Tsohon gwamnan Jihar Kano, Rabiu Musa Kwankwaso, ya goyi bayan matakin jam’iyyar NDC na bai wa yankin Kudu tikitin takarar shugaban ƙasa na shekarar 2027.
Kwankwaso, ya bayyana haka ne yayin babban taron jam’iyyar na ƙasa da aka gudanar a Abuja a ranar Asabar, inda ya ce matakin zai ƙarfafa adalci, haɗin kai da zaman lafiya a ƙasa.
Ya ce ya dace a bar yankin Kudu ya kammala wa’adinsa, yana mai cewa tsarin ya yi daidai da manufar daidaito tsakanin yankuna.
Tun da farko dai jam’iyyar NDC ta sanar da bai wa yankin Kudu tikitin takarar shugaban ƙasa na 2027, yayin da za a bai wa Arewa damar tsayawa takara a 2031 a ƙarƙashin tsarin karɓa-karɓa.
Kwankwaso ya kuma nuna damuwa kan halin da ƙasar nan ke ciki, yana cewa matsalar tsaro, matsalar tattalin arziƙi da rashin kyakkyawan shugabanci sun jefa mutane cikin ƙunci.
A cewarsa, matsalar tsaro ta raba mutane da muhallansu, kamfanoni na barin Nijeriya, ana watsi da manyan ayyukan more rayuwa, yayin da harkar ilimi ke ƙara taɓarɓarewa.
Ya ƙara da cewa jam’iyyar NDC za ta fifita shugabanci bisa ƙwarewa maimakon bambancin ƙabila ko addini.
Kwankwaso ya kuma buƙaci ’yan Najeriya su yi rajistar katin zaɓe tare da shiga jam’iyyar NDC, yana mai bayyana jam’iyyar a matsayin wata sabuwar kafa ta kawo sauyi a ƙasa.















Discussion about this post