Shugaba Tunibu ya yi wannan kira a ranar Lahadi a wani sakon fatan alheri da ya aike a Kano wajen taron Mauludin Sheikh Ahmad Al-Tijjani RTA wanda sakataren gwamnatin tarayya Sanata George Akume ya wakilta.

Da yake jawabi ga Khalifan Tijjaniyya na duniya, malamai, shugabannin addini da mabiya daga Nijeriya da wasu ƙasashe, shugaban ƙasa ya buƙaci cibiyoyin addini da su ƙara ƙaimi wajen wayar da kan al’umma game da ilimin zaman lafiya, fahimtar addini, neman ilimi da kuma tarbiyyantar da matasa bisa ƙyawawan ɗabi’u.

ADVERTISEMENT

Dole ne ku yi amfani da muryoyin ku a kowane lokaci domin ƙalubalentar kisan mutanen da ba su ji, ba su gani ba da ƴan ta’adda ke yi da masu garkuwa da mutane da masu amfani da addini wajen biyan buƙatar kan su. Alaƙar wannan damdala ta ku dole ta ƙara karfi wajen kawo zaman lafiya da ilimin addini tare da bunƙasa jama’ar ku maza da mata” inji shi

“Haka kuma dole ne ku tunawa shugabannin siyasa irin nauyin da ya rataya akan su, sannan ku faɗawa ƴan ƙasa cewa jin haushin abu ba shi zai bada damar yin abinda mutum ya ga dama ba. Dukkan waɗannan abubuwan jagororin mu ya kamata su cigaba da faɗakar da al’umma yadda ake bautar Allah ba ta hanyar kashe -kashen al’umma.”  Inji shugaban ƙasa

LABARAI MASU NASABA

‘Yan Bindiga Sun Kashe 2, Sun Yi Garkuwa Da 26 A Kaduna

Gwamna Radda Ya Gabatar Da Kasafin N828.6bn Na 2027

Shugaba Tunibu ya bayyana cewa wannan taro ya zo a daidai lokacin da al’umma ke fuskantar ƙalubale da faɗace-faɗace da barazanar canjin yanayi da ƙarancin abinci da hare-haren ƴan bindiga da juya al’umma ta wata hanyar da bai daidai ba.

Da yake ambaton wani rahoto na hukumar kula da ƴan gudun hijira ta majalisar ɗinkin duniya Tunibu ya ce mutane miliyan 117.8 ne aka tilasta musu barin gidajensu a faɗin duniya zuwa wasu ƙarshen a shekarar 2025, lamarin da ke ƙara nuna muhimmancin shugabannin addini wajen taimakawa a riƙa ba zuciya hakuri ta hanyar sauraran korafe-korafe da yaƙi da ƙiyayya.

Bola Tunibu ya ce al’umma magoya bayan Tijjaniya suna da wani irin tsari haɗuwa a ƙasashen Afrika da Afrika ta Arewa da za su iya taka muhimmiyar rawa wajen taimakawa zaman lafiya tare da tunkarar duk wani ƙalubalen tsaro da baiwa matasa kyakkyawar kulawa da nuna kauna.

Malamai
El-Zaharadeen Umar
+ postsBio
  • El-Zaharadeen Umar
    https://hausa.leadership.ng/author/el-zaharadeen-umar/
    Cutar Mashako:Yadda Yara Ke Mutuwar Bazata A Jihohin Katsina Da Kano
  • El-Zaharadeen Umar
    https://hausa.leadership.ng/author/el-zaharadeen-umar/
    Mauludin Annabi (SAW): Shugaba Tinubu Ya Nemi A Yi Addu’o’in Nasara Kan Matsalar Tsaro
  • El-Zaharadeen Umar
    https://hausa.leadership.ng/author/el-zaharadeen-umar/
    Shekaru 8 Cikin Raɗaɗi: Wani Bawan Allah Ya Samu Tiyata Kyauta Daga Gidauniyar Mangal
  • El-Zaharadeen Umar
    https://hausa.leadership.ng/author/el-zaharadeen-umar/
    NSCDC Ta Tura Jami’ai 10,210 Da Za Su Sanya Ido A Zaɓen Gwamnan Jihar Osun

