ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Wednesday, June 24, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

2027: Obi Da Kwankwaso Za Su Fafata Da Atiku Wajen Neman Takarar Shugaban Kasa A ADC

by Yusuf Shuaibu and Sulaiman
3 months ago
Kwankwaso

Tsohon gwamnan Jihar Kano kuma dan takarar shugaban kasa a jam’iyyar NNPP a 2023, Sanata Rabiu Musa Kwankwaso, ya yi murabus a hukumance a jam’iyyarsa ta NNPP, inda ya sanar da sauya sheka zuwa jam’iyyar ADC.

Shigowar Kwankwaso cikin ADC ta tayar da tattaunawa kan hadin gwiwarsa da dan takarar shugaban kasa na jam’iyyar LP a 2023, Peter Obi, don samun tikitin shugaban kasa na jam’iyyar a 2027.

  • Sin Ta Fitar Da Mizanin Kasa Na Kyautata Nagartar Na’urar Adana Lantarki
  • Ba Za A Iya Daidaita Batun Mashigin Hormuz Ba Har Sai An Kawo Karshen Yaki

An samu labarin cewa tafiyar Obi zuwa Kano kwanan nan a lokacin watan Ramadan ta bude hanyar tattaunawar tsakanin manyan ‘yan siyasar guda biyu.

ADVERTISEMENT

Sannan kuma an bayyana cewa Obi ya yi alkawari yin wa’adi daya kawai idan aka zabe shi a matsayin shugaban kasa domin samun kuri’un ‘yan arewaci, yayin da arewa za ta nemi dawowa kann mulki a 2031.

Majiyoyi sun ce sauya shekar Kwankwaro zuwa ADC na nuna babban sauyi a siyasa yayin da dan takarar daga arewa maso yamma zai iya haduwa da dan takara daga kudu maso gabas don kayar da shugaban kasa daga jam’iyyar APC.

LABARAI MASU NASABA

Yadda Matsin Lamba Ta Sa Amaechi Ya Amince Ya Zama Abokin Takarar Atiku

2027: Kallo Ya Koma Kan Yadda APC, ADC Da PDP Ke Neman Abokan Takarar Mataimakin Shugaban Kasa

Haka kuma wasu majiyoyi sun tabbatar da cewa manyan shugabannin ADC na neman yanayi, inda Obi da Kwankwaso za su yi hadin kai a takarar shugaban kasa, yayin da tsohon mataimakin shugaban kasa, Atiku Abubakar zai iya goyon bayan tikitin.

“Wani abu ne da muke aiki a kai, kuma akwai kwarin gwiwa mai karfi na cewa tsohon gwamnan Jihar Kano yana da dubban magoya baya a arewa maso yamma wadanda za su kara yawan kuri’un Obi idan ya samu damar tsayawa takara a zaben fitar da gwani na kai tsaye,” in ji wata majiya.

Sai dai kuma sakataren yada labarai na jam’iyyar ADC, Malam Bolaji Abdullahi, ya musanta wannan hadaka game da tikitin Obi da Kwankwaso, yana mai cewa kawai, ‘A’a. Ba gaskiya ba ne.’

Yayin da yake amsa tambayoyin manema labarai, Abdullahi ya karyata ra’ayin cewa ADC ta bai wa Kwankwaso matsayin abokin takarar Obi. “A’a. Ba gaskiya ba ne,” in ji shi.

Kazalika, majiyoyi sun shaida cewa jam’iyyar na da sha’awar samu yarjejeiya ta hanyar tara manyan ‘yan takarar shugaban kasa don su shiga cikin shirye-shiryenta.

An sanar da sauya shekar Kwankwaso ta hanyar wata sanarwa da aka fitar ranar 29 ga Maris, 2026, wacce ya sanar da yin murabus daga NNPP, yana bayyana bukatar sake tsara dabaru don amsa canje-canjen siyasa a kasar.

Ya ce, “Ina so in sanar da a hukumance game da yi muraus dina daga jam’iyyar NNPP nan take,” in ji shi, ya kara da cewa wannan shawara, duk da wahalar ta, ta zama dole domin ba shi damar shiga wani jam’iyyar siyasa wanda ke ba da mafi kyawun damar sauya kasa.

