ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Thursday, July 16, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Ƴansanda Sun Gano Bindiga Ƙirar AK-47 Da Ake Alaƙantawa Da Shugaban Wata Kungiyar Sa-Kai (Vigilante)

by Rabi'u Ali Indabawa
3 months ago

Wani haɗin gwiwar jami’an Ƴansandan tare da sauran hukumomin tsaro ya kai ga rushe sansanonin ƴan ta’adda da ake amfani da su wajen garkuwa da mutane da sauran laifuffuka a yankunan Ipo da Igwuruta-Ali da ke karamar hukumar Ikwerre a Jihar Rivers.

A yayin aikin, an kama mutum guda tare da ƙwato makamai da harsasai, ciki har da bindigar pump-action, bindiga kirar AK-47 guda ɗaya, da na’urorin sadarwa. An kuma bayyana cewa wasu da ake zargi da zama a sansanonin sun tsere.

  • Saliba Zai Yi Jinyar Watanni 5 Bayan Raunin Da Ya Samu A Bayansa
  • Kotu Ta Yanke Wa Wani Hukuncin Ɗaurin Shekara 7 Kan Tallan Wiwi A Kafafen Sada Zumunta
  • Ganduje Ya Buƙaci A Yi Siyasar Aƙida Domin Inganta Dimokuraɗiyya A Nijeriya
  • Binciken CGTN: Amfanar Da Kowa Da Kowa Shi Ne Ainihin Alherin Da Fasahohin Kwaikwayon Tunanin Bil Adama Suka Kawo
  • Sin Ta Yi Kira Da A Kafa Tsarin Jagorantar Muhimman Ma’adinai Ga Sauyawa Zuwa Amfani Da Makamashi Mai Tsafta

Mai magana da yawun rundunar ƴansandan jihar, Blessing Agabe, ce ta bayyana hakan a wata sanarwa da ta fitar a Port Harcourt ranar Talata, inda aka aikawa manema labarai.

ADVERTISEMENT

Agabe ta bayyana cewa bindigar pump-action din ana zargin ta shugaban wata ƙungiyar sa-kai ta tsaro ta OSPAC ce, wanda aka ce ƴan bindiga sun yi garkuwa da shi a lokacin da ya jagoranci mutanensa domin fuskantar su a makon da ya gabata.

Sanarwar ta ce, “Rundunar ƴansandan Jihar Riɓers na sanar da jama’a nasarar wani haɗin gwiwar aikin tsaro da aka gudanar kan ƴan ta’adda a jihar.

LABARAI MASU NASABA

Saliba Zai Yi Jinyar Watanni 5 Bayan Raunin Da Ya Samu A Bayansa

Kotu Ta Yanke Wa Wani Hukuncin Ɗaurin Shekara 7 Kan Tallan Wiwi A Kafafen Sada Zumunta

“Bisa umarnin Sufeto Janar na ƴansanda, rundunar na ci gaba da aiki tare da sauran hukumomin tsaro domin ƙara kare rayuka da dukiyoyin jama’a tare da ƙarfafa haɗin kai tsakanin hukumomi.

“A ranar 12 ga Afrilu, 2026, da misalin ƙarfe 1:00 na rana, rundunar ta haɗu da sauran hukumomin tsaro ciki har da Nigerian Rundunar Sojojin Ƙasa ta Nijeriya,– Rundunar Sojojin Ruwa ta Nijeriya – Rundunar Sojojin Sama ta Nijeriya– Hukumar Tsaron Farin Kaya ta Ƙasa (DSS) – Hukumar Tsaro da Kariya ta Farar Hula ta Nijeriya domin ƙaddamar da wani aiki na musamman don rushe sansanonin ƴan ta’adda da ake zargin suna ɓoyewa a wuraren.”

Ta ƙara da cewa a yayin aikin, jami’an tsaron sun gano wuraren boye ƴan ta’adda a sansanonin Ipo da Igwuruta-Ali.

A yayin aikin, an ƙwato kayayyaki kamar haka: bindiga ƙirar AK-47 guda ɗaya, bindigar pump-action guda daya, harsasai 274 na 7.62mm, harsasai guda huɗu, kayan kariya na gargajiya, wata babbar almakashi ta ƙarfe, rediyon sadarwa da sauran kayayyaki.

Binciken farko ya nuna cewa bindigar pump-action ɗin na iya zama ta shugaban ƙungiyar tsaro ta OSPAC wanda aka yi garkuwa da shi a baya.

Sanarwar ta ƙara da cewa an yi nasarar rushe sansanonin ƴan ta’addan, yayin da aka kama mutum guda a yankin, wanda ake ci gaba da bincike a kansa, yayin da sauran suka tsere kafin isowar jami’an tsaro.

Ta ce ana ci gaba da bincike domin cafke waɗanda suka tsere da kuma ceto wanda aka yi garkuwa da shi.

A halin da ake ciki, Kwamishinan ƴansandan jihar, Olugbenga Adepoju, ya tabbatar wa al’ummar jihar ƙudirin rundunar na kare rayuka da dukiyoyi.

Sai dai ya buƙaci jama’a da su ci gaba da bai wa hukumomin tsaro haɗin kai ta hanyar bayar da sahihan bayanai cikin lokaci domin kama masu aikata laifuka cikin gaggawa.

