ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Thursday, June 25, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

A Dauki Matakin Da Ya Dace Bayan Bayyana Masu Daukar Nauyin Ta’addanci

by Leadership Hausa
2 years ago
Ta’addanci

Daga karshe dai gwamnatin tarayya ta saurari kiraye kirayen ‘yan Nijeriya suka yi na neman a bayyana sunayen wadanda ke daukar nauyin ayyukan ta’addanci a fadin kasar nan, abin da ya kamata ta yi shekaru masu yawa da suka wuce. An jirkirta bayyana sunayen wadanda suke daukar nauyin ‘yan ta’adda ne saboda wasu dalilai da suka hada da na siyasa, musamman a lokacin mulkin Shugaban Kasa Muhammadu Buhari. Shawarar da kasar Hadaddiyar Daular Larabawa (UAE) ta yanke na bayyana sunayen wasu ‘yan Nijeriyan da ke hada baki da su wajen daukar nauyin masu aikata ta’addanci a Nijeriya bai zaburar da gwamnati ba wajen yin abin da ya kamata har sai a makon jiya da Hukumar Kula da Yadda Ake Sarrafa Kudi (NFIU), ta yi bayani, inda ta sanar da cewa, wasu mutane 9 da cibiyoyin canjin kudi 6 suke daukar nauyin ta’addanci a Nijeriya.

A kan haka ne dole a yaba wa Shugaban Kasa Bola Ahmed Tinubu saboda karfin halin da ya yi na bayyana sunayen. Haka kuma ya kamata a yaba wa Shugaba Tinubu a kan yadda jami’an tsaro suka gayyaci Sheik Gumi don ya yi masu bayanin abin da ya sani game da yadda ‘yan ta’addar ke gudanar da harkokinsu.
Sanannen Malamin addinin musuluncin nan mazaunin jihar Kaduna dakta Ahmad Gumi yana kan gaba na kira da a rika tattaunawa da ‘yan ta’addar don ganin sun sako wadanda suka yi garkuwa da su, ya nuna rashin amincewarsa a kan yadda gwamnati ke amfani da karfi a kan ‘yan bindiga, inda ya yi gargadin al’amurra na iya tabarbarewa in har ba a yi abin da ya kamata ba.

  • Kasar Sin Na Bayar Da Cikakken Goyon-Baya Ga Pakistan Wajen Yakar Ta’addanci
  • ‘Yan Bindiga Sun Kashe Mutum 5, Sun Saki 51 Bayan Biyan Fansa A Kaduna

Ita kuwa hukuma, a takardar sanarwar da ta fito da ita a ranar 18 ga watan Maris 2024 ta bayyana sunayen wasu kamfanonin canjin kudi da wasu mutane masu zaman kansu da ke daukar nauyin ayyukan ta’addanci a Nijeriya inda ta ba da shawarar a dauki matakin hukunci a kan su ba tare da bata wani lokaci ba.

ADVERTISEMENT

Cikin wadanda aka sanar da sunayensu, wanda ya fi yin fice daga ciki shi ne mawallafin nan na Kaduna, Tukur Mamu, sunan shi yana cikin jerin masu daukar nauyin ta’addancin ne saboda yadda ya jagoranci karbar kudaden da suka kai Dala 200,000 na kudin fansa a kan mutanen da aka sace a kan jirgin kasan nan da ya taso daga Abuja zuwa Kaduna wadanda ‘yan ta’addar ISWAP suka sace. Idan za a iya tunawa a halin yanzu gwamnati ta gurfanar da Mamu a gaban kotu a kan laifin tallafa wa ‘yan ta’addar a harin da suka kai wa jirgin da ya taso daga Abuja zuwa Kaduna watan Maris na shekarar 2022.

Bayan kasancewar su mambobi a wasu manya-manyan kungiyoyin ‘yan ta’adda na duniya wadanda aka bayyana sunayen su sun kasance cikin wadanda ake zargi da hannu a hare-haren ta’addanci da aka kai Cocin St. Francis Catholic Church na garin Owo,Jihar Ondo a ranar 5 ga watan Yuni na shekarar 2022 da wanda aka kai gidan yarin Kuje da ke Abuja a ranar 5 ga watan Yuli 2022.

