ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Wednesday, September 9, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Achraf Hakimi: Sabon Angon Afrika A Harkar Ƙwallon Ƙafa

by Sadiq
10 months ago
Hakimi

Achraf Hakimi ba ɗan wasan baya ba ne kaɗai, fitaccen ɗan wasan Afrika ne wanda tauraronsa ya haska a duniya. A makon da ya gabata ne, ya lashe Gwarzon Ɗan Ƙwallon Afrika na 2025, wanda ya zama ɗan baya na farko cikin shekaru 52 da ya samu wannan lambar yabo.

Tarihin Rayuwarsa

An haifi Hakimi a Birnin Madrid na ƙasar Sifaniya a shekarar 1998, asalin iyayensa ‘yan ƙasar Maroko ne. Ya taso a unguwar talakawa da ke Getafe. Tun farkon ƙuruciyarsa yaro ne mai son taka leda, kuma bai daɗe ba ƙwarewarsa ta kai shi ƙungiyar matasa ta Real Madrid. A nan ne ya fara samun horo da gogewa.

  • Dalilin Da Ya Sa Muka Tafi Amurka Don Taron Tsaro – Gwamna Radda
  • Gwamnatin Tarayya Ta Umarci A Fara Karatun Digiri Da Yaren Tibi Da Nupe A Jami’o’i

Tauraronsa Ya Haska A Turai

Hakimi ya yi fice sosai lokacin da Real Madrid ta kai shi aro zuwa Borussia Dortmund. A nan ne ya nuna kalar ƙwarewarsa wajen murza leda: tare ƙwallo a matsayin ɗan wasa baya tare da kai-hari, gudu, da iya sarrafa kwallo.

ADVERTISEMENT

Daga Dortmund ya koma Inter Milan, inda ya samu sabbin dabarun sarrafa ƙwallo a fili, ya kuma taimaka wa ƙungiyar wajen samun manyan nasarori. Daga bisani ya koma Paris Saint-Germain (PSG), inda ya tauraronsa ya ƙara haskakawa sosai.

A PSG, Hakimi bai tsaya taka ƙwalla a matsayin ɗan baya ba kaɗai, yana taimakawa wajen zura ƙwallaye a ragar abokan hamayya, yana kai farmaki, kuma ya kasance ɗaya daga cikin manyan taurarin ƙungiyar.

LABARAI MASU NASABA

Ballon d’Or: Messi, Yamal, Da Mane Na Cikin ‘Yan Wasa 30 Da Aka Zaɓo

Ƙungiyoyi 5 Da Ke Takarar Gwarzuwar Ƙungiya Ta Bana

Ɗaga Martabar Tawagar ‘Yan Wasan Maroko

Hakimi na taka leda ne a tawagar ‘yan wasan Maroko, kuma wannan shi ne abin da ya fi alfahari da shi. A Gasar Cin Kofin Duniya ta 2022, ya taka muhimmiyar rawa da ta kai Maroko zuwa matakin kusa da na ƙarshe, wanda babban abun alfahari ne ga ƙasar da kuma Afrika.

Hakimi kuma mutum ne mai matuƙar son kasancewa iyayensa. Bayan buga wasanni, ya kan tafi ya rungumi mahaifiyarsa a filin wasa, wanda hakan ya a taɓa zuciyar masoyansa sosai.

Shekarar Da Ya Kafa Tarihi A PSG

A 2025, Hakimi ya taka wasa mai ban mamaki tare da PSG. Ya lashe gasar zakarun Turai ta Champions League, Ligue 1, Coupe de France, da UEFA Super Cup. Wannan gagarumar nasara ta sa ya doke fitattun ‘yan wasa kamar Mohamed Salah da Victor Osimhen, wajen lashe Gwarzon Ɗan Ƙwallon Afrika na 2025.

A jawabin karɓar kyautarsa, ya ce wannan lambar yabo “ba tawa ba ce ni kaɗai, ta dukkanin matasa maza da mata masu mafarkin zama ‘yan wasa a Afrika ce.”

Halayyarsa A Wajen Filin Wasa

A zahiri, Hakimi mutum ne mai nutsuwa da ladabi. Abokan wasansa suna yaba masa kan yadda halinsa da aiki tuƙuru yake. Ba ya son hayaniya ko jita-jita, aikinsa a fili shi ne yake bayyana wanw irin mutum ne.

