ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Wednesday, June 24, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Ƴansanda Sun Gano Bindiga Ƙirar AK-47 Da Ake Alaƙantawa Da Shugaban Wata Kungiyar Sa-Kai (Vigilante)

by Rabi'u Ali Indabawa
2 months ago

Wani haɗin gwiwar jami’an Ƴansandan tare da sauran hukumomin tsaro ya kai ga rushe sansanonin ƴan ta’adda da ake amfani da su wajen garkuwa da mutane da sauran laifuffuka a yankunan Ipo da Igwuruta-Ali da ke karamar hukumar Ikwerre a Jihar Rivers.

A yayin aikin, an kama mutum guda tare da ƙwato makamai da harsasai, ciki har da bindigar pump-action, bindiga kirar AK-47 guda ɗaya, da na’urorin sadarwa. An kuma bayyana cewa wasu da ake zargi da zama a sansanonin sun tsere.

  • Sin Ta Gabatar Da Tsarin Karfafa Kwarin Gwiwar Kamfanoni Masu Jarin Waje
  • Shugaban Kasar Burundi: Dangantakar Afirka Da Sin Misali Ce Ta Hadin Gwiwar Kasashe Masu Tasowa
  • Zargin Ɓata Suna: Kwankwaso Ya Yi Barazanar Neman Diyyar Naira Biliyan 10 Kan Wani Malamin Coci
  • Li Qiang Ya Halarci Bikin Bude Dandalin Tattalin Arzikin Duniya Na Davos Na Shekarar 2026
  • Xi Ya Yi Kiran Daukar Matakan Zamanantar Da Aikin Gona Da Yankunan Karkara

Mai magana da yawun rundunar ƴansandan jihar, Blessing Agabe, ce ta bayyana hakan a wata sanarwa da ta fitar a Port Harcourt ranar Talata, inda aka aikawa manema labarai.

ADVERTISEMENT

Agabe ta bayyana cewa bindigar pump-action din ana zargin ta shugaban wata ƙungiyar sa-kai ta tsaro ta OSPAC ce, wanda aka ce ƴan bindiga sun yi garkuwa da shi a lokacin da ya jagoranci mutanensa domin fuskantar su a makon da ya gabata.

Sanarwar ta ce, “Rundunar ƴansandan Jihar Riɓers na sanar da jama’a nasarar wani haɗin gwiwar aikin tsaro da aka gudanar kan ƴan ta’adda a jihar.

LABARAI MASU NASABA

Zargin Ɓata Suna: Kwankwaso Ya Yi Barazanar Neman Diyyar Naira Biliyan 10 Kan Wani Malamin Coci

Atiku Ya Soki Tsare El-Rufai, Ya Ce Sharuɗan Belinsa Sun Yi Tsauri

“Bisa umarnin Sufeto Janar na ƴansanda, rundunar na ci gaba da aiki tare da sauran hukumomin tsaro domin ƙara kare rayuka da dukiyoyin jama’a tare da ƙarfafa haɗin kai tsakanin hukumomi.

“A ranar 12 ga Afrilu, 2026, da misalin ƙarfe 1:00 na rana, rundunar ta haɗu da sauran hukumomin tsaro ciki har da Nigerian Rundunar Sojojin Ƙasa ta Nijeriya,– Rundunar Sojojin Ruwa ta Nijeriya – Rundunar Sojojin Sama ta Nijeriya– Hukumar Tsaron Farin Kaya ta Ƙasa (DSS) – Hukumar Tsaro da Kariya ta Farar Hula ta Nijeriya domin ƙaddamar da wani aiki na musamman don rushe sansanonin ƴan ta’adda da ake zargin suna ɓoyewa a wuraren.”

Ta ƙara da cewa a yayin aikin, jami’an tsaron sun gano wuraren boye ƴan ta’adda a sansanonin Ipo da Igwuruta-Ali.

A yayin aikin, an ƙwato kayayyaki kamar haka: bindiga ƙirar AK-47 guda ɗaya, bindigar pump-action guda daya, harsasai 274 na 7.62mm, harsasai guda huɗu, kayan kariya na gargajiya, wata babbar almakashi ta ƙarfe, rediyon sadarwa da sauran kayayyaki.

Binciken farko ya nuna cewa bindigar pump-action ɗin na iya zama ta shugaban ƙungiyar tsaro ta OSPAC wanda aka yi garkuwa da shi a baya.

Sanarwar ta ƙara da cewa an yi nasarar rushe sansanonin ƴan ta’addan, yayin da aka kama mutum guda a yankin, wanda ake ci gaba da bincike a kansa, yayin da sauran suka tsere kafin isowar jami’an tsaro.

Ta ce ana ci gaba da bincike domin cafke waɗanda suka tsere da kuma ceto wanda aka yi garkuwa da shi.

A halin da ake ciki, Kwamishinan ƴansandan jihar, Olugbenga Adepoju, ya tabbatar wa al’ummar jihar ƙudirin rundunar na kare rayuka da dukiyoyi.

