Hukumar Zaɓe Mai Zaman Kanta ta Ƙasa,(INEC), ta sabunta rajistarta na shugabannin jam’iyyun siyasa inda ta sake sanya tsohon Shugaban Majalisar Dattawa, David Mark, a matsayin shugaban jam’iyyar African Democratic Congress (ADC).
Hakanan, tsohon gwamnan Jihar Osun, Rauf Aregbesola, an jera shi a matsayin sakataren jam’iyyar na ƙasa, tare da wasu shugabanni ciki har da Mani Ahmad a matsayin ma’aji, Akibu Dalhatu a matsayin sakataren kuɗi, da Farfesa Oserheimen Osunbor a matsayin mai ba da shawara kan harkokin shari’a.
Matakin ya biyo bayan hukuncin da Kotun ƙolin ta yanke a ranar Alhamis, wanda ya shafi rikicin shugabanci a jam’iyyar ADC.
Wannan sabuntawa ya soke matakin da INEC ta ɗauka a farkon watan Afrilu, lokacin da ta cire sunayen shugabancin ɓangaren David Mark daga shafinta, bisa wani hukuncin kotun ɗaukaka ƙara da ya shafi rikicin.
Hukuncin kotun ƙoli ya kuma soke umarnin komawa tsarin da “status quo ante bellum” da ya dakatar da batun shugabanci, tare da umartar a mayar da shari’ar zuwa Kotun Tarayya domin ci gaba da sauraron ƙarar.














Discussion about this post