Ɗan takarar mataimakin shugaban kasa na jam’iyyar NDC a babban zaben 2027, Rabiu Kwankwaso, ya yi kira ga ’yan Nijeriya da su yi watsi da siyasar da ke haifar da rarrabuwar kai, tare da neman shugabanci nagari, kwarewa da kuma rikon amana gabanin babban zaben 2027.
Kwankwaso, wanda tsohon Gwamnan Jihar Kano ne, ya yi wannan kiran ne a cikin wata sanarwa da ya wallafa a shafinsa na X a ranar Alhamis, a yayin da aka kaddamar da gangamin yaƙin neman zaben shugaban kasa na 2027.
Ya bukaci ’yan Nijeriya da su yi nazari kan halin da kasar ke ciki da kuma irin kasar da suke son bar wa al’ummar da za su zo nan gaba, yana mai jero hauhawar farashin kayan abinci, rashin aikin yi, tsadar gudanar da harkokin kasuwanci da kuma rashin tsaro a matsayin wasu daga cikin manyan kalubalen da ke addabar al’umma.
Kwankwaso ya ce, “Hauhawar farashin abinci da muhimman kayayyaki na kara jefa iyalai cikin matsananciyar wahala. Miliyoyin matasan Nijeriya na neman ayyukan yi masu ma’ana da damar inganta rayuwarsu, yayin da ‘yan kasuwa ke fama da tsadar gudanar da harkokinsu.”














