ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Wednesday, September 9, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

2027: Ministocin Da Ake Tsammanin Za Su Yi Murabus Kafin Wa’adin Tinubu Na Ranar 31 ga Maris

by Yusuf Shuaibu and Sulaiman
5 months ago
pate

Akalla ministoci shida a cikin majalisar zartarwar Shugaban kasa, Bola Ahmed Tinubu na iya yin murabus kafin cikar wa’adin shugaban kasa na ranar 31 ga Maris ga masu mukaman siyasa da ke neman tsayawa takara a zaben 2027.

Wani umarni daga Tinubu, wanda ofishin sakataren gwamnatin tarayya, George Akume, ya bayar, ya umarci duk jami’an da abin ya shafa su yi murabus kafin shiga zabukan fid da gwani na jam’iyyu.

An bayar da umarni ne bisa sashe na 88(1) na dokar zabe ta 2026, da kuma jadawalin da hukumar zabe mai zaman kanta ta kasa (INEC) ta fitar kan zaben fitar da gwani na jam’iyyun siyasa kafin zaben 2027.

ADVERTISEMENT

A cikin wata sanarwa da Akume ya sanya hannu kuma aka fitar daga hannun babban sakataren ofishin, Ibrahim Abubakar Kana, gwamnati ta bayyana cewa na bukatar yin murabus na dukkan masu rike da mukaman siyasa da shugaban kasa ya nada, ciki har da ministoci, masu ba da shawara na musamman, manyan mataimakan na musamman, da shugabannin hukumomin tarayya.

“Dukkan jami’an da abin ya shafa ana bukatar su mika wasikun murabus dinsu ta ofishin sakataren gwamnatin tarayya ba tare da wuce ranar 31 ga Maris, 2026 ba,” in ji sanarwar.

LABARAI MASU NASABA

2027: APC Na Fuskantar Matsin Lamba Kan Sake Fasalin Tawagar Yakin Neman Zabe

Cacar Baki Ta Kaure Tsakanin APC Da ‘Yan Adawa Kan Tallafin Gwamnatin Tarayya Ga Magidanta

Kafin wa’adin ya cika, rahotani sun yi tsammai wasu ministoci wadanda ka iya bin umarnin domin shiga cikin tsarin samun tikitin gwamna a jam’iyyar APC a jihohinsu. Wasu daga cikin ministocin kamar haka:

 

Ministan Wutar Lantarki, Bayo Adelabu

Bayo Adelabu na cikin manyan shahararrun mutane da za su iya barin majalisar zartaswar Tinubu. Ya kasance tsohon mataimakin gwamnan Babban Bankin Nijeriya (CBN), ya gina kyakkyawan matsayin siyasa a Jihar Oyo a cikin shekaru goma da suka gabata.

Adelabu ya tsaya takarar gwamnan jihar a shekarar 2019 karkashin jam’iyyar APC, sannan kuma a shekarar 2023, ya tsaya a karkashin Jam’iyyar Accord, inda ya sha kaye duka a hannun Gwamna Seyi Makinde. Burinsa na sake neman takara a 2027 ana ganin shi a matsayin ci gaba da dogon aikin siyasa da yake da shi a jihar.

An ruwaito cewa Adelabu ya bayyana a niyarsa a watan Oktoba 2025, cewa shi ne zai zama gwamnan Jihar Oyo a 2027.

A cikin wani bidiyo da Adelabu ke yin jawabi a wani taro, ya ce burinsa ba saboda son kai ba ne amma saboda ainihin sha’awar inganta rayuwar mutanen Jihar Oyo ne.

 

Ministan Lafiya Da Walwalar Jama‘a, Muhammad Ali Pate

Ministan lafiya da walwalar jama’a, Muhammad Ali Pate, kwararren masani ne a fannin kiwon lafiya wanda ya samu kwarewa a matakin kasa da kasa. A baya ya yi aiki a matsayin karamin ministan lafiya a tsakanin watan Yulin 2011 zuwa Yuli 2013 a karkashin tsohon shugaban kasa, Goodluck Jonathan, sannan daga baya ya yi aiki a matsayin daraktan cibiyar kudi ta Dduniya (GFF) da ke karkashin Bankin Duniya.