MASU ALAKA

'Yan Bindiga
Labarai

‘Yan Bindiga Sun Kashe 2, Sun Yi Garkuwa Da 26 A Kaduna

September 8, 2026
Yadda Taron Tattalin Arziki Da Zuba Jari Na Kwana Biyu Ya Gudana A Katsina
Labarai

Gwamna Radda Ya Gabatar Da Kasafin N828.6bn Na 2027

September 8, 2026
Gwamnan Kebbi Ya Bayyana Shirin Sake Duba Albashin Malaman Firamare
Labarai

Gwamna Idris Ya Rushe Majalisar Shugabannin Hukumar Zaɓe Ta Kebbi

September 8, 2026
Next Post
Alhaji Lawal Musa Daura Ya Sauya Sheƙa Zuwa Jam’iyyar APM A Katsina

Alhaji Lawal Musa Daura Ya Sauya Sheƙa Zuwa Jam’iyyar APM A Katsina

LABARAI MASU NASABA

Batun AI Zai Fi Daukar Hankali A Bikin Baje Kolin Fasahar Zamani Ta Duniya Karo Na 5

Batun AI Zai Fi Daukar Hankali A Bikin Baje Kolin Fasahar Zamani Ta Duniya Karo Na 5

September 8, 2026
Gwamna Radda Ya Samu Goyon Bayan APC A Katsina Gabanin Zaɓen 2027

Gwamna Radda Ya Samu Goyon Bayan APC A Katsina Gabanin Zaɓen 2027

September 8, 2026
Cinikin Wajen Sin Ya Ci Gaba Da Samun Bunkasa Cikin Sauri A Watanni Takwas Na Farkon Bana

Cinikin Wajen Sin Ya Ci Gaba Da Samun Bunkasa Cikin Sauri A Watanni Takwas Na Farkon Bana

September 8, 2026
'Yan Bindiga

‘Yan Bindiga Sun Kashe 2, Sun Yi Garkuwa Da 26 A Kaduna

September 8, 2026
Binciken CGTN Ya Nuna Gamsuwa Da Yadda Baje Kolin CIFTIS Ke Shaida Karfin Gwiwar Sin A Fannin Kara Fadada Bude Kofa Bisa Babban Matsayi

Binciken CGTN Ya Nuna Gamsuwa Da Yadda Baje Kolin CIFTIS Ke Shaida Karfin Gwiwar Sin A Fannin Kara Fadada Bude Kofa Bisa Babban Matsayi

September 8, 2026
Yadda Taron Tattalin Arziki Da Zuba Jari Na Kwana Biyu Ya Gudana A Katsina

Gwamna Radda Ya Gabatar Da Kasafin N828.6bn Na 2027

September 8, 2026
Sin Za Ta Yi Aiki Tare Da Sassa Daban Daban Domin Mayar Da Fasahar AI Wata Dama Ta Cin Gajiya Mai Dorewa

Sin Za Ta Yi Aiki Tare Da Sassa Daban Daban Domin Mayar Da Fasahar AI Wata Dama Ta Cin Gajiya Mai Dorewa

September 8, 2026
Gwamnan Kebbi Ya Bayyana Shirin Sake Duba Albashin Malaman Firamare

Gwamna Idris Ya Rushe Majalisar Shugabannin Hukumar Zaɓe Ta Kebbi

September 8, 2026
Han Zheng Ya Halarci Baje Kolin CIFIT Karo Na 26 Tare Da Gabatar Da Jawabi

Han Zheng Ya Halarci Baje Kolin CIFIT Karo Na 26 Tare Da Gabatar Da Jawabi

September 8, 2026
Wani Soja Ya Kashe Kansa Bayan Kashe Matarsa A Jihar Neja

Kano Za Ta Kafa Sansanonin Sojoji A Ƙananan Hukumomin Da Ke Fuskantar Barazanar Tsaro

September 8, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.