Ƙungiyar Tarayyar Turai (EU), ta bayyana cewa; Nijeriya ce kan gaba a nahiyar Afirka, wajen wulaƙantar da abinci, inda ta ƙiyasata cewa; a duk sheka, ana yin asarar abincin da ya kai kimanin tan miliyan 38 a ƙasar. A cewar ta EU, hakan ya nuna irin illolin da ke afkwa a ƙasar na ƙarancin abinci, wanda kuma hakan ke jawo gurɓatar muhalli.
Jakadan EU a Nijeriya, Zissimos Ɓergos ya sanar da haka a Abuja, a taron zagayowar ranar magance asarar abinci ta duniya da aka saba gudanarwa a duk ranar 30 ga watan Maris na kowace shekara.
- Sarki Sanusi II Ya Tuɓe Rawanin Mai Unguwar Rikadawa Kan Badaƙalar Fili
- Tawagar Masanan Dakile Yaduwar Cututtuka Ta Sin Ta Isa DR Congo
- Uba Sani Ya Sanya Hannu Kan Sabbin Dokoki A Bangaren Sauya Fannin Wuta, Noma, Da Muhalli
- Han Zheng Zai Halarci Taron SPIEF Karo Na 29 A Rasha Tare Da Gudanar Da Ziyarar Aiki A Belarus
- ’Yan Majalisar Tarayya 3 Sun Fice Daga APC Zuwa ADC da PRP
Zissimos ya jaddada muhimmancin rage wulaƙantar da abinci a wannan ƙasa, inda ya yi nuni da cewa; batun ba wai kawai na wulaƙantar da abinci ba ne, wata dama ce da ake yin asararta na yaƙi da yunwa a ƙasar da kuma yadda matsalar ke zama barazana ga sararin samaniya.
Ya ƙara da cewa, a ɗaukacin faɗin duniya a 2022, aƙalla an wulaƙanta abincin da ya kai tan biliyan ɗaya.
“Asarar abinci da kuma wulaƙantar da shi, ya kasance wata babbar barazana ga gurɓatar muhalli, wanda hakan ya ruɓanya har sau biyar na irin hayaƙin da ke fita daga fannin sufurin jiragen sama,” a cewarsa.
Sai dai, ya nuna gamsuwarsa, kan kafa wani kwamiti na ƙasa da zai sanya ido kan manhajar da aka samar ta CER da kuma wani shiri da aka ƙirƙiro da shi da nufin daƙile zubar da robobin cin abinci a ɗaukacin faɗin ƙasar nan.
Ya ƙara da cewa, a nata ɓangaren EU, ta samar da wasu tsaruka uku da za su taimaka wa ƙasar nan, wajen magance matsalar ta wulaƙantar da abinci.
Shi kuwa, Philbert Johnson, a nasa jawabin a wajen taron, darakta kuma wakilin sashen yarjejeniyar sauyin yanayi a majalisar ɗinkin duniya, wato UNIDO, ya bayyana cewa; wulaƙantar da abinci, musamman yadda ake zubar da shi barkatai, na shafar lafiyar Ɗan’adam.
Ƙungiyar ta EU da UNIDO da kuma ɓangaren gwamnatin ƙasar, sun buƙaci da a ɗauki matakan gaggawa, domin magance wannan matsala.















Discussion about this post