Burin Da Ya Cimma

Zama Gwarzon Ɗan Ƙwallon Afrika a matsayin ɗan baya babban tarihi ne. Ya nuna irin ci gaban da Hakimi ya yi fatan samu a harkar ƙwallon ƙafa. Ya nuna cewa ko a ɓangaren ‘yan wasan baya, akwai gurbin taurari kamarsa.

Yanzu Hakimi yana da shekaru 27 kacal a duniya, amma ya kafa tarihin da zai daɗe ana tunawa da shi. Ɗan wasa ne da ke tsakanin Turai da Afrika, wanda ke nuna ƙwarewarsa a kowace nahiya ya tsinci kansa. Kuma babu shakka, labarinsa ya nuna yadda jajircewa da himma suka kai shi ga zama tauraro.

MASU ALAKA

Ballon D'or
Manyan Labarai

Ballon d’Or: Messi, Yamal, Da Mane Na Cikin ‘Yan Wasa 30 Da Aka Zaɓo

September 8, 2026
Ƙungiyoyi 5 Da Ke Takarar Gwarzuwar Ƙungiya Ta Bana
Wasanni

Ƙungiyoyi 5 Da Ke Takarar Gwarzuwar Ƙungiya Ta Bana

September 8, 2026
Kofin Duniya: Yau Falconets Za Su Kece Raini Da Spain
Wasanni

Kofin Duniya: Yau Falconets Za Su Kece Raini Da Spain

September 7, 2026
Next Post
An Bude Dandalin Tunis Na Bunkasa Hadin Gwiwar Ayyukan Likitanci Tsakanin Sin Da Afirka

An Bude Dandalin Tunis Na Bunkasa Hadin Gwiwar Ayyukan Likitanci Tsakanin Sin Da Afirka

LABARAI MASU NASABA

Sojoji

Sojoji Sun Dakile Hare-Hare, Sun Ceto Mutane 12 A Zamfara

September 9, 2026
Batun AI Zai Fi Daukar Hankali A Bikin Baje Kolin Fasahar Zamani Ta Duniya Karo Na 5

Batun AI Zai Fi Daukar Hankali A Bikin Baje Kolin Fasahar Zamani Ta Duniya Karo Na 5

September 8, 2026
Gwamna Radda Ya Samu Goyon Bayan APC A Katsina Gabanin Zaɓen 2027

Gwamna Radda Ya Samu Goyon Bayan APC A Katsina Gabanin Zaɓen 2027

September 8, 2026
Cinikin Wajen Sin Ya Ci Gaba Da Samun Bunkasa Cikin Sauri A Watanni Takwas Na Farkon Bana

Cinikin Wajen Sin Ya Ci Gaba Da Samun Bunkasa Cikin Sauri A Watanni Takwas Na Farkon Bana

September 8, 2026
'Yan Bindiga

‘Yan Bindiga Sun Kashe 2, Sun Yi Garkuwa Da 26 A Kaduna

September 8, 2026
Binciken CGTN Ya Nuna Gamsuwa Da Yadda Baje Kolin CIFTIS Ke Shaida Karfin Gwiwar Sin A Fannin Kara Fadada Bude Kofa Bisa Babban Matsayi

Binciken CGTN Ya Nuna Gamsuwa Da Yadda Baje Kolin CIFTIS Ke Shaida Karfin Gwiwar Sin A Fannin Kara Fadada Bude Kofa Bisa Babban Matsayi

September 8, 2026
Yadda Taron Tattalin Arziki Da Zuba Jari Na Kwana Biyu Ya Gudana A Katsina

Gwamna Radda Ya Gabatar Da Kasafin N828.6bn Na 2027

September 8, 2026
Sin Za Ta Yi Aiki Tare Da Sassa Daban Daban Domin Mayar Da Fasahar AI Wata Dama Ta Cin Gajiya Mai Dorewa

Sin Za Ta Yi Aiki Tare Da Sassa Daban Daban Domin Mayar Da Fasahar AI Wata Dama Ta Cin Gajiya Mai Dorewa

September 8, 2026
Gwamnan Kebbi Ya Bayyana Shirin Sake Duba Albashin Malaman Firamare

Gwamna Idris Ya Rushe Majalisar Shugabannin Hukumar Zaɓe Ta Kebbi

September 8, 2026
Han Zheng Ya Halarci Baje Kolin CIFIT Karo Na 26 Tare Da Gabatar Da Jawabi

Han Zheng Ya Halarci Baje Kolin CIFIT Karo Na 26 Tare Da Gabatar Da Jawabi

September 8, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.