Ɗaliban sashin Injiniyarin na Jami’ar Jihar Nasarawa da ke harabar Gudi, waɗanda wasu ‘yan bindiga suka sace, sun shaki iskar ‘yanci.
Rundunar ‘Yansandan Jihar Nasarawa ta bayyana hakan a ranar Talata, inda ta tabbatar da cewa waɗanda aka ceto na samun kulawar lafiya da kuma tallafin ƙwararrun masu kula da lafiyar kwakwalwa bayan halin da suka shiga.
Da yake sanar da hakan, jami’in hulɗa da jama’a na rundunar ‘yansanda, SP Ramhan Nansel, ya ce an kama mutane biyu da ake zargi da hannu a satar ɗaliban ta hanyar amfani da bayanan sirri wajen gudanar da aiki.
Ya bayyana sunayen waɗanda ake zargin da Abdullahi Yeyi Haro, wanda ake zargin shi ne shugaban ƙungiyar masu garkuwa da mutane, da kuma Basiru Abdullahi, dukkansu ‘yan asalin Gudi ne.
A cewar rundunar, an samu nasarar kamen ne bayan haɗin gwiwar ayyukan tsaro da aka gudanar domin tarwatsa ƙungiyar masu aikata laifin da ke da hannu a satar.
Kwamishinan ‘Yansandan Jihar Nasarawa, CP Shetima Jauro Mohammed, ya yaba wa jami’an tsaron bisa ƙwarewa da jajircewarsu wajen tabbatar da tsaron jama’a.















Discussion about this post