ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Wednesday, June 24, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Ƴansanda Sun Gano Bindiga Ƙirar AK-47 Da Ake Alaƙantawa Da Shugaban Wata Kungiyar Sa-Kai (Vigilante)

by Rabi'u Ali Indabawa
2 months ago

Wani haɗin gwiwar jami’an Ƴansandan tare da sauran hukumomin tsaro ya kai ga rushe sansanonin ƴan ta’adda da ake amfani da su wajen garkuwa da mutane da sauran laifuffuka a yankunan Ipo da Igwuruta-Ali da ke karamar hukumar Ikwerre a Jihar Rivers.

A yayin aikin, an kama mutum guda tare da ƙwato makamai da harsasai, ciki har da bindigar pump-action, bindiga kirar AK-47 guda ɗaya, da na’urorin sadarwa. An kuma bayyana cewa wasu da ake zargi da zama a sansanonin sun tsere.

  • Atiku Ya Soki Tsare El-Rufai, Ya Ce Sharuɗan Belinsa Sun Yi Tsauri
  • Trump Ne Zai Jagoranci Bayar Da Kofin Duniya A Wasan Ƙarshe – Infantino
  • ’Yansanda Sun Kama Wani Mutum da Harsasai 174 A Nasarawa
  • Sojoji Sun Kama Ɗan Fashi Da Makami A Taraba
  • An Kashe Mutum 2, 8 Sun Jikkata Yayin Rikici A Bauchi

Mai magana da yawun rundunar ƴansandan jihar, Blessing Agabe, ce ta bayyana hakan a wata sanarwa da ta fitar a Port Harcourt ranar Talata, inda aka aikawa manema labarai.

ADVERTISEMENT

Agabe ta bayyana cewa bindigar pump-action din ana zargin ta shugaban wata ƙungiyar sa-kai ta tsaro ta OSPAC ce, wanda aka ce ƴan bindiga sun yi garkuwa da shi a lokacin da ya jagoranci mutanensa domin fuskantar su a makon da ya gabata.

Sanarwar ta ce, “Rundunar ƴansandan Jihar Riɓers na sanar da jama’a nasarar wani haɗin gwiwar aikin tsaro da aka gudanar kan ƴan ta’adda a jihar.

LABARAI MASU NASABA

Atiku Ya Soki Tsare El-Rufai, Ya Ce Sharuɗan Belinsa Sun Yi Tsauri

’Yansanda Sun Kama Wani Mutum da Harsasai 174 A Nasarawa

“Bisa umarnin Sufeto Janar na ƴansanda, rundunar na ci gaba da aiki tare da sauran hukumomin tsaro domin ƙara kare rayuka da dukiyoyin jama’a tare da ƙarfafa haɗin kai tsakanin hukumomi.

“A ranar 12 ga Afrilu, 2026, da misalin ƙarfe 1:00 na rana, rundunar ta haɗu da sauran hukumomin tsaro ciki har da Nigerian Rundunar Sojojin Ƙasa ta Nijeriya,– Rundunar Sojojin Ruwa ta Nijeriya – Rundunar Sojojin Sama ta Nijeriya– Hukumar Tsaron Farin Kaya ta Ƙasa (DSS) – Hukumar Tsaro da Kariya ta Farar Hula ta Nijeriya domin ƙaddamar da wani aiki na musamman don rushe sansanonin ƴan ta’adda da ake zargin suna ɓoyewa a wuraren.”

Ta ƙara da cewa a yayin aikin, jami’an tsaron sun gano wuraren boye ƴan ta’adda a sansanonin Ipo da Igwuruta-Ali.

A yayin aikin, an ƙwato kayayyaki kamar haka: bindiga ƙirar AK-47 guda ɗaya, bindigar pump-action guda daya, harsasai 274 na 7.62mm, harsasai guda huɗu, kayan kariya na gargajiya, wata babbar almakashi ta ƙarfe, rediyon sadarwa da sauran kayayyaki.

Binciken farko ya nuna cewa bindigar pump-action ɗin na iya zama ta shugaban ƙungiyar tsaro ta OSPAC wanda aka yi garkuwa da shi a baya.

Sanarwar ta ƙara da cewa an yi nasarar rushe sansanonin ƴan ta’addan, yayin da aka kama mutum guda a yankin, wanda ake ci gaba da bincike a kansa, yayin da sauran suka tsere kafin isowar jami’an tsaro.

Ta ce ana ci gaba da bincike domin cafke waɗanda suka tsere da kuma ceto wanda aka yi garkuwa da shi.

A halin da ake ciki, Kwamishinan ƴansandan jihar, Olugbenga Adepoju, ya tabbatar wa al’ummar jihar ƙudirin rundunar na kare rayuka da dukiyoyi.

