Jam’iyyar PDP ƙarƙashin tsagin Nyesom Wike da Abdurrahman Mohammed ya ayyana Sandy Onor a matsayin ɗan takarar shugaban ƙasa na jam’iyyar a zaɓen 2027.
An sanar da hakan ne bayan gudanar da taron masalaha da tattaunawa da mambobin jam’iyyar daga jihohin ƙasar nan.
Tsohon gwamnan Jihar Benuwe, Samuel Ortom, wanda shi ne shugaban kwamitin gudanar da zaɓen fidda gwani, ya bayyana sakamakon a hedikwatar jam’iyyar da ke Wadata Plaza a Abuja.
Kwamitin ya ce an gudanar da zaɓen cikin lumana tare da samun goyon bayan mambobin jam’iyyar.
Sandy Onor ya samu tikitin takarar ne bayan ya nuna aniyarsa ta tsayawa takarar shugaban ƙasa tare da sayen fom kamar yadda dokokin jam’iyyar suka tanada.















Discussion about this post