ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Thursday, July 16, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Achraf Hakimi: Sabon Angon Afrika A Harkar Ƙwallon Ƙafa

by Sadiq
8 months ago
Hakimi

Achraf Hakimi ba ɗan wasan baya ba ne kaɗai, fitaccen ɗan wasan Afrika ne wanda tauraronsa ya haska a duniya. A makon da ya gabata ne, ya lashe Gwarzon Ɗan Ƙwallon Afrika na 2025, wanda ya zama ɗan baya na farko cikin shekaru 52 da ya samu wannan lambar yabo.

Tarihin Rayuwarsa

An haifi Hakimi a Birnin Madrid na ƙasar Sifaniya a shekarar 1998, asalin iyayensa ‘yan ƙasar Maroko ne. Ya taso a unguwar talakawa da ke Getafe. Tun farkon ƙuruciyarsa yaro ne mai son taka leda, kuma bai daɗe ba ƙwarewarsa ta kai shi ƙungiyar matasa ta Real Madrid. A nan ne ya fara samun horo da gogewa.

  • Dalilin Da Ya Sa Muka Tafi Amurka Don Taron Tsaro – Gwamna Radda
  • Gwamnatin Tarayya Ta Umarci A Fara Karatun Digiri Da Yaren Tibi Da Nupe A Jami’o’i

Tauraronsa Ya Haska A Turai

Hakimi ya yi fice sosai lokacin da Real Madrid ta kai shi aro zuwa Borussia Dortmund. A nan ne ya nuna kalar ƙwarewarsa wajen murza leda: tare ƙwallo a matsayin ɗan wasa baya tare da kai-hari, gudu, da iya sarrafa kwallo.

ADVERTISEMENT

Daga Dortmund ya koma Inter Milan, inda ya samu sabbin dabarun sarrafa ƙwallo a fili, ya kuma taimaka wa ƙungiyar wajen samun manyan nasarori. Daga bisani ya koma Paris Saint-Germain (PSG), inda ya tauraronsa ya ƙara haskakawa sosai.

A PSG, Hakimi bai tsaya taka ƙwalla a matsayin ɗan baya ba kaɗai, yana taimakawa wajen zura ƙwallaye a ragar abokan hamayya, yana kai farmaki, kuma ya kasance ɗaya daga cikin manyan taurarin ƙungiyar.

LABARAI MASU NASABA

Na Yi Tsayin-daka Domin Cika Alƙawarin Ƙasata Nijeriya

FIFA Na Nazarin Faɗaɗa Gasar Kofin Duniya Zuwa Ƙasashe 64

Ɗaga Martabar Tawagar ‘Yan Wasan Maroko

Hakimi na taka leda ne a tawagar ‘yan wasan Maroko, kuma wannan shi ne abin da ya fi alfahari da shi. A Gasar Cin Kofin Duniya ta 2022, ya taka muhimmiyar rawa da ta kai Maroko zuwa matakin kusa da na ƙarshe, wanda babban abun alfahari ne ga ƙasar da kuma Afrika.

Hakimi kuma mutum ne mai matuƙar son kasancewa iyayensa. Bayan buga wasanni, ya kan tafi ya rungumi mahaifiyarsa a filin wasa, wanda hakan ya a taɓa zuciyar masoyansa sosai.

Shekarar Da Ya Kafa Tarihi A PSG

A 2025, Hakimi ya taka wasa mai ban mamaki tare da PSG. Ya lashe gasar zakarun Turai ta Champions League, Ligue 1, Coupe de France, da UEFA Super Cup. Wannan gagarumar nasara ta sa ya doke fitattun ‘yan wasa kamar Mohamed Salah da Victor Osimhen, wajen lashe Gwarzon Ɗan Ƙwallon Afrika na 2025.

A jawabin karɓar kyautarsa, ya ce wannan lambar yabo “ba tawa ba ce ni kaɗai, ta dukkanin matasa maza da mata masu mafarkin zama ‘yan wasa a Afrika ce.”

