ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Thursday, June 4, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Ƴansanda Sun Gano Bindiga Ƙirar AK-47 Da Ake Alaƙantawa Da Shugaban Wata Kungiyar Sa-Kai (Vigilante)

by Rabi'u Ali Indabawa
2 months ago

Wani haɗin gwiwar jami’an Ƴansandan tare da sauran hukumomin tsaro ya kai ga rushe sansanonin ƴan ta’adda da ake amfani da su wajen garkuwa da mutane da sauran laifuffuka a yankunan Ipo da Igwuruta-Ali da ke karamar hukumar Ikwerre a Jihar Rivers.

A yayin aikin, an kama mutum guda tare da ƙwato makamai da harsasai, ciki har da bindigar pump-action, bindiga kirar AK-47 guda ɗaya, da na’urorin sadarwa. An kuma bayyana cewa wasu da ake zargi da zama a sansanonin sun tsere.

  • Sarki Sanusi II Ya Tuɓe Rawanin Mai Unguwar Rikadawa Kan Badaƙalar Fili
  • Tawagar Masanan Dakile Yaduwar Cututtuka Ta Sin Ta Isa DR Congo
  • Uba Sani Ya Sanya Hannu Kan Sabbin Dokoki A Bangaren Sauya Fannin Wuta, Noma, Da Muhalli
  • Han Zheng Zai Halarci Taron SPIEF Karo Na 29 A Rasha Tare Da Gudanar Da Ziyarar Aiki A Belarus
  • ’Yan Majalisar Tarayya 3 Sun Fice Daga APC Zuwa ADC da PRP

Mai magana da yawun rundunar ƴansandan jihar, Blessing Agabe, ce ta bayyana hakan a wata sanarwa da ta fitar a Port Harcourt ranar Talata, inda aka aikawa manema labarai.

ADVERTISEMENT

Agabe ta bayyana cewa bindigar pump-action din ana zargin ta shugaban wata ƙungiyar sa-kai ta tsaro ta OSPAC ce, wanda aka ce ƴan bindiga sun yi garkuwa da shi a lokacin da ya jagoranci mutanensa domin fuskantar su a makon da ya gabata.

Sanarwar ta ce, “Rundunar ƴansandan Jihar Riɓers na sanar da jama’a nasarar wani haɗin gwiwar aikin tsaro da aka gudanar kan ƴan ta’adda a jihar.

LABARAI MASU NASABA

Sarki Sanusi II Ya Tuɓe Rawanin Mai Unguwar Rikadawa Kan Badaƙalar Fili

Uba Sani Ya Sanya Hannu Kan Sabbin Dokoki A Bangaren Sauya Fannin Wuta, Noma, Da Muhalli

“Bisa umarnin Sufeto Janar na ƴansanda, rundunar na ci gaba da aiki tare da sauran hukumomin tsaro domin ƙara kare rayuka da dukiyoyin jama’a tare da ƙarfafa haɗin kai tsakanin hukumomi.

“A ranar 12 ga Afrilu, 2026, da misalin ƙarfe 1:00 na rana, rundunar ta haɗu da sauran hukumomin tsaro ciki har da Nigerian Rundunar Sojojin Ƙasa ta Nijeriya,– Rundunar Sojojin Ruwa ta Nijeriya – Rundunar Sojojin Sama ta Nijeriya– Hukumar Tsaron Farin Kaya ta Ƙasa (DSS) – Hukumar Tsaro da Kariya ta Farar Hula ta Nijeriya domin ƙaddamar da wani aiki na musamman don rushe sansanonin ƴan ta’adda da ake zargin suna ɓoyewa a wuraren.”

Ta ƙara da cewa a yayin aikin, jami’an tsaron sun gano wuraren boye ƴan ta’adda a sansanonin Ipo da Igwuruta-Ali.

A yayin aikin, an ƙwato kayayyaki kamar haka: bindiga ƙirar AK-47 guda ɗaya, bindigar pump-action guda daya, harsasai 274 na 7.62mm, harsasai guda huɗu, kayan kariya na gargajiya, wata babbar almakashi ta ƙarfe, rediyon sadarwa da sauran kayayyaki.

Binciken farko ya nuna cewa bindigar pump-action ɗin na iya zama ta shugaban ƙungiyar tsaro ta OSPAC wanda aka yi garkuwa da shi a baya.

Sanarwar ta ƙara da cewa an yi nasarar rushe sansanonin ƴan ta’addan, yayin da aka kama mutum guda a yankin, wanda ake ci gaba da bincike a kansa, yayin da sauran suka tsere kafin isowar jami’an tsaro.

Ta ce ana ci gaba da bincike domin cafke waɗanda suka tsere da kuma ceto wanda aka yi garkuwa da shi.

A halin da ake ciki, Kwamishinan ƴansandan jihar, Olugbenga Adepoju, ya tabbatar wa al’ummar jihar ƙudirin rundunar na kare rayuka da dukiyoyi.

Sai dai ya buƙaci jama’a da su ci gaba da bai wa hukumomin tsaro haɗin kai ta hanyar bayar da sahihan bayanai cikin lokaci domin kama masu aikata laifuka cikin gaggawa.