Sai dai ya buƙaci jama’a da su ci gaba da bai wa hukumomin tsaro haɗin kai ta hanyar bayar da sahihan bayanai cikin lokaci domin kama masu aikata laifuka cikin gaggawa.

Rabi'u Ali Indabawa
+ postsBio
  • Rabi'u Ali Indabawa
    https://hausa.leadership.ng/author/rabiu-ali-indabawa/
    Nijar Ta Rattaba Hannu A Kan Dokar Haramta Auren Jinsi
  • Rabi'u Ali Indabawa
    https://hausa.leadership.ng/author/rabiu-ali-indabawa/
    Za Mu Iya Sayar Da Manmu Ba Tare Da Wata Matsala Ba -Iran
  • Rabi'u Ali Indabawa
    https://hausa.leadership.ng/author/rabiu-ali-indabawa/
    Dattawan Arewa Sun Buƙaci Tinubu Ya Ayyana Dokar Ta-baci Kan Tabarbarewar Tsaro
  • Rabi'u Ali Indabawa
    https://hausa.leadership.ng/author/rabiu-ali-indabawa/
    Nijeriya Ta Karbi Ƴan Nijeriya 268 Da Suka Tsero Daga Afirka Ta Kudu

MASU ALAKA

Tinubu Ya Gaza Wajen Magance Matsalar Tsaro A Nijeriya — Atiku
Manyan Labarai

Atiku Ya Soki Tsare El-Rufai, Ya Ce Sharuɗan Belinsa Sun Yi Tsauri

June 24, 2026
‘Yansanda Sun Kama Ɗan Bindiga Da Kuɗin Fansa Naira Miliyan 5 A Delta
Manyan Labarai

’Yansanda Sun Kama Wani Mutum da Harsasai 174 A Nasarawa

June 24, 2026
Sojoji Sun Kama Ɗan Fashi Da Makami A Taraba
Labarai

Sojoji Sun Kama Ɗan Fashi Da Makami A Taraba

June 24, 2026
Next Post
Nijeriya Ce Kan Gaba Wajen Wulaƙanta Abinci A Afirka – EU

Nijeriya Ce Kan Gaba Wajen Wulaƙanta Abinci A Afirka - EU

LABARAI MASU NASABA

Tinubu Ya Gaza Wajen Magance Matsalar Tsaro A Nijeriya — Atiku

Atiku Ya Soki Tsare El-Rufai, Ya Ce Sharuɗan Belinsa Sun Yi Tsauri

June 24, 2026
Trump Ne Zai Jagoranci Bayar Da Kofin Duniya A Wasan Ƙarshe – Infantino

Trump Ne Zai Jagoranci Bayar Da Kofin Duniya A Wasan Ƙarshe – Infantino

June 24, 2026
‘Yansanda Sun Kama Ɗan Bindiga Da Kuɗin Fansa Naira Miliyan 5 A Delta

’Yansanda Sun Kama Wani Mutum da Harsasai 174 A Nasarawa

June 24, 2026
Sojoji Sun Kama Ɗan Fashi Da Makami A Taraba

Sojoji Sun Kama Ɗan Fashi Da Makami A Taraba

June 24, 2026
An Kashe Mutum 2, 8 Sun Jikkata Yayin Rikici A Bauchi

An Kashe Mutum 2, 8 Sun Jikkata Yayin Rikici A Bauchi

June 24, 2026
Tsohon Shugaban APC Na Kebbi Ya Rasu A Hannun ’Yan Bindiga

Tsohon Shugaban APC Na Kebbi Ya Rasu A Hannun ’Yan Bindiga

June 24, 2026
Ya Kamata Sin Da Birtaniya Su Yi Aiki Tare Don Ci Gaba Da Inganta Dangantakarsu

Ya Kamata Sin Da Birtaniya Su Yi Aiki Tare Don Ci Gaba Da Inganta Dangantakarsu

June 23, 2026
Firaministan Sin Ya Jaddada Muhimmancin Kara Azamar Bunkasa Kirar Kayayyakin Aikin Masana’antu Na Zamani

Firaministan Sin Ya Jaddada Muhimmancin Kara Azamar Bunkasa Kirar Kayayyakin Aikin Masana’antu Na Zamani

June 23, 2026
Gombe Ta Zabge Farashin Taki Da Kashi 50 Cikin 100

Gombe Ta Zabge Farashin Taki Da Kashi 50 Cikin 100

June 23, 2026
Wang Yi Ya Gana Da Babban Sakataren Majalisar Tsaron Masar Da Ministan Fadar Gwamnatin Afirka Ta Kudu A Indiya

Wang Yi Ya Gana Da Babban Sakataren Majalisar Tsaron Masar Da Ministan Fadar Gwamnatin Afirka Ta Kudu A Indiya

June 23, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.