Rabi'u Ali Indabawa
+ postsBio
  • Rabi'u Ali Indabawa
    https://hausa.leadership.ng/author/rabiu-ali-indabawa/
    Wasu Fusatattun Mutane Sun Lakaɗa Wa Mutum Biyu Duka Har Lahira A Kaduna
  • Rabi'u Ali Indabawa
    https://hausa.leadership.ng/author/rabiu-ali-indabawa/
    Mun Ɗauki Nauyin Karatun Masu Digiri Ta Hanyar Sayar Da Ƙosai Da Ƙuli-ƙuli —Wasu Ƴan Kasuwa
  • Rabi'u Ali Indabawa
    https://hausa.leadership.ng/author/rabiu-ali-indabawa/
    Adadin Mutanen Da Tsananin Zafi Ya Kashe A Turai Ya Haura Dubu 1,300 —WHO
  • Rabi'u Ali Indabawa
    https://hausa.leadership.ng/author/rabiu-ali-indabawa/
    Pakistan Ta Kashe Mutum 36 A Hare-haren Da Ta Kai Kan Iyakarta Da Afghanistan

MASU ALAKA

Saliba Zai Yi Jinyar Watanni 5 Bayan Raunin Da Ya Samu A Bayansa
Manyan Labarai

Saliba Zai Yi Jinyar Watanni 5 Bayan Raunin Da Ya Samu A Bayansa

July 16, 2026
Kotu Ta Yanke Wa Wani Hukuncin Ɗaurin Shekara 7 Kan Tallan Wiwi A Kafafen Sada Zumunta
Manyan Labarai

Kotu Ta Yanke Wa Wani Hukuncin Ɗaurin Shekara 7 Kan Tallan Wiwi A Kafafen Sada Zumunta

July 16, 2026
Tinubu Yana Zuba Kyawawan Ayyuka A Nijeriya – Ganduje
Manyan Labarai

Ganduje Ya Buƙaci A Yi Siyasar Aƙida Domin Inganta Dimokuraɗiyya A Nijeriya

July 16, 2026
Next Post
Nijeriya Ce Kan Gaba Wajen Wulaƙanta Abinci A Afirka – EU

Nijeriya Ce Kan Gaba Wajen Wulaƙanta Abinci A Afirka - EU

LABARAI MASU NASABA

Saliba Zai Yi Jinyar Watanni 5 Bayan Raunin Da Ya Samu A Bayansa

Saliba Zai Yi Jinyar Watanni 5 Bayan Raunin Da Ya Samu A Bayansa

July 16, 2026
Kotu Ta Yanke Wa Wani Hukuncin Ɗaurin Shekara 7 Kan Tallan Wiwi A Kafafen Sada Zumunta

Kotu Ta Yanke Wa Wani Hukuncin Ɗaurin Shekara 7 Kan Tallan Wiwi A Kafafen Sada Zumunta

July 16, 2026
Tinubu Yana Zuba Kyawawan Ayyuka A Nijeriya – Ganduje

Ganduje Ya Buƙaci A Yi Siyasar Aƙida Domin Inganta Dimokuraɗiyya A Nijeriya

July 16, 2026
Binciken CGTN: Amfanar Da Kowa Da Kowa Shi Ne Ainihin Alherin Da Fasahohin Kwaikwayon Tunanin Bil Adama Suka Kawo

Binciken CGTN: Amfanar Da Kowa Da Kowa Shi Ne Ainihin Alherin Da Fasahohin Kwaikwayon Tunanin Bil Adama Suka Kawo

July 15, 2026
Sin Ta Yi Kira Da A Kafa Tsarin Jagorantar Muhimman Ma’adinai Ga Sauyawa Zuwa Amfani Da Makamashi Mai Tsafta

Sin Ta Yi Kira Da A Kafa Tsarin Jagorantar Muhimman Ma’adinai Ga Sauyawa Zuwa Amfani Da Makamashi Mai Tsafta

July 15, 2026
Gwamna Dauda Lawal Zai Gabatar Da Jawabi A Taron Ƙasa Da Ƙasa Na Jami’ar FUE Zariya

Gwamna Dauda Lawal Zai Gabatar Da Jawabi A Taron Ƙasa Da Ƙasa Na Jami’ar FUE Zariya

July 15, 2026
Neman Raba-Gari Da Sauran Kasashe Zai Kawo Mummuann Tasiri Ga Bangarorin Da Abin Ya Shafa

Neman Raba-Gari Da Sauran Kasashe Zai Kawo Mummuann Tasiri Ga Bangarorin Da Abin Ya Shafa

July 15, 2026
Kevin Kelly: AI Na Iya Taimakawa Wajen Cimma Burin “Koyar Da Dalibai Da Kwazonsu”

Kevin Kelly: AI Na Iya Taimakawa Wajen Cimma Burin “Koyar Da Dalibai Da Kwazonsu”

July 15, 2026
Gwamna Yusuf Ya Bai Wa Masu Kula Da Akwatinan Zaɓe Na APC Filaye 1,540 Da Tallafin Miliyan 100

Gwamna Yusuf Ya Bai Wa Masu Kula Da Akwatinan Zaɓe Na APC Filaye 1,540 Da Tallafin Miliyan 100

July 15, 2026
Sabbin Ministoci

Rashin Tsaro: Majalisar Dattawa Ta Bukaci A Tura Ƙarin Sojoji da ’Yansanda Zuwa Benuwe

July 15, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.