Sanata Orji Kalu ya ce Shugaba Bola Ahmed Tinubu har yanzu shi ne ɗan takarar da ya fi ƙarfi a fafatawar da za a yi a zaɓen shugaban ƙasa na 2027, duk da ƙalubalen tattalin arziƙin da Nijeriya ke fuskanta.
Da yake magana a shirin siyasa na gidan talabijin na Channels, Kalu ya ce sauye-sauyen tattalin arziƙi da gwamnatin Tinubu ta aiwatar sun fara daidaita tattalin arziƙin ƙasar.
Ya ce canjin kuɗi, farashin man fetur da kuma zuba jari daga ƙasashen waje na ci gaba da inganta, amma ya amince cewa har yanzu ‘yan Nijeriya na fama da tsadar rayuwa.
Kalu ya danganta matsalar tattalin arziƙi da matsalolin da duniya ke fuskanta da kuma rashin tsaro.
Ya ce hare-haren ‘yan bindiga da masu tayar da ƙayar baya sun hana manoma da dama komawa gonakinsu, lamarin da ya jawo hauhawar farashin kayan abinci.
Ya kuma yi watsi da zargin cewa Shugaba Tinubu ba shi da kyakkyawar alaƙa da Cocin Katolika.
A cewarsa, cocin na da damar bayyana ra’ayinta kan al’amuran ƙasa, kuma shugaban ƙasa na girmama shugabanninta.
Dangane da zaɓen 2027, Kalu ya ce jam’iyyar APC na da tabbacin za ta ci gaba da zama a kan mulki.
Ya bai wa Tinubu maki 65 cikin 100 kan yadda yake tafiyar da mulki, yana mai cewa gwamnati ta samu nasarori a fannonin gine-ginen more rayuwa, tsaro da sauye-sauyen tattalin arziƙi, sai dai ba ta yi isasshen bayani ga jama’a kan waɗannan nasarori ba.
Ya kuma ce kundin tsarin mulkin Nijeriya ya bai wa ‘yan ƙasa damar yin zanga-zangar lumana, amma ya gargaɗi mutane da su yi taka-tsantsan wajen yaɗa labaran ƙarya da bayanan da ke yawo a kafafen sada zumunta.