LABARAI MASU NASABA

Yadda Uba Sani Ya Farfaɗo Da Asibitin Da Aka Yi Watsi Da Shi Tsawon Shekaru 40 – Hakimin Makarfi

Dandalin DAVOS Na Bana: Fage Ne Da “Kirkire-Kirkiren Sin” Ya Sadu Da “Kyakkyawan Fatan Afirka”

Amma kuma abin lura a nan shi ne al’ummar Nijeriya basu nuna zakuwa ba da jin dadin bayanin da aka yi na bayyana sunayen masu daukar ayyukan ta’addanci, wannan kuma ya faru ne saboda a baya an sha kama manya-manyan masu garkuwa da mutane amma sai ta kasance iyakar labarin Kenan.

Alal misali a shekarar 2022, gwamnatin tarayya ta sanar da kasancewar kungiyoyi 96 da suke ayyukan tallafa wa ‘yan ta’addar Boko a kasar nan. Ministan yada labarai na wancan lokacin ya bayyana wa duniya a wani taron manema labaran da ya kira a Abuja inda ya ce, gwamnati ta gano kamfanoni 123 da cibiyoyin canji 33 da aka tabbatar da suna taimaka wa ‘yan ta’addar. An kuma kama masu garkuwa da mutane 26 da masu taimaka musu mutum 7.

Bugu da kari Ministan ya ce, an kama mutum 45 da suke daukar nauyin ta’addanci,kuma za a gaggauta hukunta su amma ba mu sake jin wani bayani a kan lamarin ba sai a wannan lokacin kuma ba mu ji an hukunta wani ko wata ba har zuwa wannan lokacin.

A shekarar ne kuma gwamnati ta kara fadada aikin binciko da sa ido a kan masu daukar nauyin ta’addanci inda ajka bayar da umarnin sa ido don gano yadda kudi ke zirga-zirga a tsakanin ‘yan ta’adda da masu daukar nauyin su.

A ra’ayinmu bai kamata a zargi wannan gwamnatin ba a kan mastalolin da ta gada shekara da shekaru, musamman ma ganin lamarin ayyukan ta’addanci ya dade a kasa ya kuma samu wuri ya zauna a yankuna daban-daban na kasar nan.Abu ne da yake bukatar kowa ya bayar da tasa gudummawar don ganin an samu nasarar yaki da dukkan nau’oin ta’addanci.

A kan haka ne ya zama dole ga wannan gwamnati ta tsaya wajen ganin an hukunta dukkan wadanda aka samu da hannu a daukar nauyin ta’addancin, ta haka ne za a iya tabbatar da cewa, lallai gwamnatin da gaske take yi.Haka kuma ya kamata dukkan rundunonin tsaronmu su hada kai tare da aiki tare.Ana kuma bukatar ‘yan Nijeriya su taimaka wajen bayar da bayanan sirri da za su kai ga sa an bankado ayyukan masu garkuwa da mutane a duk inda suke a fadin tarayyar kasar nan.

Ta’addanci
Leadership Hausa
Website |  + postsBio
  • Leadership Hausa
    Batun Dakile Shan Taba Sigari A Tsakanin Yara A Nijeriya
  • Leadership Hausa
    Har Yanzu Akwai Sauran Rina A Kaba Game Da Makomar Yara A Nijeriya
  • Leadership Hausa
    Yadda Arsenal Ta Lashe Gasar Firimiya Bayan Shekara 22
  • Leadership Hausa
    Bukatar Kawo Karshen Akidar Kyamar Baki A Kasar Afirka Ta Kudu

MASU ALAKA

Yadda Uba Sani Ya Farfaɗo Da Asibitin Da Aka Yi Watsi Da Shi Tsawon Shekaru 40 – Hakimin Makarfi
Labarai

Yadda Uba Sani Ya Farfaɗo Da Asibitin Da Aka Yi Watsi Da Shi Tsawon Shekaru 40 – Hakimin Makarfi

