A daidai lokacin harkokin siyasa suka kankama, ‘yan siyasa daga bangaren masu mulki da kuma bangaren ‘yan adawa sunata fafutukar ganin sun tabbata a kan karagar mulki ko kuma sun kwace ragamar mulki a matakai daban-daban a fadin tarayyar kasar nan, wani shaharren Malamin addinin Musulunci da ke garin Kano wanda kuma shi ne Shugaban Kungiyar Masu Ilimin Taurari na Nahiyar Afrika Sheikh Muhajjadina Sani Kano ya nemi ‘yan siyasa su kai zuciyar su kai nesa tare da nisantar kalaman batanci da duk wani abin da zai iya ruguje ginshikan zaman lafiya da tattalin arzikin kasar nan.
Sheikh Muhajjadina ya yi wannan bayanin ne a tattaunawarsa da manema labarai a ofishinsa da ke Abuja. Ya ce, wannan kiran ya zama dole musamman ganin yadda fagen harkokin siyasar kasar ke daukar zafi, a inda bangarori daban-daban ke kokari kama madafun iko ta kowacce hanya.
“A ‘yan kwanakin nan ‘yan siyasa suna ta sauya sheka daga jam’iyyar siyasa zuwa wata, hakan ya sa wasu ke ganin an ci amanar su, wasu kuma na ganin tsawon shekara 4 da wasu suka yi suna mulki ba a kyauta musu ba saboda haka za su tabbatar da sauyi ko ta halin kaka” in ji shi
Ya kara da cewa, wannan mataki yana da hadari ga rayuwar kasar nan ta bangarori da dama musamman ganin dama kasar na fama harkokin ‘yan bindiga da ‘yan ta’adda a jihohi da dama ga shi kuma muna fuskantar matsalar tattalin arziki sakamakon matakai da tsare-tsaren gwamnati mai mulki, a wannan lokaci ne kuma muke bukatar ganin ba a samu wanin abin da za su tayar da hankula ba.
Ya kuma yi kira ga ‘yan siyasa da al’umma gaba daya da su kusanci masu ilimin Taurari domin neman fassara da shawarwwari a kan abubuwan da suke fuskanta. Ya ce tabbas akwai kalubale a gaban shugabannin kasar nan amma cikin ikon Allah “Za mu yi nasarar kawo karshen matsalar tsaro da tattalin arzikin da muke fuskanta a yanzu” in ji shi
Daga karshe ya nemi ‘yan Nijeriya masu zabe da su natsu sosai tare da nazarin wadanda za su zaba a dukkan matakai, “Bai kamata mutum ya biye ma Taliya ko kudi dan kalilan wajen zaben wanda zai hau karagar mulki na tsawon shekara 4 ba. Kamata ya yi a duba mutumin da ya fi cancanta wanda zai kawo ayyukan raya kasa. ‘ in ji shi.















Discussion about this post