ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Wednesday, September 9, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

2027: Obi Da Kwankwaso Za Su Fafata Da Atiku Wajen Neman Takarar Shugaban Kasa A ADC

by Yusuf Shuaibu and Sulaiman
5 months ago
Kwankwaso

Tsohon gwamnan Jihar Kano kuma dan takarar shugaban kasa a jam’iyyar NNPP a 2023, Sanata Rabiu Musa Kwankwaso, ya yi murabus a hukumance a jam’iyyarsa ta NNPP, inda ya sanar da sauya sheka zuwa jam’iyyar ADC.

Shigowar Kwankwaso cikin ADC ta tayar da tattaunawa kan hadin gwiwarsa da dan takarar shugaban kasa na jam’iyyar LP a 2023, Peter Obi, don samun tikitin shugaban kasa na jam’iyyar a 2027.

  • Sin Ta Fitar Da Mizanin Kasa Na Kyautata Nagartar Na’urar Adana Lantarki
  • Ba Za A Iya Daidaita Batun Mashigin Hormuz Ba Har Sai An Kawo Karshen Yaki

An samu labarin cewa tafiyar Obi zuwa Kano kwanan nan a lokacin watan Ramadan ta bude hanyar tattaunawar tsakanin manyan ‘yan siyasar guda biyu.

ADVERTISEMENT

Sannan kuma an bayyana cewa Obi ya yi alkawari yin wa’adi daya kawai idan aka zabe shi a matsayin shugaban kasa domin samun kuri’un ‘yan arewaci, yayin da arewa za ta nemi dawowa kann mulki a 2031.

Majiyoyi sun ce sauya shekar Kwankwaro zuwa ADC na nuna babban sauyi a siyasa yayin da dan takarar daga arewa maso yamma zai iya haduwa da dan takara daga kudu maso gabas don kayar da shugaban kasa daga jam’iyyar APC.

LABARAI MASU NASABA

2027: APC Na Fuskantar Matsin Lamba Kan Sake Fasalin Tawagar Yakin Neman Zabe

Cacar Baki Ta Kaure Tsakanin APC Da ‘Yan Adawa Kan Tallafin Gwamnatin Tarayya Ga Magidanta

Haka kuma wasu majiyoyi sun tabbatar da cewa manyan shugabannin ADC na neman yanayi, inda Obi da Kwankwaso za su yi hadin kai a takarar shugaban kasa, yayin da tsohon mataimakin shugaban kasa, Atiku Abubakar zai iya goyon bayan tikitin.

“Wani abu ne da muke aiki a kai, kuma akwai kwarin gwiwa mai karfi na cewa tsohon gwamnan Jihar Kano yana da dubban magoya baya a arewa maso yamma wadanda za su kara yawan kuri’un Obi idan ya samu damar tsayawa takara a zaben fitar da gwani na kai tsaye,” in ji wata majiya.

Sai dai kuma sakataren yada labarai na jam’iyyar ADC, Malam Bolaji Abdullahi, ya musanta wannan hadaka game da tikitin Obi da Kwankwaso, yana mai cewa kawai, ‘A’a. Ba gaskiya ba ne.’

Yayin da yake amsa tambayoyin manema labarai, Abdullahi ya karyata ra’ayin cewa ADC ta bai wa Kwankwaso matsayin abokin takarar Obi. “A’a. Ba gaskiya ba ne,” in ji shi.

Kazalika, majiyoyi sun shaida cewa jam’iyyar na da sha’awar samu yarjejeiya ta hanyar tara manyan ‘yan takarar shugaban kasa don su shiga cikin shirye-shiryenta.

An sanar da sauya shekar Kwankwaso ta hanyar wata sanarwa da aka fitar ranar 29 ga Maris, 2026, wacce ya sanar da yin murabus daga NNPP, yana bayyana bukatar sake tsara dabaru don amsa canje-canjen siyasa a kasar.

Ya ce, “Ina so in sanar da a hukumance game da yi muraus dina daga jam’iyyar NNPP nan take,” in ji shi, ya kara da cewa wannan shawara, duk da wahalar ta, ta zama dole domin ba shi damar shiga wani jam’iyyar siyasa wanda ke ba da mafi kyawun damar sauya kasa.

