ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Saturday, July 25, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

2027: Gwamnan Bauchi Na Shirin Komawa ADC, Bayan Kasa Shawo Kan Rikicin PDP 

by Khalid Idris Doya and Sulaiman
4 months ago
Bauchi

Gwamnan Jihar Bauchi kuma Shugaban Ƙungiyar Gwamnonin PDP, Sanata Bala Mohammed, na duba yiwuwar komawa jam’iyyar African Democratic Congress (ADC).

 

Gwamnan ya nuna haka ne a ranar Talata lokacin da gwamnan ya karɓi bakwancin tawagar ADC ƙarƙashin jagorancin tsohon Sakataren Gwamnatin Tarayya (SGF), Babachir Lawal, a Ramat House da ke Bauchi.

ADVERTISEMENT
  • Kotu Ta Ɗage Sauraron Neman Beli Na El-Rufai Zuwa Gobe Laraba
  • Jakadan Sin a Najeriya Ya Halarci Bikin Kaddamar Da Aikin Cibiyar Samar Da Wutar Lantarki Ta Karfin Ruwa A Najeriya

Wannan matakin dai na zuwa ne bayan da rikici cikin gida suka mamaye jam’iyyar PDP lamarin da ya har ya sanya a kwanakin baya aka yi ta yada cewa gwamnan zan koma APC, lamarin bai yiyu ba inda yanzu kuma alƙiblar ta koma kan ADC. Hakan dai bai rasa nasaba da rikicin tsakanin ɓangaren Nyesom Wike da su ta Bala Muhammad.

 

LABARAI MASU NASABA

Kyamar Baki: Shettima Ya Ja Kunnen Gwamnatin Afirka Ta Kudu

Yadda Kasar Sin Ta Samar Da Ci Gaba Na Bai Daya

Da ya ke magana a yayin taron, Gwamna Muhammad ya ce tawagarsu ta yi zurfin tunani da tuntubar bangarori daban ciki har da APC, amma sun fahimci cewa ba za su iya ci gaba da zama a inda ba a maraba da su ba. Don haka ne suka maida hankali wajen duba yiyuwar komawa cikin jam’iyyar ADC domin ci gaba da gudanar da harkokin siyasarsu a ciki.

 

Gwamnan ya bayyana ADC a matsayin jam’iyya mai inganci kuma mai jan hankali, yana mai cewa tana ƙara samun karɓuwa daga masu ruwa da tsaki da suke tattaunawa da ita, tare da al’ummar ƙasa.

 

Sai dai ya bayyana cewa har yanzu tattaunawa na ci gaba kuma ba a kai ga cimma matsaya ta ƙarshe ba.

 

“Ya zuwa yanzu, ADC ita ce zaɓinmu na farko, amma ba mu kammala tattaunawa ta yadda za ta tabbatar da cikakken haɗin kai da masu ruwa da tsaki ba. Muna son kauce wa yin kuskure,” don haka ya nuna cewa dole su ƙara zurfafa tuntuɓa a tsakanin sauran masu ruwa da tsaki da ‘yan tawagarsu domin tafiya tare.

 

Gwamna Muhammad ya bayyana cewa a matsayinsa na jagora a jihar Bauchi da ma ƙasa dole ne ya nemi jin sauran bangarori domin tafiya tare don neman wa jama’a mafita.

 

“Dole ne mu yi komai a hankali. Muna buƙatar daidaita muradun masu ruwa da tsaki a matakan ƙasa da jiha, shi ya sa tattaunawa ta ɗauki lokaci,” in ji shi.

 

Ya ƙara da cewa tawagarsa a shirye take ta yi haɗaka da ADC, duk da cewa har yanzu ana ci gaba da tattaunawa tare da wasu jam’iyyun siyasa, domin duba wacce ta fi dacewa da tawagar tasu.

 

“Mun nuna shirye-shiryenmu na shiga tare da su bisa yarjejeniya. Ko da yake ba a kammala tattaunawa gaba ɗaya ba, ADC ce har yanzu zaɓinmu a halin yanzu” ya bayyana.