Pate ya taba tsayawa takarar gwamnan Gombe a baya kuma har yanzu yana da tasiri a siyasar jihar, abin da ke ci gaba da sanya shi cikin jerin masu yiwuwar tsayawa takara a 2027.

An ya ruwaito cewa wasu kungiyoyi sun ci gaba da bayyana shi a matsayin dan takara mai karfi a zaben gwamnan Gombe a shekarar 2027. Daya daga cikin irin wadannan kungiyoyin sun hada da kungiyar tsofaffin daliban makarantar firamare ta Bakaro/Dangikka, ta bayyana shi a matsayin dan takarar da ya dace da wannan mukami.

A cikin wata sanarwa da sakataren janar na kungiyar, Umar Musa, ya sanya hannu, mai taken “Dalilin da ya sa Gombe ke bukatar Farfesa Ali Pate a matsayin gwamna a 2027”, kungiyar ta bukaci shi ya yi takara, inda ta bayyana cewa, “Lokaci ya yi na sabon zamani na shugabanci mai ma’ana da ci gaba a Jihar Bauchi tare da hangen nesa, kwarewa da sadaukarwa ga hidimin jama’a.

“A ra’ayinmu ministan harkokin lafiya da walwalar jama’a, Farfesa Mohammed Ali Pate shi ne mutumin da ya fi dacewa da kujerar gwamnan Gombe a 2027.

“Pate shi ne ministan harkokin lafiya da walwalar jama’a. Nasarori da cancantarsa su ne suka sanya shi ya zama dan takara mafi dacewa, wanda yake da duk abin da ake bukata don zama gwamnan Jihar Gombe a 2027.”

 

Ministan Noma Da Samar Da Abinci, Abubakar Kyari

An fara zaben Kyari zuwa majalisar wakilai a shekarar 1998 a lokacin mulkin soja na Janar Sani Abacha karkashin tutar jam’iyyar UNCP. Daga baya ya koma jam’iyyar APC, ya yi aiki a matsayin mataimakin shugaban jam’iyyar na arewa, matsayin da ya karfafa tasirinsa a cikin jam’iyyar.

An zabe shi zuwa majalisar dattawa a shekarar 2015 karkashin tutar jam’iyyar APC kuma an sake zabe shi a shekarar 2019, ya yi aiki har zuwa Afrilun 2022 lokacin da ya yi murabus domin daukar matsayin mataimakin shugaban jam’iyyar na arewa. Ya yi dan gajeren lokaci yana aiki a matsayin mukaddashin shugaban jam’iyyar a watan Yulin 2023 bayan murabus din Abdullahi Adamu, kafin a nadinshi a matsayin ministan noma da samar da abinci ta cikin majalisar zartarwar Shugaba kasa Bola Tinubu a watan Agusta 2023 bayan amincewar majalisar dattawa.

Ko da yake bai yi wata sanarwa a hukumace ba, amma kungiyoyi da dama, ciki har da Borno ‘Social Media Frontiers’ (BSF), sun nuna Kyari a matsayin dan takara gwamnan Jihar Borno da zai gaji Babagana Umara Zulum.

 

Ministan Sufuri, Saidu Alkali

Tsohon sanatan da ya yi wa’adi har guda uku wanda ya wakilci Gombe ta arewa a majalisu na 6, 7 da na 9, ana ganin yana aiki daga Abuja don samun tikitin gwamna na APC a Jihar Gombe.

Kwarewar siyasar Alkali ya shafi rawar da ya taka a majalisar dokoki da na zartarwa. A baya ya yi aiki a matsayin kwamishina yada labarai a Jihar Gombe, sannan daga baya ya shugabanci kwamitin majalisar dattawa kan harkokin sojan saman Nijeriya.

Kwarewarsa da hanyar sadarwarsa na siyasa sun sa da yawa suna hasashen zai iya samun tikitin takarar gwamnan APC a jihar.