Kwankwaso, wanda ya yi aiki a matsayin jagorar jam’iyyar NNPP kuma dan takarar shugaban kasa a 2023, ya yi godiya ga shugabancin jam’iyyar, ciki har da shugaban jam’iyyar na kasa, Ajuji Ahmed da kwamitin gudanarwa na jam’iyyar da kwamitin amintattu na kasa da mambobi jam’iyyar a dukkan matakai bisa goyon bayansu a lokacin da yake cikin jam’iyyar.

Har ila yau, ya amince da kugiyarsa ta Kwankwasiyya a matsayin wata kungiyar siyasa mai karfi a matakin tushe wanda aka yarda cewa ta kara tasirin NNPP, musamman a Jihar Kano da wasu sassan arewacin Nijeriya.

“Za mu ci gaba da hada kai da yin aiki tare don tsara makoma mafi kyau da kyawun yanayi ga kasarmu ta gado,” in ji shi.

 

Murabus din Kwankwaso ta zo ne kafin ya sauya sheka zuwa jam’iyyar ADC, wanda aka tsara a ranar Litinin da misalin karfe 12 na rana a Jihar Kano.

A wani martani ga lamarin, NNPP ta tabbatar da cewa ta san da shirin barin jam’iyyar da Kwankwaso ya yi kuma tana bibiyar yanayin sosai.

Sakataren yada labarai na kasa na jam’iyyar, Ladipo Johnson, ya ce sanarwar farko ta fito ne daga kungiyar Kwankwasiyya amma ya lura cewa jam’iyyar ta dauki sanarwa ta hukuma game da wannan lamari.

“Mun san da shirin barin jam’iyya, kuma a makonni masu zuwa, ana sa ran wasu ‘yan jam’iyya za su kuma bi shi zuwa sabon jam’iyyar siyasa da ya tafi,” in ji Johnson.

Mai magana da yawun NNPP ya amince cewa ficewar Kwankwaso na iya haifar da karin masu sauya sheka, ya nuna damuwa game da rage karfin jam’iyyar, musamman a yankunan arewacin da tafi karfi.

Ana sa ran cewa kungiyar Kwankwasiyya za ta yi aiki tare da Obidients, kungiyar da ke goyon bayan Mista Peter Obi don samun tikitin shugaban kasa a ADC.

Ficewar Kwankwaso na zuwa ne a daidai lokacin da manyan ‘yan siyasa a fadin kasar da jam’iyyun siyasa ke sake tsara matsayinsu kafin zaben da ke tafe.

Ana ganin shigar Kwankwaso jam’iyyar ADC zai kara habaka matsayin jam’iyyar bisa la’akari da kwarewar siyasarsa da kuma karfin goyon baya a arewa maso yamma.

Kwankwaso
Yusuf Shuaibu
+ posts Bio
  • Yusuf Shuaibu
    https://hausa.leadership.ng/author/yusuf-shuaibu/
    2027: APC Na Fuskantar Matsin Lamba Kan Sake Fasalin Tawagar Yakin Neman Zabe
  • Yusuf Shuaibu
    https://hausa.leadership.ng/author/yusuf-shuaibu/
    Cacar Baki Ta Kaure Tsakanin APC Da ‘Yan Adawa Kan Tallafin Gwamnatin Tarayya Ga Magidanta
  • Yusuf Shuaibu
    https://hausa.leadership.ng/author/yusuf-shuaibu/
    INEC Ta Zayyano Kalubalen Da Ke Iya Shafar Sahihancin Zaben 2027
  • Yusuf Shuaibu
    https://hausa.leadership.ng/author/yusuf-shuaibu/
    2027:Kamun Ludayin Yakin Neman Zaben Manyan ‘Yan Takarar Shugaban Kasa
Kwankwaso
Sulaiman
+ posts Bio
  • Sulaiman
    Batun AI Zai Fi Daukar Hankali A Bikin Baje Kolin Fasahar Zamani Ta Duniya Karo Na 5
  • Sulaiman
    Cinikin Wajen Sin Ya Ci Gaba Da Samun Bunkasa Cikin Sauri A Watanni Takwas Na Farkon Bana
  • Sulaiman
    ‘Yan Bindiga Sun Kashe 2, Sun Yi Garkuwa Da 26 A Kaduna
  • Sulaiman
    Binciken CGTN Ya Nuna Gamsuwa Da Yadda Baje Kolin CIFTIS Ke Shaida Karfin Gwiwar Sin A Fannin Kara Fadada Bude Kofa Bisa Babban Matsayi

