Ƙungiyar Tarayyar Turai (EU), ta bayyana cewa; Nijeriya ce kan gaba a nahiyar Afirka, wajen wulaƙantar da abinci, inda ta ƙiyasata cewa; a duk sheka, ana yin asarar abincin da ya kai kimanin tan miliyan 38 a ƙasar. A cewar ta EU, hakan ya nuna irin illolin da ke afkwa a ƙasar na ƙarancin abinci, wanda kuma hakan ke jawo gurɓatar muhalli.
Jakadan EU a Nijeriya, Zissimos Ɓergos ya sanar da haka a Abuja, a taron zagayowar ranar magance asarar abinci ta duniya da aka saba gudanarwa a duk ranar 30 ga watan Maris na kowace shekara.
- Li Qiang Ya Halarci Bikin Bude Dandalin Tattalin Arzikin Duniya Na Davos Na Shekarar 2026
- Xi Ya Yi Kiran Daukar Matakan Zamanantar Da Aikin Gona Da Yankunan Karkara
- Atiku Ya Soki Tsare El-Rufai, Ya Ce Sharuɗan Belinsa Sun Yi Tsauri
- Trump Ne Zai Jagoranci Bayar Da Kofin Duniya A Wasan Ƙarshe – Infantino
- ’Yansanda Sun Kama Wani Mutum da Harsasai 174 A Nasarawa
Zissimos ya jaddada muhimmancin rage wulaƙantar da abinci a wannan ƙasa, inda ya yi nuni da cewa; batun ba wai kawai na wulaƙantar da abinci ba ne, wata dama ce da ake yin asararta na yaƙi da yunwa a ƙasar da kuma yadda matsalar ke zama barazana ga sararin samaniya.
Ya ƙara da cewa, a ɗaukacin faɗin duniya a 2022, aƙalla an wulaƙanta abincin da ya kai tan biliyan ɗaya.
“Asarar abinci da kuma wulaƙantar da shi, ya kasance wata babbar barazana ga gurɓatar muhalli, wanda hakan ya ruɓanya har sau biyar na irin hayaƙin da ke fita daga fannin sufurin jiragen sama,” a cewarsa.
Sai dai, ya nuna gamsuwarsa, kan kafa wani kwamiti na ƙasa da zai sanya ido kan manhajar da aka samar ta CER da kuma wani shiri da aka ƙirƙiro da shi da nufin daƙile zubar da robobin cin abinci a ɗaukacin faɗin ƙasar nan.
Ya ƙara da cewa, a nata ɓangaren EU, ta samar da wasu tsaruka uku da za su taimaka wa ƙasar nan, wajen magance matsalar ta wulaƙantar da abinci.
Shi kuwa, Philbert Johnson, a nasa jawabin a wajen taron, darakta kuma wakilin sashen yarjejeniyar sauyin yanayi a majalisar ɗinkin duniya, wato UNIDO, ya bayyana cewa; wulaƙantar da abinci, musamman yadda ake zubar da shi barkatai, na shafar lafiyar Ɗan’adam.
Ƙungiyar ta EU da UNIDO da kuma ɓangaren gwamnatin ƙasar, sun buƙaci da a ɗauki matakan gaggawa, domin magance wannan matsala.