 

Ministan Harkokin Waje, Yusuf Maitama Tuggar

Ana sa ran Yusuf Maitama Tuggar zai bar majalisar ministoci don cimma burinsa na zama gwamnan Jihar Bauchi, wanda zai shiga cikin wadanda za su fafatawa takara a cikin jam’iyyar APC.

A baya ya yi aiki a matsayin mamba na majalisar wakilai daga 2007 zuwa 2011, ya wakilci mazabar Gamawa, kuma ya yi takarar gwamnan sau biyu.

Burinsa ya fara tun daga shekara ta 2011 lokacin da ya tsaya takara karkashin jam’iyyar CPC, sannan kuma a shekara ta 2015 lokacin da ya sha kaye a zabukan fid da gwani na APC. A yanzu ana ganin shi a matsayin dan takara mai karfi wajen fafatawa a jihar.

Wata kungiyar masu matsin lamba da ke Bauchi, ta yi kira ga Tuggar a wani taro da aka gudanar ‘yan watanni da suka gabata da ya shiga takarar zaben gwamna na 2027, tana mai jaddada bukatar mulkin jiyar ya juya zuwa Bauchi ta arewa bayan shekaru na shugabancin Bauchi ta kudu.

Wani dattijo na APC, Abdullahi Usman Matori, wanda ya yi magana a taron, ya kare kiran da ake yi na cewa Bauchi ta arewa su samar da gwamnan jihar na gaba, yana mai lura cewa Bauchi ta kudu ta rike wannan matsayi tun daga 1999.

 

Ministan Sadarwa Da Tattalin Arzikin Zamani, Bosun Tijani

Bosun Tijani, ana yawan girmama shi saboda kwarewarsa a fannin fasaha. Yana daya daga cikin wadanda suka kafa ‘Co-Creation Hub’ (CcHUB), daya daga cikin manyan cibiyoyin kirkira a Afirka, kuma ya samu digirin digirgir a fannin kirƙira da ci gaban tattalin arziki daga Jami’ar Leicester a 2023.

Tun lokacin da aka nada shi, ya mai da hankali kan kayayyakin more rayuwa na zamani da tallafa wa ci gaban tattalin arziki da fasaha ke jagoranta.

Ko da yake bai bayyana niyyarsa ta tsayawa takarar gwamna tun da dadewa, an kuma ambaci Tijani a matsayin mai yiwuwa ya tsaya takarar gwamnan Jihar Ogun a 2027.

Ministoci
Yusuf Shuaibu
+ posts Bio
  • Yusuf Shuaibu
    https://hausa.leadership.ng/author/yusuf-shuaibu/
    2027: APC Na Fuskantar Matsin Lamba Kan Sake Fasalin Tawagar Yakin Neman Zabe
  • Yusuf Shuaibu
    https://hausa.leadership.ng/author/yusuf-shuaibu/
    Cacar Baki Ta Kaure Tsakanin APC Da ‘Yan Adawa Kan Tallafin Gwamnatin Tarayya Ga Magidanta
  • Yusuf Shuaibu
    https://hausa.leadership.ng/author/yusuf-shuaibu/
    INEC Ta Zayyano Kalubalen Da Ke Iya Shafar Sahihancin Zaben 2027
  • Yusuf Shuaibu
    https://hausa.leadership.ng/author/yusuf-shuaibu/
    2027:Kamun Ludayin Yakin Neman Zaben Manyan ‘Yan Takarar Shugaban Kasa
Ministoci
Sulaiman
+ posts Bio
  • Sulaiman
    Batun AI Zai Fi Daukar Hankali A Bikin Baje Kolin Fasahar Zamani Ta Duniya Karo Na 5
  • Sulaiman
    Cinikin Wajen Sin Ya Ci Gaba Da Samun Bunkasa Cikin Sauri A Watanni Takwas Na Farkon Bana
  • Sulaiman
    ‘Yan Bindiga Sun Kashe 2, Sun Yi Garkuwa Da 26 A Kaduna
  • Sulaiman
    Binciken CGTN Ya Nuna Gamsuwa Da Yadda Baje Kolin CIFTIS Ke Shaida Karfin Gwiwar Sin A Fannin Kara Fadada Bude Kofa Bisa Babban Matsayi