Kwankwaso, wanda ya yi aiki a matsayin jagorar jam’iyyar NNPP kuma dan takarar shugaban kasa a 2023, ya yi godiya ga shugabancin jam’iyyar, ciki har da shugaban jam’iyyar na kasa, Ajuji Ahmed da kwamitin gudanarwa na jam’iyyar da kwamitin amintattu na kasa da mambobi jam’iyyar a dukkan matakai bisa goyon bayansu a lokacin da yake cikin jam’iyyar.

Har ila yau, ya amince da kugiyarsa ta Kwankwasiyya a matsayin wata kungiyar siyasa mai karfi a matakin tushe wanda aka yarda cewa ta kara tasirin NNPP, musamman a Jihar Kano da wasu sassan arewacin Nijeriya.

“Za mu ci gaba da hada kai da yin aiki tare don tsara makoma mafi kyau da kyawun yanayi ga kasarmu ta gado,” in ji shi.

 

Murabus din Kwankwaso ta zo ne kafin ya sauya sheka zuwa jam’iyyar ADC, wanda aka tsara a ranar Litinin da misalin karfe 12 na rana a Jihar Kano.

A wani martani ga lamarin, NNPP ta tabbatar da cewa ta san da shirin barin jam’iyyar da Kwankwaso ya yi kuma tana bibiyar yanayin sosai.

Sakataren yada labarai na kasa na jam’iyyar, Ladipo Johnson, ya ce sanarwar farko ta fito ne daga kungiyar Kwankwasiyya amma ya lura cewa jam’iyyar ta dauki sanarwa ta hukuma game da wannan lamari.

“Mun san da shirin barin jam’iyya, kuma a makonni masu zuwa, ana sa ran wasu ‘yan jam’iyya za su kuma bi shi zuwa sabon jam’iyyar siyasa da ya tafi,” in ji Johnson.

Mai magana da yawun NNPP ya amince cewa ficewar Kwankwaso na iya haifar da karin masu sauya sheka, ya nuna damuwa game da rage karfin jam’iyyar, musamman a yankunan arewacin da tafi karfi.

Ana sa ran cewa kungiyar Kwankwasiyya za ta yi aiki tare da Obidients, kungiyar da ke goyon bayan Mista Peter Obi don samun tikitin shugaban kasa a ADC.

Ficewar Kwankwaso na zuwa ne a daidai lokacin da manyan ‘yan siyasa a fadin kasar da jam’iyyun siyasa ke sake tsara matsayinsu kafin zaben da ke tafe.

Ana ganin shigar Kwankwaso jam’iyyar ADC zai kara habaka matsayin jam’iyyar bisa la’akari da kwarewar siyasarsa da kuma karfin goyon baya a arewa maso yamma.

Kwankwaso
Yusuf Shuaibu
+ posts Bio
  • Yusuf Shuaibu
    https://hausa.leadership.ng/author/yusuf-shuaibu/
    Rashin Tsaro Na Barazana Ga Zaben 2027 —Rahotanni
  • Yusuf Shuaibu
    https://hausa.leadership.ng/author/yusuf-shuaibu/
    Yadda Matsin Lamba Ta Sa Amaechi Ya Amince Ya Zama Abokin Takarar Atiku
  • Yusuf Shuaibu
    https://hausa.leadership.ng/author/yusuf-shuaibu/
    2027: Kallo Ya Koma Kan Yadda APC, ADC Da PDP Ke Neman Abokan Takarar Mataimakin Shugaban Kasa
  • Yusuf Shuaibu
    https://hausa.leadership.ng/author/yusuf-shuaibu/
    Ko INEC Na Da Hannu A Rikice-rikicen Jam’iyyun Siyasa A Nijeriya?
Kwankwaso
Sulaiman
+ posts Bio
  • Sulaiman
    Yadda Uba Sani Ya Farfaɗo Da Asibitin Da Aka Yi Watsi Da Shi Tsawon Shekaru 40 – Hakimin Makarfi
  • Sulaiman
    Dandalin DAVOS Na Bana: Fage Ne Da “Kirkire-Kirkiren Sin” Ya Sadu Da “Kyakkyawan Fatan Afirka”
  • Sulaiman
    Binciken CGTN: Amfanarwa A Aikace Shi Ne Nagartaccen Ma’aunin Tantance Ainihin Kimar Sabbin Fasahohi
  • Sulaiman
    Kasar Sin Na Kara Zama Babban Ginshikin Ci Gaban Tattalin Arzikin Duniya Na Gaba