 

Gwamnan ya gode wa shugabannin ADC bisa gayyatar da suka miƙa masa, yana mai cewa hakan ya zo a kan lokaci duba da ƙalubalen siyasa da ake fuskanta.

 

“Idan kana fuskantar ƙalubalen siyasa masu tsanani kuma wani ya miƙa maka hannu na haɗin gwiwa, ya dace ka nuna godiya. Amma har yanzu muna mai da hankali ne kan lashe zaɓe, wanda a ƙarshe ke faruwa a rumfunan zaɓe,” in ji shi.

 

Ya kuma jaddada buƙatar dabarun neman mafita a siyasa da haɗin kai, yana mai cewa halin da ake ciki a jam’iyyar PDP a halin yanzu ba yanayi ne da zai haifar da sakamakon mai kyau ba.

 

“Don haka dole ne mu fuskanci gaskiyar halin da ake ciki mu kuma duba wannan damar da ADC ta bayar. Ba za mu yi wasa da wannan damar ba,” ya ƙara da cewa.

 

Gwamna Mohammed ya kuma bayyana cewa an kafa kwamitoci biyu, ɗaya a matakin ƙasa a Abuja, ɗaya kuma a Bauchi domin nazarin alkiblar siyasarsu da kuma tunƙarar yadda za a yi zaɓukan da suke tafe a cikin jam’iyyu daban-daban.

 

“Za ku ji cikakken matsayarmu a ranar Alhamis bayan taronmu a Abuja,” in ji shi.

 

Tun da farko, jagoran tawagar ADC, Babachir David Lawal, ya ce ziyarar tasu ta zo ne bisa umarnin Shugaban Jam’iyyar na ƙasa, David Mark, domin gayyatar Gwamna Bala Mohammed ya shiga ADC gabanin zaɓen 2027.

 

Ya bayyana gwamnan a matsayin jajirtaccen ɗan siyasa mai tasiri, yana mai cewa shigarsa jam’iyyar zai ƙara ƙarfinta da damar lashe zaɓe.

 

Lawal ya kuma jaddada muhimmancin haɗin kan jam’iyyun adawa, yana mai gargadin cewa rashin haɗin kan domin tunƙarar kalubalen da suke jibge iya haifar da barazana ga dimokuraɗiyyar Nijeriya.

 

Taron na zuwa ne kwanaki kaɗan bayan Gwamna Bala Mohammed ya kira taron masu ruwa da tsaki na PDP a Bauchi, domin magance saɓanin cikin gida da ƙarfafa haɗin kan jam’iyyar.

Bauchi
Khalid Idris Doya
+ posts Bio
  • Khalid Idris Doya
    https://hausa.leadership.ng/author/khalid-idris-doya/
    ‘Yansanda Sun Kama Wanda Ake Zargi Da Harbe Mai Unguwa Har Lahira A Bauchi
  • Khalid Idris Doya
    https://hausa.leadership.ng/author/khalid-idris-doya/
    Ba Mu Sayar Wa Dangote Da Reshen Jami’ar SAZU Na Yuli Ba-Gwamnatin Bauchi
  • Khalid Idris Doya
    https://hausa.leadership.ng/author/khalid-idris-doya/
    Gwamna Bala Ya Rushe Kwamitin Gudanarwar Wikki Tourists Bayan Rashin Nasararta A Gasar NPFL
  • Khalid Idris Doya
    https://hausa.leadership.ng/author/khalid-idris-doya/
    M.A. Abubakar Ya Zaɓi Farouk Mustapha A Matsayin Mataimakinsa
Bauchi
Sulaiman
+ posts Bio
  • Sulaiman
    An Karrama Masana Ilimin Lissafi Na Kasar Sin Da Lambobin Yabo Na Fields Medal
  • Sulaiman
    Ta Da Zaune Tsaye Da Philippines Ta Yi A Teku Ba Zai Lalata Dangantakar Hadin Gwiwar Sin Da ASEAN Ba
  • Sulaiman
    An Zartas Da Sanarwar Chengdu A Taron Ministocin Kungiyar APEC Kan Harkar Raya Fasahohin Dijital Da AI
  • Sulaiman
    Sin Ta Kara Kamfanoni 14 Na Tarayyar Turai Cikin Jerin Wadanda Aka Hana Fitar Masu Da Kaya

