Tsohon gwamnan Jihar Kano kuma jagoran Kwankwasiyya, Rabiu Musa Kwankwaso, ya ce a shirye yake ya zama mataimakin Peter Obi a zaɓen shugaban ƙasa na 2027.
Da yake magana a gidan talabijin na Arise News a ranar Litinin, Kwankwaso ya ce Nijeriya na buƙatar nagartaccen shugabanci domin magance matsalar tsaro, matsalar tattalin arzikƙi da rashin kyakkyawan shugabanci.
Ya ce shugabannin haɗakar sun amince cewa mulki ya kamata ya ci gaba da kasancewa a Kudu na wani wa’adi kafin ya dawo Arewa, yana mai cewa hakan zai taimaka wajen ƙarfafa haɗin kai kafin zaɓen 2027.
Da aka tambaye shi ko zai amince ya zama mataimakin Obi, Kwankwaso ya ce: “Eh. Idan jam’iyya ta yanke shawarar na zama mataimakin kowane ɗan takara daga Kudu, zan yi farin cikin yin aiki tare da shi.”
Kwankwaso ya bayyana Obi a matsayin ɗaya daga cikin ‘yan siyasar da za su iya bai wa Nijeriya irin shugabancin da take buƙata.
Ya kuma ce matasa da dama a Nijeriya yanzu sun fi mayar da hankali kan nagartaccen shugabanci sama da siyasar ƙabilanci ko addini saboda matsalolin tsaro, rashin aikin yi da wahalar rayuwa.
Tsohon gwamnan ya musanta cewa haɗakar Obi da Kwankwaso za ta rage ƙarfin adawa a Arewa, yana mai cewa ‘yan Nijeriya sun fi damuwa da halin da ƙasar ke ciki sama da siyasar yanki.
Kwankwaso ya kuma soki jam’iyyar APC, inda ya bayyana cewa shugabanninta sun yi buris da halin da talakawa ke ciki.















Discussion about this post