Rabi'u Ali Indabawa
+ postsBio
  • Rabi'u Ali Indabawa
    https://hausa.leadership.ng/author/rabiu-ali-indabawa/
    NSCDC Ta Cafke Mutum 10 Da Ake Zargi Da Satar Kayan Gwamnati Da Kuma Fashi A Kano
  • Rabi'u Ali Indabawa
    https://hausa.leadership.ng/author/rabiu-ali-indabawa/
    Ƴansanda Su Ƙi Karɓar Cin Hancin Naira Miliyan 500 Daga Hannun Dillalin Miyagun Ƙwayoyi
  • Rabi'u Ali Indabawa
    https://hausa.leadership.ng/author/rabiu-ali-indabawa/
    Ƙasashen DR Congo Uganda Da Sudan Sun Haɗa Kai Domin Yaƙar Ibola
  • Rabi'u Ali Indabawa
    https://hausa.leadership.ng/author/rabiu-ali-indabawa/
    Zafin Rana Ya Yi Ajalin Mutum 16 A Indiya

MASU ALAKA

Sarki Sanusi II Ya Tuɓe Rawanin Mai Unguwar Rikadawa Kan Badaƙalar Fili
Manyan Labarai

Sarki Sanusi II Ya Tuɓe Rawanin Mai Unguwar Rikadawa Kan Badaƙalar Fili

June 4, 2026
Uba Sani Ya Sanya Hannu Kan Sabbin Dokoki A Bangaren Sauya Fannin Wuta, Noma, Da Muhalli
Labarai

Uba Sani Ya Sanya Hannu Kan Sabbin Dokoki A Bangaren Sauya Fannin Wuta, Noma, Da Muhalli

June 3, 2026
Tambuwal Ya Jajanta Wa Waɗanda Harin ’Yan Bindiga Ya Shafa A Sokoto, Ya Nemi A Ƙara Tsaro
Manyan Labarai

Tambuwal Ya Jajanta Wa Waɗanda Harin ’Yan Bindiga Ya Shafa A Sokoto, Ya Nemi A Ƙara Tsaro

June 3, 2026
Next Post
Nijeriya Ce Kan Gaba Wajen Wulaƙanta Abinci A Afirka – EU

Nijeriya Ce Kan Gaba Wajen Wulaƙanta Abinci A Afirka - EU

Discussion about this post

LABARAI MASU NASABA

Sarki Sanusi II Ya Tuɓe Rawanin Mai Unguwar Rikadawa Kan Badaƙalar Fili

Sarki Sanusi II Ya Tuɓe Rawanin Mai Unguwar Rikadawa Kan Badaƙalar Fili

June 4, 2026
Tawagar Masanan Dakile Yaduwar Cututtuka Ta Sin Ta Isa DR Congo

Tawagar Masanan Dakile Yaduwar Cututtuka Ta Sin Ta Isa DR Congo

June 3, 2026
Uba Sani Ya Sanya Hannu Kan Sabbin Dokoki A Bangaren Sauya Fannin Wuta, Noma, Da Muhalli

Uba Sani Ya Sanya Hannu Kan Sabbin Dokoki A Bangaren Sauya Fannin Wuta, Noma, Da Muhalli

June 3, 2026
Han Zheng Zai Halarci Taron SPIEF Karo Na 29 A Rasha Tare Da Gudanar Da Ziyarar Aiki A Belarus

Han Zheng Zai Halarci Taron SPIEF Karo Na 29 A Rasha Tare Da Gudanar Da Ziyarar Aiki A Belarus

June 3, 2026
Majalisa Ta Nemi Tinubu Ya Canza Dabarun Yaƙi Da Ta’addanci Don Kawo Ƙarshen Kashe-kashe

’Yan Majalisar Tarayya 3 Sun Fice Daga APC Zuwa ADC da PRP

June 3, 2026
An Fara Watsa Shirye-Shirye Masu Taken “Sha’awar Xi Jinping Ga Al’adu” Da Sauran Fina-Finan Bayyana Labaran Sin A Kasar Laos

An Fara Watsa Shirye-Shirye Masu Taken “Sha’awar Xi Jinping Ga Al’adu” Da Sauran Fina-Finan Bayyana Labaran Sin A Kasar Laos

June 3, 2026
Tambuwal Ya Jajanta Wa Waɗanda Harin ’Yan Bindiga Ya Shafa A Sokoto, Ya Nemi A Ƙara Tsaro

Tambuwal Ya Jajanta Wa Waɗanda Harin ’Yan Bindiga Ya Shafa A Sokoto, Ya Nemi A Ƙara Tsaro

June 3, 2026
Gwamnatin Beijing Ta Amince Da Kafa Cibiyar Kirkire-Kirkiren Fasahar Lissafi Mai Nasaba Da Sararin Samaniya

Gwamnatin Beijing Ta Amince Da Kafa Cibiyar Kirkire-Kirkiren Fasahar Lissafi Mai Nasaba Da Sararin Samaniya

June 3, 2026
Za A Fara Buga Gasar Kofin Sarkin Gombe Bayan Masu Ruwa Da Tsaki Sun Cimma Matsaya

Za A Fara Buga Gasar Kofin Sarkin Gombe Bayan Masu Ruwa Da Tsaki Sun Cimma Matsaya

June 3, 2026
Hada Kai Da ’Yan Awaren Yankin Taiwan Ba Zai Haifar Da Ɗa Mai Ido Ba

Hada Kai Da ’Yan Awaren Yankin Taiwan Ba Zai Haifar Da Ɗa Mai Ido Ba

June 3, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.