ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Thursday, July 16, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

2027: Obi Da Kwankwaso Za Su Fafata Da Atiku Wajen Neman Takarar Shugaban Kasa A ADC

by Yusuf Shuaibu and Sulaiman
3 months ago
Kwankwaso

Tsohon gwamnan Jihar Kano kuma dan takarar shugaban kasa a jam’iyyar NNPP a 2023, Sanata Rabiu Musa Kwankwaso, ya yi murabus a hukumance a jam’iyyarsa ta NNPP, inda ya sanar da sauya sheka zuwa jam’iyyar ADC.

Shigowar Kwankwaso cikin ADC ta tayar da tattaunawa kan hadin gwiwarsa da dan takarar shugaban kasa na jam’iyyar LP a 2023, Peter Obi, don samun tikitin shugaban kasa na jam’iyyar a 2027.

  • Sin Ta Fitar Da Mizanin Kasa Na Kyautata Nagartar Na’urar Adana Lantarki
  • Ba Za A Iya Daidaita Batun Mashigin Hormuz Ba Har Sai An Kawo Karshen Yaki

An samu labarin cewa tafiyar Obi zuwa Kano kwanan nan a lokacin watan Ramadan ta bude hanyar tattaunawar tsakanin manyan ‘yan siyasar guda biyu.

ADVERTISEMENT

Sannan kuma an bayyana cewa Obi ya yi alkawari yin wa’adi daya kawai idan aka zabe shi a matsayin shugaban kasa domin samun kuri’un ‘yan arewaci, yayin da arewa za ta nemi dawowa kann mulki a 2031.

Majiyoyi sun ce sauya shekar Kwankwaro zuwa ADC na nuna babban sauyi a siyasa yayin da dan takarar daga arewa maso yamma zai iya haduwa da dan takara daga kudu maso gabas don kayar da shugaban kasa daga jam’iyyar APC.

LABARAI MASU NASABA

‘Yan Ƙasar Turkiyya Sun Nuna Jarumta Da Kare Dimokuraɗiyya Mafi Girma A Tarihi – Erdoğan

Amurka Ta Yi Alƙawarin Sa Ido Sosai A Zaɓen Nijeriya Na 2027

Haka kuma wasu majiyoyi sun tabbatar da cewa manyan shugabannin ADC na neman yanayi, inda Obi da Kwankwaso za su yi hadin kai a takarar shugaban kasa, yayin da tsohon mataimakin shugaban kasa, Atiku Abubakar zai iya goyon bayan tikitin.

“Wani abu ne da muke aiki a kai, kuma akwai kwarin gwiwa mai karfi na cewa tsohon gwamnan Jihar Kano yana da dubban magoya baya a arewa maso yamma wadanda za su kara yawan kuri’un Obi idan ya samu damar tsayawa takara a zaben fitar da gwani na kai tsaye,” in ji wata majiya.

Sai dai kuma sakataren yada labarai na jam’iyyar ADC, Malam Bolaji Abdullahi, ya musanta wannan hadaka game da tikitin Obi da Kwankwaso, yana mai cewa kawai, ‘A’a. Ba gaskiya ba ne.’

Yayin da yake amsa tambayoyin manema labarai, Abdullahi ya karyata ra’ayin cewa ADC ta bai wa Kwankwaso matsayin abokin takarar Obi. “A’a. Ba gaskiya ba ne,” in ji shi.

Kazalika, majiyoyi sun shaida cewa jam’iyyar na da sha’awar samu yarjejeiya ta hanyar tara manyan ‘yan takarar shugaban kasa don su shiga cikin shirye-shiryenta.

An sanar da sauya shekar Kwankwaso ta hanyar wata sanarwa da aka fitar ranar 29 ga Maris, 2026, wacce ya sanar da yin murabus daga NNPP, yana bayyana bukatar sake tsara dabaru don amsa canje-canjen siyasa a kasar.

Ya ce, “Ina so in sanar da a hukumance game da yi muraus dina daga jam’iyyar NNPP nan take,” in ji shi, ya kara da cewa wannan shawara, duk da wahalar ta, ta zama dole domin ba shi damar shiga wani jam’iyyar siyasa wanda ke ba da mafi kyawun damar sauya kasa.

Kwankwaso, wanda ya yi aiki a matsayin jagorar jam’iyyar NNPP kuma dan takarar shugaban kasa a 2023, ya yi godiya ga shugabancin jam’iyyar, ciki har da shugaban jam’iyyar na kasa, Ajuji Ahmed da kwamitin gudanarwa na jam’iyyar da kwamitin amintattu na kasa da mambobi jam’iyyar a dukkan matakai bisa goyon bayansu a lokacin da yake cikin jam’iyyar.

