ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Saturday, July 4, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

2027: Gwamnan Bauchi Na Shirin Komawa ADC, Bayan Kasa Shawo Kan Rikicin PDP 

by Khalid Idris Doya and Sulaiman
3 months ago
Bauchi

Gwamnan Jihar Bauchi kuma Shugaban Ƙungiyar Gwamnonin PDP, Sanata Bala Mohammed, na duba yiwuwar komawa jam’iyyar African Democratic Congress (ADC).

 

Gwamnan ya nuna haka ne a ranar Talata lokacin da gwamnan ya karɓi bakwancin tawagar ADC ƙarƙashin jagorancin tsohon Sakataren Gwamnatin Tarayya (SGF), Babachir Lawal, a Ramat House da ke Bauchi.

ADVERTISEMENT
  • Kotu Ta Ɗage Sauraron Neman Beli Na El-Rufai Zuwa Gobe Laraba
  • Jakadan Sin a Najeriya Ya Halarci Bikin Kaddamar Da Aikin Cibiyar Samar Da Wutar Lantarki Ta Karfin Ruwa A Najeriya

Wannan matakin dai na zuwa ne bayan da rikici cikin gida suka mamaye jam’iyyar PDP lamarin da ya har ya sanya a kwanakin baya aka yi ta yada cewa gwamnan zan koma APC, lamarin bai yiyu ba inda yanzu kuma alƙiblar ta koma kan ADC. Hakan dai bai rasa nasaba da rikicin tsakanin ɓangaren Nyesom Wike da su ta Bala Muhammad.

 

LABARAI MASU NASABA

CAF Ta Gayyaci Ƙasashen Afirka Su Nemi Ɗaukar Nauyin Gasar AFCON Ta 2028, 2032 da 2036

Gwamnatin Zamfara Ta Jinjina Wa Shugaban NAHCON Kan Nasarar Aikin Hajjin 2026

Da ya ke magana a yayin taron, Gwamna Muhammad ya ce tawagarsu ta yi zurfin tunani da tuntubar bangarori daban ciki har da APC, amma sun fahimci cewa ba za su iya ci gaba da zama a inda ba a maraba da su ba. Don haka ne suka maida hankali wajen duba yiyuwar komawa cikin jam’iyyar ADC domin ci gaba da gudanar da harkokin siyasarsu a ciki.

 

Gwamnan ya bayyana ADC a matsayin jam’iyya mai inganci kuma mai jan hankali, yana mai cewa tana ƙara samun karɓuwa daga masu ruwa da tsaki da suke tattaunawa da ita, tare da al’ummar ƙasa.

 

Sai dai ya bayyana cewa har yanzu tattaunawa na ci gaba kuma ba a kai ga cimma matsaya ta ƙarshe ba.

 

“Ya zuwa yanzu, ADC ita ce zaɓinmu na farko, amma ba mu kammala tattaunawa ta yadda za ta tabbatar da cikakken haɗin kai da masu ruwa da tsaki ba. Muna son kauce wa yin kuskure,” don haka ya nuna cewa dole su ƙara zurfafa tuntuɓa a tsakanin sauran masu ruwa da tsaki da ‘yan tawagarsu domin tafiya tare.

 

Gwamna Muhammad ya bayyana cewa a matsayinsa na jagora a jihar Bauchi da ma ƙasa dole ne ya nemi jin sauran bangarori domin tafiya tare don neman wa jama’a mafita.

 

“Dole ne mu yi komai a hankali. Muna buƙatar daidaita muradun masu ruwa da tsaki a matakan ƙasa da jiha, shi ya sa tattaunawa ta ɗauki lokaci,” in ji shi.

 

Ya ƙara da cewa tawagarsa a shirye take ta yi haɗaka da ADC, duk da cewa har yanzu ana ci gaba da tattaunawa tare da wasu jam’iyyun siyasa, domin duba wacce ta fi dacewa da tawagar tasu.

 

“Mun nuna shirye-shiryenmu na shiga tare da su bisa yarjejeniya. Ko da yake ba a kammala tattaunawa gaba ɗaya ba, ADC ce har yanzu zaɓinmu a halin yanzu” ya bayyana.

