ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Wednesday, July 15, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

2027: ADC Na Duba Yiwuwar Fitar Da Dan Takarar Shugaban Kasa Ta Hanyar Yarjejeniya — Kakakin Jam’iyya

by Yusuf Shuaibu and Sulaiman
3 months ago
ADC

Jam’iyyar ADC ta ce tana la’akari da karbar hanyar da kowa zai amince da ita wajen zaben dan takararta na shugaban kasa a 2027.

Sakataren yada labarai na jam’iyyar, Bolaji Abdullahi, ya bayyana hakan a wani shiri na gidan talabijin na Arise TB, a ranar Asabar.

  • Tsohon Ɗan Takarar Gwamnan PDP A Kaduna, Ashiru, Zai Koma ADC A Ranar Lahadi
  • CBN Ya Ɗage Tsarin Dijital, Zai Biya Mahajjata Kuɗin Guzurinsu A Hannu

Ya ce jam’iyyar na da zabin yin zaben fitar da gwai kai tsaye ko bin hanyar yarjejeniya wajen zaben wanda zai tsaya mata takara a zaben shugaban kasa. Ya kara da cewa zabukan fid da gwani ba su kasance ‘a tebur’ ba bisa ga dokar zabe da aka gyara.

ADVERTISEMENT

A cewarsa, zabin yin yarjejeniya ita ce kadai hanyar zabin da aka fi so, saboda tana da sauki wajen kashe kudade.

“Muna kokarin gwadawa gwargwadon ikomu ta rungumar hanyar yarjejeiya, saboda wannan shi ne mafi karancin kudi a garemu. A bangarenmu kuma, mafi kyawun yanayi shi ne samun damar tsara yarjejeiyar, kuma wannan ne abin da muke aiki a kai,” in ji shi.

LABARAI MASU NASABA

Amurka Ta Yi Alƙawarin Sa Ido Sosai A Zaɓen Nijeriya Na 2027

Sautin Muryar Da Aka Fallasa Kan El-Rufai Ya Haifar Da Zazzafar Muhawara

Abdullahi ya kuma soki jam’iyyar APC mai mulki, yana jayayya cewa hadin kan jam’iyyar tana da alaka da shugabancinta a yanzu.

“Idan ka cire iko daga APC, APC ba komai ba ne a zahiri. Na san jam’iyyar sosai.

“Bayan Bola Tinubu, za su rushe cikin sauri, har ma da kansu za su yi mamaki. Shi ne kadai mai rike jam’iyyar gaba daya,” in ji shi.

Ya bayyana APC a matsayin mota ta musamman da aka kirkira don kawo shugabancin, Marigayi Muhammadu Buhari da Tinubu, yana kara da cewa jam’iyyar ta cika wannan manufa gaba daya.

Mai magana da yawun ADC ya kara zargin cewa jam’iyyar mai mulki tana nuna alamun damuwa gabanin zaben da ke tafe.

“A kowace sahihin zabe mai cike da adalci a Nijeriya a yau, babu yadda APC za ta ci zabe.

“Me ya sa jam’iyya mai gwamnonin 31 da kusan kashi 90 cikin dari na ‘yan majalisar kasa ke ci gaba da firgita? Me ya sa har yanzu suke kokarin Sanya wa sauran jam’iyyu masu adawa cikin tashin hankali?

“Ya kamata su kasance suna shirin nasarar Tinubu, la’akari da iko mai yawa da suke da shi. Amma ba su kwantar da hankalinsu ba saboda sun san a zaben da ya kasance mai kyauta kuma mai adalci, ba za su iya samun nasara ba. ‘Yan Nijeriya sun gaji da su,” in ji shi.

Wannan mataki ya zo ne yayin da ADC, wacce ta sanya kanta a matsayin babban jam’iyyar adawa da ta hada fitattun ‘yan siyasa.

Cikin masu neman tikiti takarar shugaba kasa a zaben 2027, akwai tsohon mataimakin shugaban kasa, Atiku Abubakar da tsohon gwamnan Anambra, Peter Obi, da tsohon ministan sufuri, Rotimi Amaechi, da sauransu.

Sai dai kuma babu sanarwa a hukumance game da takamaiman ‘yan takara.