Har ila yau, ya amince da kugiyarsa ta Kwankwasiyya a matsayin wata kungiyar siyasa mai karfi a matakin tushe wanda aka yarda cewa ta kara tasirin NNPP, musamman a Jihar Kano da wasu sassan arewacin Nijeriya.

“Za mu ci gaba da hada kai da yin aiki tare don tsara makoma mafi kyau da kyawun yanayi ga kasarmu ta gado,” in ji shi.

 

Murabus din Kwankwaso ta zo ne kafin ya sauya sheka zuwa jam’iyyar ADC, wanda aka tsara a ranar Litinin da misalin karfe 12 na rana a Jihar Kano.

A wani martani ga lamarin, NNPP ta tabbatar da cewa ta san da shirin barin jam’iyyar da Kwankwaso ya yi kuma tana bibiyar yanayin sosai.

Sakataren yada labarai na kasa na jam’iyyar, Ladipo Johnson, ya ce sanarwar farko ta fito ne daga kungiyar Kwankwasiyya amma ya lura cewa jam’iyyar ta dauki sanarwa ta hukuma game da wannan lamari.

“Mun san da shirin barin jam’iyya, kuma a makonni masu zuwa, ana sa ran wasu ‘yan jam’iyya za su kuma bi shi zuwa sabon jam’iyyar siyasa da ya tafi,” in ji Johnson.

Mai magana da yawun NNPP ya amince cewa ficewar Kwankwaso na iya haifar da karin masu sauya sheka, ya nuna damuwa game da rage karfin jam’iyyar, musamman a yankunan arewacin da tafi karfi.

Ana sa ran cewa kungiyar Kwankwasiyya za ta yi aiki tare da Obidients, kungiyar da ke goyon bayan Mista Peter Obi don samun tikitin shugaban kasa a ADC.

Ficewar Kwankwaso na zuwa ne a daidai lokacin da manyan ‘yan siyasa a fadin kasar da jam’iyyun siyasa ke sake tsara matsayinsu kafin zaben da ke tafe.

Ana ganin shigar Kwankwaso jam’iyyar ADC zai kara habaka matsayin jam’iyyar bisa la’akari da kwarewar siyasarsa da kuma karfin goyon baya a arewa maso yamma.

Kwankwaso
Yusuf Shuaibu
+ posts Bio
  • Yusuf Shuaibu
    https://hausa.leadership.ng/author/yusuf-shuaibu/
    Amurka Ta Yi Alƙawarin Sa Ido Sosai A Zaɓen Nijeriya Na 2027
  • Yusuf Shuaibu
    https://hausa.leadership.ng/author/yusuf-shuaibu/
    Sautin Muryar Da Aka Fallasa Kan El-Rufai Ya Haifar Da Zazzafar Muhawara
  • Yusuf Shuaibu
    https://hausa.leadership.ng/author/yusuf-shuaibu/
    Ci-ma-zaunen Ƴan Siyasa Ne Ke Tunanin Yin Maguɗi A Zaɓen 2027 – Makarfi
  • Yusuf Shuaibu
    https://hausa.leadership.ng/author/yusuf-shuaibu/
    An Samu Ruɗani Kan Rashin Bayyana Jerin Ƴan Takarar Jam’iyyun Siyasa Na Zaɓen 2027
Kwankwaso
Sulaiman
+ posts Bio
  • Sulaiman
    Binciken CGTN: Amfanar Da Kowa Da Kowa Shi Ne Ainihin Alherin Da Fasahohin Kwaikwayon Tunanin Bil Adama Suka Kawo
  • Sulaiman
    Sin Ta Yi Kira Da A Kafa Tsarin Jagorantar Muhimman Ma’adinai Ga Sauyawa Zuwa Amfani Da Makamashi Mai Tsafta
  • Sulaiman
    Gwamna Dauda Lawal Zai Gabatar Da Jawabi A Taron Ƙasa Da Ƙasa Na Jami’ar FUE Zariya
  • Sulaiman
    Neman Raba-Gari Da Sauran Kasashe Zai Kawo Mummuann Tasiri Ga Bangarorin Da Abin Ya Shafa

MASU ALAKA

‘Yan Ƙasar Turkiyya Sun Nuna Jarumta Da Kare Dimokuraɗiyya Mafi Girma A Tarihi – Erdoğan
Manyan Labarai