June 24, 2026
Dandalin DAVOS Na Bana: Fage Ne Da “Kirkire-Kirkiren Sin” Ya Sadu Da “Kyakkyawan Fatan Afirka”
Ra'ayi Riga

Dandalin DAVOS Na Bana: Fage Ne Da “Kirkire-Kirkiren Sin” Ya Sadu Da “Kyakkyawan Fatan Afirka”

June 24, 2026
Tsaro: Dasuki Ya Bukaci Tinubu Ya Gyara Alaka Da Nijar Domin Kare Iyakokin Arewa-Maso-Yamma
Labarai

Tsaro: Dasuki Ya Bukaci Tinubu Ya Gyara Alaka Da Nijar Domin Kare Iyakokin Arewa-Maso-Yamma

June 24, 2026
Next Post
nijeriya

Jerin Manyan Attajiran Nijeriya A 2024

LABARAI MASU NASABA

Dokar Sin Ta Gurfanar Da Masu Rajin Ballewar Kabilun Kasar Da Ke Kasashen Waje Ta Dace

Dokar Sin Ta Gurfanar Da Masu Rajin Ballewar Kabilun Kasar Da Ke Kasashen Waje Ta Dace

June 24, 2026
’Yan Kasuwa Na Kasashen Waje Sun Yaba Wa Yanayin Kasuwanci Na Sin

’Yan Kasuwa Na Kasashen Waje Sun Yaba Wa Yanayin Kasuwanci Na Sin

June 24, 2026
Yadda Uba Sani Ya Farfaɗo Da Asibitin Da Aka Yi Watsi Da Shi Tsawon Shekaru 40 – Hakimin Makarfi

Yadda Uba Sani Ya Farfaɗo Da Asibitin Da Aka Yi Watsi Da Shi Tsawon Shekaru 40 – Hakimin Makarfi

June 24, 2026
Dandalin DAVOS Na Bana: Fage Ne Da “Kirkire-Kirkiren Sin” Ya Sadu Da “Kyakkyawan Fatan Afirka”

Dandalin DAVOS Na Bana: Fage Ne Da “Kirkire-Kirkiren Sin” Ya Sadu Da “Kyakkyawan Fatan Afirka”

June 24, 2026
Binciken CGTN: Amfanarwa A Aikace Shi Ne Nagartaccen Ma’aunin Tantance Ainihin Kimar Sabbin Fasahohi

Binciken CGTN: Amfanarwa A Aikace Shi Ne Nagartaccen Ma’aunin Tantance Ainihin Kimar Sabbin Fasahohi

June 24, 2026
Kasar Sin Na Kara Zama Babban Ginshikin Ci Gaban Tattalin Arzikin Duniya Na Gaba

Kasar Sin Na Kara Zama Babban Ginshikin Ci Gaban Tattalin Arzikin Duniya Na Gaba

June 24, 2026
Tsaro: Dasuki Ya Bukaci Tinubu Ya Gyara Alaka Da Nijar Domin Kare Iyakokin Arewa-Maso-Yamma

Tsaro: Dasuki Ya Bukaci Tinubu Ya Gyara Alaka Da Nijar Domin Kare Iyakokin Arewa-Maso-Yamma

June 24, 2026
Sabbin Ministoci

Kafa ‘Yansandan Jihohi: Majalisa Ta Amince Da Tsarin ‘Yar Tinƙe Wajen Kaɗa Ƙuri’a 

June 24, 2026
Sin Ta Gabatar Da Tsarin Karfafa Kwarin Gwiwar Kamfanoni Masu Jarin Waje

Sin Ta Gabatar Da Tsarin Karfafa Kwarin Gwiwar Kamfanoni Masu Jarin Waje

June 24, 2026
Shugaban Kasar Burundi: Dangantakar Afirka Da Sin Misali Ce Ta Hadin Gwiwar Kasashe Masu Tasowa

Shugaban Kasar Burundi: Dangantakar Afirka Da Sin Misali Ce Ta Hadin Gwiwar Kasashe Masu Tasowa

June 24, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.