TATTALIN ARZIKI

ADC
Yusuf Shuaibu
+ posts Bio
  • Yusuf Shuaibu
    https://hausa.leadership.ng/author/yusuf-shuaibu/
    Amurka Ta Yi Alƙawarin Sa Ido Sosai A Zaɓen Nijeriya Na 2027
  • Yusuf Shuaibu
    https://hausa.leadership.ng/author/yusuf-shuaibu/
    Sautin Muryar Da Aka Fallasa Kan El-Rufai Ya Haifar Da Zazzafar Muhawara
  • Yusuf Shuaibu
    https://hausa.leadership.ng/author/yusuf-shuaibu/
    Ci-ma-zaunen Ƴan Siyasa Ne Ke Tunanin Yin Maguɗi A Zaɓen 2027 – Makarfi
  • Yusuf Shuaibu
    https://hausa.leadership.ng/author/yusuf-shuaibu/
    An Samu Ruɗani Kan Rashin Bayyana Jerin Ƴan Takarar Jam’iyyun Siyasa Na Zaɓen 2027
ADC
Sulaiman
+ posts Bio
  • Sulaiman
    Majalisa Ta Ba da Tallafin ₦50m Ga Iyalan Malamai Da Jami’an Tsaro Da Aka Kashe A Aikin Ceto A Oyo
  • Sulaiman
    Xi Ya Bukaci A Mayar Da Hankali Kan Bukatun Jama’a Yayin Rangadin Da Ya Yi A Shanghai
  • Sulaiman
    Lalata Da Ƙaramar Yarinya: Kotu Ta Yanke Wa Tsoho Mai Shekara 75 Hukuncin Ɗaurin Shekara 10 A Ribas
  • Sulaiman
    Ci Gaban Fasaha Na Hidimtawa Jama’a Cikin Kowane Yanayi A Kasar Sin

MASU ALAKA

Amurka Ta Yi Alƙawarin Sa Ido Sosai A Zaɓen Nijeriya Na 2027
Tambarin Dimokuradiyya

Amurka Ta Yi Alƙawarin Sa Ido Sosai A Zaɓen Nijeriya Na 2027

July 11, 2026
Sautin Muryar Da Aka Fallasa Kan El-Rufai Ya Haifar Da Zazzafar Muhawara
Tambarin Dimokuradiyya

Sautin Muryar Da Aka Fallasa Kan El-Rufai Ya Haifar Da Zazzafar Muhawara

July 11, 2026
makarfi
Tambarin Dimokuradiyya

Ci-ma-zaunen Ƴan Siyasa Ne Ke Tunanin Yin Maguɗi A Zaɓen 2027 – Makarfi

June 26, 2026
Next Post
Tallafin Abinci Na Gaggawa Daga Sin Ya Isa Togo

Tallafin Abinci Na Gaggawa Daga Sin Ya Isa Togo

LABARAI MASU NASABA

Majalisa Ta Ba da Tallafin ₦50m Ga Iyalan Malamai Da Jami’an Tsaro Da Aka Kashe A Aikin Ceto A Oyo

Majalisa Ta Ba da Tallafin ₦50m Ga Iyalan Malamai Da Jami’an Tsaro Da Aka Kashe A Aikin Ceto A Oyo

July 15, 2026
Xi Ya Bukaci A Mayar Da Hankali Kan Bukatun Jama’a Yayin Rangadin Da Ya Yi A Shanghai

Xi Ya Bukaci A Mayar Da Hankali Kan Bukatun Jama’a Yayin Rangadin Da Ya Yi A Shanghai

July 15, 2026
Katsina: Kotu Ta Yanke Wa Hauwa’u Hukuncin Kisa Ta Hanyar Rataya Kan Taimaka Wa ’Yan Bindiga

Lalata Da Ƙaramar Yarinya: Kotu Ta Yanke Wa Tsoho Mai Shekara 75 Hukuncin Ɗaurin Shekara 10 A Ribas

July 15, 2026
Ci Gaban Fasaha Na Hidimtawa Jama’a Cikin Kowane Yanayi A Kasar Sin

Ci Gaban Fasaha Na Hidimtawa Jama’a Cikin Kowane Yanayi A Kasar Sin

July 15, 2026
‘Yan Bindiga Sun Sace Shugaban Makaranta, Jami’in NECO Da Ɗalibai A Kogi

‘Yan Bindiga Sun Sace Shugaban Makaranta, Jami’in NECO Da Ɗalibai A Kogi

July 15, 2026
Tsohon Ɗan Takarar Gwamnan SDP A Gombe Ya Koma PDP, Ya Mara Wa Pantami Baya

Tsohon Ɗan Takarar Gwamnan SDP A Gombe Ya Koma PDP, Ya Mara Wa Pantami Baya

July 15, 2026
Zazzaɓin Lassa: Mutum 31 Sun Kamu Da Cutar A Jihohi 4, Waɗanda Suka Rasu Sun Kai 221

Zazzaɓin Lassa: Mutum 31 Sun Kamu Da Cutar A Jihohi 4, Waɗanda Suka Rasu Sun Kai 221

July 15, 2026
‘Yansanda Sun Kama Shugaban PFIPC, Adeyemi

‘Yansanda Sun Kama Shugaban PFIPC, Adeyemi

July 15, 2026
‘Yansanda Sun Kama Ɗan Bindiga Da Kuɗin Fansa Naira Miliyan 5 A Delta

‘Yansanda Sun Kama Wani Kan Zargin Yi Wa ‘Yan Bindiga Safarar Makamai A Kano

July 15, 2026
Sakamakon Binciken Masana Na Kasar Da Ake Fitarwa Kyauta Yana Kara Jan Hankalin Duniya

Sakamakon Binciken Masana Na Kasar Da Ake Fitarwa Kyauta Yana Kara Jan Hankalin Duniya

July 14, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.