Ɗan Majalisar Tarayya, Abdulmumin Jibrin Kofa, ya ce bai yi dana sanin mara wa Shugaba Bola Tinubu baya a kan tsohon ubangidansa na siyasa, Rabiu Kwankwaso, gabanin zaɓen 2027 ba.
Kofa, wanda ke wakiltar mazaɓar Kiru/Bebeji a Jihar Kano, ya bayyana hakan ne yayin wata hira a shirin Politics Today na gidan talabijin na Channels.
Ya ce har yanzu yana girmama Kwankwaso tare da kallonsa a matsayin jagoransa kuma wanda ya taimaka masa a siyasa, duk da bambancin siyasar da ke tsakaninsu.
A cewarsa, bai bar jam’iyyar NNPP ba, sai da aka kore shi a shekarar 2025 bisa zargin ayyukan da suka saɓa wa jam’iyyar.
Ɗan majalisar ya ce goyon bayan da yake bai wa Tinubu ba cin amana ba ne, yana mai cewa bai taɓa fitowa bainar jama’a yana cin mutuncin shugabannin da ya taɓa aiki da su ba.
Kofa ya koma jam’iyyar APC, kuma yanzu yana goyon bayan takarar Tinubu a zaɓen 2027.















Discussion about this post