MASU ALAKA

2027: APC Na Fuskantar Matsin Lamba Kan Sake Fasalin Tawagar Yakin Neman Zabe
Tambarin Dimokuradiyya

2027: APC Na Fuskantar Matsin Lamba Kan Sake Fasalin Tawagar Yakin Neman Zabe

September 5, 2026
Cacar Baki Ta Kaure Tsakanin APC Da ‘Yan Adawa Kan Tallafin Gwamnatin Tarayya Ga Magidanta
Tambarin Dimokuradiyya

Cacar Baki Ta Kaure Tsakanin APC Da ‘Yan Adawa Kan Tallafin Gwamnatin Tarayya Ga Magidanta

September 4, 2026
Ko INEC Na Da Hannu A Rikice-rikicen Jam’iyyun Siyasa A Nijeriya?
Tambarin Dimokuradiyya

INEC Ta Zayyano Kalubalen Da Ke Iya Shafar Sahihancin Zaben 2027

August 28, 2026
Next Post
CBN Ya Ɗage Tsarin Dijital, Zai Biya Mahajjata Kuɗin Guzurinsu A Hannu

CBN Ya Ɗage Tsarin Dijital, Zai Biya Mahajjata Kuɗin Guzurinsu A Hannu

LABARAI MASU NASABA

Batun AI Zai Fi Daukar Hankali A Bikin Baje Kolin Fasahar Zamani Ta Duniya Karo Na 5

Batun AI Zai Fi Daukar Hankali A Bikin Baje Kolin Fasahar Zamani Ta Duniya Karo Na 5

September 8, 2026
Gwamna Radda Ya Samu Goyon Bayan APC A Katsina Gabanin Zaɓen 2027

Gwamna Radda Ya Samu Goyon Bayan APC A Katsina Gabanin Zaɓen 2027

September 8, 2026
Cinikin Wajen Sin Ya Ci Gaba Da Samun Bunkasa Cikin Sauri A Watanni Takwas Na Farkon Bana

Cinikin Wajen Sin Ya Ci Gaba Da Samun Bunkasa Cikin Sauri A Watanni Takwas Na Farkon Bana

September 8, 2026
'Yan Bindiga

‘Yan Bindiga Sun Kashe 2, Sun Yi Garkuwa Da 26 A Kaduna

September 8, 2026
Binciken CGTN Ya Nuna Gamsuwa Da Yadda Baje Kolin CIFTIS Ke Shaida Karfin Gwiwar Sin A Fannin Kara Fadada Bude Kofa Bisa Babban Matsayi

Binciken CGTN Ya Nuna Gamsuwa Da Yadda Baje Kolin CIFTIS Ke Shaida Karfin Gwiwar Sin A Fannin Kara Fadada Bude Kofa Bisa Babban Matsayi

September 8, 2026
Yadda Taron Tattalin Arziki Da Zuba Jari Na Kwana Biyu Ya Gudana A Katsina

Gwamna Radda Ya Gabatar Da Kasafin N828.6bn Na 2027

September 8, 2026
Sin Za Ta Yi Aiki Tare Da Sassa Daban Daban Domin Mayar Da Fasahar AI Wata Dama Ta Cin Gajiya Mai Dorewa

Sin Za Ta Yi Aiki Tare Da Sassa Daban Daban Domin Mayar Da Fasahar AI Wata Dama Ta Cin Gajiya Mai Dorewa

September 8, 2026
Gwamnan Kebbi Ya Bayyana Shirin Sake Duba Albashin Malaman Firamare

Gwamna Idris Ya Rushe Majalisar Shugabannin Hukumar Zaɓe Ta Kebbi

September 8, 2026
Han Zheng Ya Halarci Baje Kolin CIFIT Karo Na 26 Tare Da Gabatar Da Jawabi

Han Zheng Ya Halarci Baje Kolin CIFIT Karo Na 26 Tare Da Gabatar Da Jawabi

September 8, 2026
Wani Soja Ya Kashe Kansa Bayan Kashe Matarsa A Jihar Neja

Kano Za Ta Kafa Sansanonin Sojoji A Ƙananan Hukumomin Da Ke Fuskantar Barazanar Tsaro

September 8, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.