Sai dai ya buƙaci jama’a da su ci gaba da bai wa hukumomin tsaro haɗin kai ta hanyar bayar da sahihan bayanai cikin lokaci domin kama masu aikata laifuka cikin gaggawa.

Rabi'u Ali Indabawa
+ postsBio
  • Rabi'u Ali Indabawa
    https://hausa.leadership.ng/author/rabiu-ali-indabawa/
    Nijar Ta Rattaba Hannu A Kan Dokar Haramta Auren Jinsi
  • Rabi'u Ali Indabawa
    https://hausa.leadership.ng/author/rabiu-ali-indabawa/
    Za Mu Iya Sayar Da Manmu Ba Tare Da Wata Matsala Ba -Iran
  • Rabi'u Ali Indabawa
    https://hausa.leadership.ng/author/rabiu-ali-indabawa/
    Dattawan Arewa Sun Buƙaci Tinubu Ya Ayyana Dokar Ta-baci Kan Tabarbarewar Tsaro
  • Rabi'u Ali Indabawa
    https://hausa.leadership.ng/author/rabiu-ali-indabawa/
    Nijeriya Ta Karbi Ƴan Nijeriya 268 Da Suka Tsero Daga Afirka Ta Kudu

MASU ALAKA

Yadda Na Sayar Da Kadarori Na Don Ɗaukar Nauyin Ɗalibai A Ƙasashen Waje – Kwankwaso
Manyan Labarai

Zargin Ɓata Suna: Kwankwaso Ya Yi Barazanar Neman Diyyar Naira Biliyan 10 Kan Wani Malamin Coci

June 24, 2026
Tinubu Ya Gaza Wajen Magance Matsalar Tsaro A Nijeriya — Atiku
Manyan Labarai

Atiku Ya Soki Tsare El-Rufai, Ya Ce Sharuɗan Belinsa Sun Yi Tsauri

June 24, 2026
‘Yansanda Sun Kama Ɗan Bindiga Da Kuɗin Fansa Naira Miliyan 5 A Delta
Manyan Labarai

’Yansanda Sun Kama Wani Mutum da Harsasai 174 A Nasarawa

June 24, 2026
Next Post
Nijeriya Ce Kan Gaba Wajen Wulaƙanta Abinci A Afirka – EU

Nijeriya Ce Kan Gaba Wajen Wulaƙanta Abinci A Afirka - EU

LABARAI MASU NASABA

Sin Ta Gabatar Da Tsarin Karfafa Kwarin Gwiwar Kamfanoni Masu Jarin Waje

Sin Ta Gabatar Da Tsarin Karfafa Kwarin Gwiwar Kamfanoni Masu Jarin Waje

June 24, 2026
Shugaban Kasar Burundi: Dangantakar Afirka Da Sin Misali Ce Ta Hadin Gwiwar Kasashe Masu Tasowa

Shugaban Kasar Burundi: Dangantakar Afirka Da Sin Misali Ce Ta Hadin Gwiwar Kasashe Masu Tasowa

June 24, 2026
Yadda Na Sayar Da Kadarori Na Don Ɗaukar Nauyin Ɗalibai A Ƙasashen Waje – Kwankwaso

Zargin Ɓata Suna: Kwankwaso Ya Yi Barazanar Neman Diyyar Naira Biliyan 10 Kan Wani Malamin Coci

June 24, 2026
Li Qiang Ya Halarci Bikin Bude Dandalin Tattalin Arzikin Duniya Na Davos Na Shekarar 2026

Li Qiang Ya Halarci Bikin Bude Dandalin Tattalin Arzikin Duniya Na Davos Na Shekarar 2026

June 24, 2026
Xi Ya Yi Kiran Daukar Matakan Zamanantar Da Aikin Gona Da Yankunan Karkara

Xi Ya Yi Kiran Daukar Matakan Zamanantar Da Aikin Gona Da Yankunan Karkara

June 24, 2026
Tinubu Ya Gaza Wajen Magance Matsalar Tsaro A Nijeriya — Atiku

Atiku Ya Soki Tsare El-Rufai, Ya Ce Sharuɗan Belinsa Sun Yi Tsauri

June 24, 2026
Trump Ne Zai Jagoranci Bayar Da Kofin Duniya A Wasan Ƙarshe – Infantino

Trump Ne Zai Jagoranci Bayar Da Kofin Duniya A Wasan Ƙarshe – Infantino

June 24, 2026
‘Yansanda Sun Kama Ɗan Bindiga Da Kuɗin Fansa Naira Miliyan 5 A Delta

’Yansanda Sun Kama Wani Mutum da Harsasai 174 A Nasarawa

June 24, 2026
Sojoji Sun Kama Ɗan Fashi Da Makami A Taraba

Sojoji Sun Kama Ɗan Fashi Da Makami A Taraba

June 24, 2026
An Kashe Mutum 2, 8 Sun Jikkata Yayin Rikici A Bauchi

An Kashe Mutum 2, 8 Sun Jikkata Yayin Rikici A Bauchi

June 24, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.