Shugaban Ƙasa, Bola Ahmed Tinubu, ya isa birnin Nairobi na ƙasar kenya, domin halartar taron nahiyar Afirka kan tattalin arziki da nufin bunƙasa haɗin gwiwa da ci gaba mai ɗorewa a faɗin nahiyar Afirka.
A cewar wata sanarwa da Mai Bai wa Shugaban Ƙasa Shawara na Musamman kan Yaɗa Labarai da Tsare-tsare, Bayo Onanuga, ya fitar, jirgin Shugaba Tinubu ya sauka a Filin Jirgin Sama na Jomo Kenyatta da misalin ƙarfe 12:18 na dare agogon ƙasar a ranar Litinin.
Bayan isowarsa, jami’in harkokin ƙasashen waje da hulɗa da ‘yan ƙasar waje na Kenya, Musalia Mudavadi, tare da Babban Kwamishinan Kenya a Nijeriya, Isaac Parashina, da sauran manyan jami’an gwamnatin Kenya da membobin tawagar diflomasiyyar Nijeriya a Kenya suka tarbe shi.Sanarwar ta bayyana cewa shugaban ƙasar Kenya, William Ruto, da takwaransa ns Faransa, Emmanuel Macron, ne za su jagoranci ɗaukar nauyin taron tare.
Ya ƙara da cewa taron na tattalin arzikin Nahiyar Afirka ya haɗa shugabannin ƙasashe, masu tsara manufofi, shugabannin kamfanoni, abokan hulɗar ci gaba da sauran masu ruwa da tsaki daga sassa daban-daban na Afirka da ma duniya baki ɗaya.
Haka kuma, mai taimaka wa shugaban ƙasar ya bayyana cewa ana sa ran Shugaba Tinubu, zai gudanar da manyan ganawa na ƙasashe biyu da kuma na ƙasashe da dama yayin taron. Ya ce halartar shugaban ƙasar na nuna ƙudirin gwamnatinsa wajen inganta hanyoyin magance matsalolin Afirka ta hanyar Afirka kanta, tare da ciyar da Muradin Renewed Hope gaba ta hanyar ƙarfafa hulɗar ƙasa da ƙasa cikin hikima.















Discussion about this post