MASU ALAKA

Yadda Matsin Lamba Ta Sa Amaechi Ya Amince Ya Zama Abokin Takarar Atiku
Tambarin Dimokuradiyya

Yadda Matsin Lamba Ta Sa Amaechi Ya Amince Ya Zama Abokin Takarar Atiku

June 19, 2026
2027: Kallo Ya Koma Kan Yadda APC, ADC Da PDP Ke Neman Abokan Takarar Mataimakin Shugaban Kasa
Tambarin Dimokuradiyya

2027: Kallo Ya Koma Kan Yadda APC, ADC Da PDP Ke Neman Abokan Takarar Mataimakin Shugaban Kasa

June 12, 2026
Ko INEC Na Da Hannu A Rikice-rikicen Jam’iyyun Siyasa A Nijeriya?
Tambarin Dimokuradiyya

Ko INEC Na Da Hannu A Rikice-rikicen Jam’iyyun Siyasa A Nijeriya?

June 12, 2026
Next Post
CBN Ya Ɗage Tsarin Dijital, Zai Biya Mahajjata Kuɗin Guzurinsu A Hannu

CBN Ya Ɗage Tsarin Dijital, Zai Biya Mahajjata Kuɗin Guzurinsu A Hannu

LABARAI MASU NASABA

Yadda Uba Sani Ya Farfaɗo Da Asibitin Da Aka Yi Watsi Da Shi Tsawon Shekaru 40 – Hakimin Makarfi

Yadda Uba Sani Ya Farfaɗo Da Asibitin Da Aka Yi Watsi Da Shi Tsawon Shekaru 40 – Hakimin Makarfi

June 24, 2026
Dandalin DAVOS Na Bana: Fage Ne Da “Kirkire-Kirkiren Sin” Ya Sadu Da “Kyakkyawan Fatan Afirka”

Dandalin DAVOS Na Bana: Fage Ne Da “Kirkire-Kirkiren Sin” Ya Sadu Da “Kyakkyawan Fatan Afirka”

June 24, 2026
Binciken CGTN: Amfanarwa A Aikace Shi Ne Nagartaccen Ma’aunin Tantance Ainihin Kimar Sabbin Fasahohi

Binciken CGTN: Amfanarwa A Aikace Shi Ne Nagartaccen Ma’aunin Tantance Ainihin Kimar Sabbin Fasahohi

June 24, 2026
Kasar Sin Na Kara Zama Babban Ginshikin Ci Gaban Tattalin Arzikin Duniya Na Gaba

Kasar Sin Na Kara Zama Babban Ginshikin Ci Gaban Tattalin Arzikin Duniya Na Gaba

June 24, 2026
Tsaro: Dasuki Ya Bukaci Tinubu Ya Gyara Alaka Da Nijar Domin Kare Iyakokin Arewa-Maso-Yamma

Tsaro: Dasuki Ya Bukaci Tinubu Ya Gyara Alaka Da Nijar Domin Kare Iyakokin Arewa-Maso-Yamma

June 24, 2026
Sabbin Ministoci

Kafa ‘Yansandan Jihohi: Majalisa Ta Amince Da Tsarin ‘Yar Tinƙe Wajen Kaɗa Ƙuri’a 

June 24, 2026
Sin Ta Gabatar Da Tsarin Karfafa Kwarin Gwiwar Kamfanoni Masu Jarin Waje

Sin Ta Gabatar Da Tsarin Karfafa Kwarin Gwiwar Kamfanoni Masu Jarin Waje

June 24, 2026
Shugaban Kasar Burundi: Dangantakar Afirka Da Sin Misali Ce Ta Hadin Gwiwar Kasashe Masu Tasowa

Shugaban Kasar Burundi: Dangantakar Afirka Da Sin Misali Ce Ta Hadin Gwiwar Kasashe Masu Tasowa

June 24, 2026
Yadda Na Sayar Da Kadarori Na Don Ɗaukar Nauyin Ɗalibai A Ƙasashen Waje – Kwankwaso

Zargin Ɓata Suna: Kwankwaso Ya Yi Barazanar Neman Diyyar Naira Biliyan 10 Kan Wani Malamin Coci

June 24, 2026
Li Qiang Ya Halarci Bikin Bude Dandalin Tattalin Arzikin Duniya Na Davos Na Shekarar 2026

Li Qiang Ya Halarci Bikin Bude Dandalin Tattalin Arzikin Duniya Na Davos Na Shekarar 2026

June 24, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.