‘Yan Ƙasar Turkiyya Sun Nuna Jarumta Da Kare Dimokuraɗiyya Mafi Girma A Tarihi – Erdoğan

July 15, 2026
Amurka Ta Yi Alƙawarin Sa Ido Sosai A Zaɓen Nijeriya Na 2027
Tambarin Dimokuradiyya

Amurka Ta Yi Alƙawarin Sa Ido Sosai A Zaɓen Nijeriya Na 2027

July 11, 2026
Sautin Muryar Da Aka Fallasa Kan El-Rufai Ya Haifar Da Zazzafar Muhawara
Tambarin Dimokuradiyya

Sautin Muryar Da Aka Fallasa Kan El-Rufai Ya Haifar Da Zazzafar Muhawara

July 11, 2026
Next Post
CBN Ya Ɗage Tsarin Dijital, Zai Biya Mahajjata Kuɗin Guzurinsu A Hannu

CBN Ya Ɗage Tsarin Dijital, Zai Biya Mahajjata Kuɗin Guzurinsu A Hannu

LABARAI MASU NASABA

Binciken CGTN: Amfanar Da Kowa Da Kowa Shi Ne Ainihin Alherin Da Fasahohin Kwaikwayon Tunanin Bil Adama Suka Kawo

Binciken CGTN: Amfanar Da Kowa Da Kowa Shi Ne Ainihin Alherin Da Fasahohin Kwaikwayon Tunanin Bil Adama Suka Kawo

July 15, 2026
Sin Ta Yi Kira Da A Kafa Tsarin Jagorantar Muhimman Ma’adinai Ga Sauyawa Zuwa Amfani Da Makamashi Mai Tsafta

Sin Ta Yi Kira Da A Kafa Tsarin Jagorantar Muhimman Ma’adinai Ga Sauyawa Zuwa Amfani Da Makamashi Mai Tsafta

July 15, 2026
Gwamna Dauda Lawal Zai Gabatar Da Jawabi A Taron Ƙasa Da Ƙasa Na Jami’ar FUE Zariya

Gwamna Dauda Lawal Zai Gabatar Da Jawabi A Taron Ƙasa Da Ƙasa Na Jami’ar FUE Zariya

July 15, 2026
Neman Raba-Gari Da Sauran Kasashe Zai Kawo Mummuann Tasiri Ga Bangarorin Da Abin Ya Shafa

Neman Raba-Gari Da Sauran Kasashe Zai Kawo Mummuann Tasiri Ga Bangarorin Da Abin Ya Shafa

July 15, 2026
Kevin Kelly: AI Na Iya Taimakawa Wajen Cimma Burin “Koyar Da Dalibai Da Kwazonsu”

Kevin Kelly: AI Na Iya Taimakawa Wajen Cimma Burin “Koyar Da Dalibai Da Kwazonsu”

July 15, 2026
Gwamna Yusuf Ya Bai Wa Masu Kula Da Akwatinan Zaɓe Na APC Filaye 1,540 Da Tallafin Miliyan 100

Gwamna Yusuf Ya Bai Wa Masu Kula Da Akwatinan Zaɓe Na APC Filaye 1,540 Da Tallafin Miliyan 100

July 15, 2026
Sabbin Ministoci

Rashin Tsaro: Majalisar Dattawa Ta Bukaci A Tura Ƙarin Sojoji da ’Yansanda Zuwa Benuwe

July 15, 2026
GDPn Sin A Rabin Farko Na Shekarar 2026 Ya Karu Da Kashi 4.7% Idan Aka Kwatanta Da Na Kwatankwacin Lokacin Bara

GDPn Sin A Rabin Farko Na Shekarar 2026 Ya Karu Da Kashi 4.7% Idan Aka Kwatanta Da Na Kwatankwacin Lokacin Bara

July 15, 2026
‘Yansanda Sun Tsaurara Tsaron Iyakokin Kano Bayan Hare-haren ‘Yan Bindiga 

Atiku Ya Nuna Damuwa Kan Kasafin Naira Biliyan 6.44 Don Gasar Cin Kofin Duniya ta 2026

July 15, 2026
Masana Kandagarkin Cututtuka Na Sin Sun Tashi Zuwa Kasar Uganda Don Aikin Hadin Gwiwar Magance Cutar Ebola

Masana Kandagarkin Cututtuka Na Sin Sun Tashi Zuwa Kasar Uganda Don Aikin Hadin Gwiwar Magance Cutar Ebola

July 15, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.