 

Gwamnan ya gode wa shugabannin ADC bisa gayyatar da suka miƙa masa, yana mai cewa hakan ya zo a kan lokaci duba da ƙalubalen siyasa da ake fuskanta.

 

“Idan kana fuskantar ƙalubalen siyasa masu tsanani kuma wani ya miƙa maka hannu na haɗin gwiwa, ya dace ka nuna godiya. Amma har yanzu muna mai da hankali ne kan lashe zaɓe, wanda a ƙarshe ke faruwa a rumfunan zaɓe,” in ji shi.

 

Ya kuma jaddada buƙatar dabarun neman mafita a siyasa da haɗin kai, yana mai cewa halin da ake ciki a jam’iyyar PDP a halin yanzu ba yanayi ne da zai haifar da sakamakon mai kyau ba.

 

“Don haka dole ne mu fuskanci gaskiyar halin da ake ciki mu kuma duba wannan damar da ADC ta bayar. Ba za mu yi wasa da wannan damar ba,” ya ƙara da cewa.

 

Gwamna Mohammed ya kuma bayyana cewa an kafa kwamitoci biyu, ɗaya a matakin ƙasa a Abuja, ɗaya kuma a Bauchi domin nazarin alkiblar siyasarsu da kuma tunƙarar yadda za a yi zaɓukan da suke tafe a cikin jam’iyyu daban-daban.

 

“Za ku ji cikakken matsayarmu a ranar Alhamis bayan taronmu a Abuja,” in ji shi.

 

Tun da farko, jagoran tawagar ADC, Babachir David Lawal, ya ce ziyarar tasu ta zo ne bisa umarnin Shugaban Jam’iyyar na ƙasa, David Mark, domin gayyatar Gwamna Bala Mohammed ya shiga ADC gabanin zaɓen 2027.

 

Ya bayyana gwamnan a matsayin jajirtaccen ɗan siyasa mai tasiri, yana mai cewa shigarsa jam’iyyar zai ƙara ƙarfinta da damar lashe zaɓe.

 

Lawal ya kuma jaddada muhimmancin haɗin kan jam’iyyun adawa, yana mai gargadin cewa rashin haɗin kan domin tunƙarar kalubalen da suke jibge iya haifar da barazana ga dimokuraɗiyyar Nijeriya.

 

Taron na zuwa ne kwanaki kaɗan bayan Gwamna Bala Mohammed ya kira taron masu ruwa da tsaki na PDP a Bauchi, domin magance saɓanin cikin gida da ƙarfafa haɗin kan jam’iyyar.

Bauchi
Khalid Idris Doya
+ posts Bio
  • Khalid Idris Doya
    https://hausa.leadership.ng/author/khalid-idris-doya/
    ATBU Ta Janye Filin Ginin Masallaci Da Ta Bai wa TIMSAN, Ta Amince Kowa Ya Yi Addininsa Yadda Ya Fahimta
  • Khalid Idris Doya
    https://hausa.leadership.ng/author/khalid-idris-doya/
    Ɗan Majalisar Dokokin Bauchi, Hon. Wanzam, Ya Rasu
  • Khalid Idris Doya
    https://hausa.leadership.ng/author/khalid-idris-doya/
    Tsohon Mataimakin Gwamnan Bauchi, Audu Sule Katagum Ya Rasu
  • Khalid Idris Doya
    https://hausa.leadership.ng/author/khalid-idris-doya/
    Kotu Ta Umarci DSS Ta Mutunta Umarninta Kan Shari’ar Filin Firo Na Bauchi
Bauchi
Sulaiman
+ posts Bio
  • Sulaiman
    Wakilin CMG Ya Zanta Da Mataimakin Shugaban Kasar Afirka Ta Kudu
  • Sulaiman
    Gwamnatin Zamfara Ta Jinjina Wa Shugaban NAHCON Kan Nasarar Aikin Hajjin 2026
  • Sulaiman
    Tawaga Ta Biyu Ta Kwararrun Kasar Sin Ta Sauka A Jamhuriyar Dimokaradiyyar Congo Domin Karfafa Yaki Da Cutar Ebola
  • Sulaiman
    Babban Dan Majalissar Dokokin Kasar Sin Ya Halarci Jana’izar Marigayi Jagoran Addini Na Iran