MASU ALAKA

2027: APC Na Fuskantar Matsin Lamba Kan Sake Fasalin Tawagar Yakin Neman Zabe
Tambarin Dimokuradiyya

2027: APC Na Fuskantar Matsin Lamba Kan Sake Fasalin Tawagar Yakin Neman Zabe

September 5, 2026
Cacar Baki Ta Kaure Tsakanin APC Da ‘Yan Adawa Kan Tallafin Gwamnatin Tarayya Ga Magidanta
Tambarin Dimokuradiyya

Cacar Baki Ta Kaure Tsakanin APC Da ‘Yan Adawa Kan Tallafin Gwamnatin Tarayya Ga Magidanta

September 4, 2026
Ko INEC Na Da Hannu A Rikice-rikicen Jam’iyyun Siyasa A Nijeriya?
Tambarin Dimokuradiyya

INEC Ta Zayyano Kalubalen Da Ke Iya Shafar Sahihancin Zaben 2027

August 28, 2026
Next Post
ADC Ta Fara Sayar Da Fom Din Takara Kafin Babban Taron Jam’iyya

ADC Ta Fara Sayar Da Fom Din Takara Kafin Babban Taron Jam'iyya

LABARAI MASU NASABA

Batun AI Zai Fi Daukar Hankali A Bikin Baje Kolin Fasahar Zamani Ta Duniya Karo Na 5

Batun AI Zai Fi Daukar Hankali A Bikin Baje Kolin Fasahar Zamani Ta Duniya Karo Na 5

September 8, 2026
Gwamna Radda Ya Samu Goyon Bayan APC A Katsina Gabanin Zaɓen 2027

Gwamna Radda Ya Samu Goyon Bayan APC A Katsina Gabanin Zaɓen 2027

September 8, 2026
Cinikin Wajen Sin Ya Ci Gaba Da Samun Bunkasa Cikin Sauri A Watanni Takwas Na Farkon Bana

Cinikin Wajen Sin Ya Ci Gaba Da Samun Bunkasa Cikin Sauri A Watanni Takwas Na Farkon Bana

September 8, 2026
'Yan Bindiga

‘Yan Bindiga Sun Kashe 2, Sun Yi Garkuwa Da 26 A Kaduna

September 8, 2026
Binciken CGTN Ya Nuna Gamsuwa Da Yadda Baje Kolin CIFTIS Ke Shaida Karfin Gwiwar Sin A Fannin Kara Fadada Bude Kofa Bisa Babban Matsayi

Binciken CGTN Ya Nuna Gamsuwa Da Yadda Baje Kolin CIFTIS Ke Shaida Karfin Gwiwar Sin A Fannin Kara Fadada Bude Kofa Bisa Babban Matsayi

September 8, 2026
Yadda Taron Tattalin Arziki Da Zuba Jari Na Kwana Biyu Ya Gudana A Katsina

Gwamna Radda Ya Gabatar Da Kasafin N828.6bn Na 2027

September 8, 2026
Sin Za Ta Yi Aiki Tare Da Sassa Daban Daban Domin Mayar Da Fasahar AI Wata Dama Ta Cin Gajiya Mai Dorewa

Sin Za Ta Yi Aiki Tare Da Sassa Daban Daban Domin Mayar Da Fasahar AI Wata Dama Ta Cin Gajiya Mai Dorewa

September 8, 2026
Gwamnan Kebbi Ya Bayyana Shirin Sake Duba Albashin Malaman Firamare

Gwamna Idris Ya Rushe Majalisar Shugabannin Hukumar Zaɓe Ta Kebbi

September 8, 2026
Han Zheng Ya Halarci Baje Kolin CIFIT Karo Na 26 Tare Da Gabatar Da Jawabi

Han Zheng Ya Halarci Baje Kolin CIFIT Karo Na 26 Tare Da Gabatar Da Jawabi

September 8, 2026
Wani Soja Ya Kashe Kansa Bayan Kashe Matarsa A Jihar Neja

Kano Za Ta Kafa Sansanonin Sojoji A Ƙananan Hukumomin Da Ke Fuskantar Barazanar Tsaro

September 8, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.