Wasu fusatattun matasa sun ƙone motar sintirin Hukumar Kula da Zirga-zirgar Ababen Hawa ta Jihar Kano (KAROTA) a ranar Laraba bayan wani hatsarin mota da ya faru a Kwanar Dawaki.
Mataimakin Manajan Daraktan KAROTA, Auwal Lawan Shu’aibu Aranposu, ya ce hatsarin ya faru ne bayan wata tirela ta yi karo da wata mota ƙirar Sharon mai ɗaukar fasinjoji.
Bayan haka jami’an KAROTA suka isa wajen domin kama direban tirelar.
Ya ce wasu matasa sun kai wa jami’an hari tare da ƙone motar sintirinsu.
Aranposu ya musanta zargin cewa jami’an KAROTA ne suka haddasa hatsarin.
Ya ce jami’an sun isa wajen ne bayan hatsarin ya riga ya faru domin gudanar da aikinsu.
Ya yi Allah-wadai da harin da aka kai wa jami’an da kuma lalata kadarorin gwamnati, sannan ya buƙaci jama’a su kwantar da hankalinsu su bar hukumomin da abin ya shafa su gudanar da bincike.
Har zuwa lokacin haɗa wannan rahoto, ba a sanar da kama kowa da hannu a lamarin ba.