MASU ALAKA

CAF Ta Gayyaci Ƙasashen Afirka Su Nemi Ɗaukar Nauyin Gasar AFCON Ta 2028, 2032 da 2036
Labarai

CAF Ta Gayyaci Ƙasashen Afirka Su Nemi Ɗaukar Nauyin Gasar AFCON Ta 2028, 2032 da 2036

July 4, 2026
Gwamnatin Zamfara Ta Jinjina Wa Shugaban NAHCON Kan Nasarar Aikin Hajjin 2026
Labarai

Gwamnatin Zamfara Ta Jinjina Wa Shugaban NAHCON Kan Nasarar Aikin Hajjin 2026

July 4, 2026
Yadda Gidauniyar Ɗahiru Mangal Ta Tallafa Wa Marasa Lafiya 30,000 A Katsina
Labarai

Yadda Gidauniyar Ɗahiru Mangal Ta Tallafa Wa Marasa Lafiya 30,000 A Katsina

July 4, 2026
Next Post
Sin Da Pakistan Sun Ba Shawarwari Biyar Kan Maido Da Zaman Lafiya A Yankin Gulf Da Gabas Ta Tsakiya

Sin Da Pakistan Sun Ba Shawarwari Biyar Kan Maido Da Zaman Lafiya A Yankin Gulf Da Gabas Ta Tsakiya

LABARAI MASU NASABA

Wakilin CMG Ya Zanta Da Mataimakin Shugaban Kasar Afirka Ta Kudu

Wakilin CMG Ya Zanta Da Mataimakin Shugaban Kasar Afirka Ta Kudu

July 4, 2026
CAF Ta Gayyaci Ƙasashen Afirka Su Nemi Ɗaukar Nauyin Gasar AFCON Ta 2028, 2032 da 2036

CAF Ta Gayyaci Ƙasashen Afirka Su Nemi Ɗaukar Nauyin Gasar AFCON Ta 2028, 2032 da 2036

July 4, 2026
Gwamnatin Zamfara Ta Jinjina Wa Shugaban NAHCON Kan Nasarar Aikin Hajjin 2026

Gwamnatin Zamfara Ta Jinjina Wa Shugaban NAHCON Kan Nasarar Aikin Hajjin 2026

July 4, 2026
Tawaga Ta Biyu Ta Kwararrun Kasar Sin Ta Sauka A Jamhuriyar Dimokaradiyyar Congo Domin Karfafa Yaki Da Cutar Ebola

Tawaga Ta Biyu Ta Kwararrun Kasar Sin Ta Sauka A Jamhuriyar Dimokaradiyyar Congo Domin Karfafa Yaki Da Cutar Ebola

July 4, 2026
Yadda Gidauniyar Ɗahiru Mangal Ta Tallafa Wa Marasa Lafiya 30,000 A Katsina

Yadda Gidauniyar Ɗahiru Mangal Ta Tallafa Wa Marasa Lafiya 30,000 A Katsina

July 4, 2026
Babban Dan Majalissar Dokokin Kasar Sin Ya Halarci Jana’izar Marigayi Jagoran Addini Na Iran

Babban Dan Majalissar Dokokin Kasar Sin Ya Halarci Jana’izar Marigayi Jagoran Addini Na Iran

July 4, 2026
Akwai Barazanar Ƙaruwar Yunwa A Arewacin Nijeriya – Peter Obi

Akwai Barazanar Ƙaruwar Yunwa A Arewacin Nijeriya – Peter Obi

July 4, 2026
Pakistan Ta Kashe Mutum 36 A Hare-haren Da Ta Kai Kan Iyakarta Da Afghanistan

Pakistan Ta Kashe Mutum 36 A Hare-haren Da Ta Kai Kan Iyakarta Da Afghanistan

July 4, 2026
Kwankwasiyya Ta Buƙaci A Binciki Zargin Kasafin Kuɗin PFIPC

Kwankwasiyya Ta Buƙaci A Binciki Zargin Kasafin Kuɗin PFIPC

July 4, 2026
Matsalar Tsaro: Gwamnatin Tarayya Ta Nemi Taimakon Ƙasashen Waje

Gwamnatin Tarayya Ta Bayyana Dalilanta Na Sake Fasalin Hukumar NYSC

July 4, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.