MASU ALAKA

Kashim Shettima Ya Mayar Da Martani Kan Tsadar Rayuwa
Labarai

Kyamar Baki: Shettima Ya Ja Kunnen Gwamnatin Afirka Ta Kudu

July 24, 2026
Yadda Kasar Sin Ta Samar Da Ci Gaba Na Bai Daya
Ra'ayi Riga

Yadda Kasar Sin Ta Samar Da Ci Gaba Na Bai Daya

July 24, 2026
NLC Ta Yi Barazanar Daukar Matakin Yajin Aiki Kan Albashi Mafi Karanci
Rahotonni

NLC Ta Yi Barazanar Daukar Matakin Yajin Aiki Kan Albashi Mafi Karanci

July 24, 2026
Next Post
Sin Da Pakistan Sun Ba Shawarwari Biyar Kan Maido Da Zaman Lafiya A Yankin Gulf Da Gabas Ta Tsakiya

Sin Da Pakistan Sun Ba Shawarwari Biyar Kan Maido Da Zaman Lafiya A Yankin Gulf Da Gabas Ta Tsakiya

LABARAI MASU NASABA

An Karrama Masana Ilimin Lissafi Na Kasar Sin Da Lambobin Yabo Na Fields Medal

An Karrama Masana Ilimin Lissafi Na Kasar Sin Da Lambobin Yabo Na Fields Medal

July 24, 2026
Ta Da Zaune Tsaye Da Philippines Ta Yi A Teku Ba Zai Lalata Dangantakar Hadin Gwiwar Sin Da ASEAN Ba

Ta Da Zaune Tsaye Da Philippines Ta Yi A Teku Ba Zai Lalata Dangantakar Hadin Gwiwar Sin Da ASEAN Ba

July 24, 2026
Jadawalin INEC:Kotun Daukaka Kara Ta Kassara Fatan Jam’iyyu Da ‘Yan Siyasa

Jadawalin INEC:Kotun Daukaka Kara Ta Kassara Fatan Jam’iyyu Da ‘Yan Siyasa

July 24, 2026
An Zartas Da Sanarwar Chengdu A Taron Ministocin Kungiyar APEC Kan Harkar Raya Fasahohin Dijital Da AI

An Zartas Da Sanarwar Chengdu A Taron Ministocin Kungiyar APEC Kan Harkar Raya Fasahohin Dijital Da AI

July 24, 2026
NNPP Za Ta Kwace Mulki A Jihar Imo – Kwankwaso

Jam’iyyar NDC Ta Shirya Tsaf Domin Kafa Gwamnati A 2027 —Kwankwaso

July 24, 2026
Sin Ta Kara Kamfanoni 14 Na Tarayyar Turai Cikin Jerin Wadanda Aka Hana Fitar Masu Da Kaya

Sin Ta Kara Kamfanoni 14 Na Tarayyar Turai Cikin Jerin Wadanda Aka Hana Fitar Masu Da Kaya

July 24, 2026
Kashim Shettima Ya Mayar Da Martani Kan Tsadar Rayuwa

Kyamar Baki: Shettima Ya Ja Kunnen Gwamnatin Afirka Ta Kudu

July 24, 2026
Yadda Kasar Sin Ta Samar Da Ci Gaba Na Bai Daya

Yadda Kasar Sin Ta Samar Da Ci Gaba Na Bai Daya

July 24, 2026
Hatsin Da Kasar Sin Ta Girbe Da Lokacin Zafin Bana Ya Zarce Tan Miliyan 150

Hatsin Da Kasar Sin Ta Girbe Da Lokacin Zafin Bana Ya Zarce Tan Miliyan 150

July 24, 2026
Wani Dalilin Da Ya Sa Al’Ummar Afirka Ke Kaunar Kasar Sin Shi Ne Yadda Take Kokarin Zuba Musu Jari

Wani Dalilin Da Ya Sa Al’Ummar Afirka Ke Kaunar Kasar Sin Shi Ne Yadda Take Kokarin Zuba Musu Jari

July 24, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.