Halayyarsa A Wajen Filin Wasa

A zahiri, Hakimi mutum ne mai nutsuwa da ladabi. Abokan wasansa suna yaba masa kan yadda halinsa da aiki tuƙuru yake. Ba ya son hayaniya ko jita-jita, aikinsa a fili shi ne yake bayyana wanw irin mutum ne.

Burin Da Ya Cimma

Zama Gwarzon Ɗan Ƙwallon Afrika a matsayin ɗan baya babban tarihi ne. Ya nuna irin ci gaban da Hakimi ya yi fatan samu a harkar ƙwallon ƙafa. Ya nuna cewa ko a ɓangaren ‘yan wasan baya, akwai gurbin taurari kamarsa.

Yanzu Hakimi yana da shekaru 27 kacal a duniya, amma ya kafa tarihin da zai daɗe ana tunawa da shi. Ɗan wasa ne da ke tsakanin Turai da Afrika, wanda ke nuna ƙwarewarsa a kowace nahiya ya tsinci kansa. Kuma babu shakka, labarinsa ya nuna yadda jajircewa da himma suka kai shi ga zama tauraro.

MASU ALAKA

Na Yi Tsayin-daka Domin Cika Alƙawarin Ƙasata Nijeriya
Rahotonni

Na Yi Tsayin-daka Domin Cika Alƙawarin Ƙasata Nijeriya

July 14, 2026
FIFA Na Nazarin Faɗaɗa Gasar Kofin Duniya Zuwa Ƙasashe 64
Wasanni

FIFA Na Nazarin Faɗaɗa Gasar Kofin Duniya Zuwa Ƙasashe 64

July 12, 2026
Harry Kane: Lashe Kofin Duniya Ya Fi Mini Muhimmanci Fiye da Takalmin Zinare
Wasanni

Harry Kane: Lashe Kofin Duniya Ya Fi Mini Muhimmanci Fiye da Takalmin Zinare

July 11, 2026
Next Post
An Bude Dandalin Tunis Na Bunkasa Hadin Gwiwar Ayyukan Likitanci Tsakanin Sin Da Afirka

An Bude Dandalin Tunis Na Bunkasa Hadin Gwiwar Ayyukan Likitanci Tsakanin Sin Da Afirka

LABARAI MASU NASABA

Binciken CGTN: Amfanar Da Kowa Da Kowa Shi Ne Ainihin Alherin Da Fasahohin Kwaikwayon Tunanin Bil Adama Suka Kawo

Binciken CGTN: Amfanar Da Kowa Da Kowa Shi Ne Ainihin Alherin Da Fasahohin Kwaikwayon Tunanin Bil Adama Suka Kawo

July 15, 2026
Sin Ta Yi Kira Da A Kafa Tsarin Jagorantar Muhimman Ma’adinai Ga Sauyawa Zuwa Amfani Da Makamashi Mai Tsafta

Sin Ta Yi Kira Da A Kafa Tsarin Jagorantar Muhimman Ma’adinai Ga Sauyawa Zuwa Amfani Da Makamashi Mai Tsafta

July 15, 2026
Gwamna Dauda Lawal Zai Gabatar Da Jawabi A Taron Ƙasa Da Ƙasa Na Jami’ar FUE Zariya

Gwamna Dauda Lawal Zai Gabatar Da Jawabi A Taron Ƙasa Da Ƙasa Na Jami’ar FUE Zariya

July 15, 2026
Neman Raba-Gari Da Sauran Kasashe Zai Kawo Mummuann Tasiri Ga Bangarorin Da Abin Ya Shafa

Neman Raba-Gari Da Sauran Kasashe Zai Kawo Mummuann Tasiri Ga Bangarorin Da Abin Ya Shafa

July 15, 2026
Kevin Kelly: AI Na Iya Taimakawa Wajen Cimma Burin “Koyar Da Dalibai Da Kwazonsu”

Kevin Kelly: AI Na Iya Taimakawa Wajen Cimma Burin “Koyar Da Dalibai Da Kwazonsu”

July 15, 2026
Gwamna Yusuf Ya Bai Wa Masu Kula Da Akwatinan Zaɓe Na APC Filaye 1,540 Da Tallafin Miliyan 100

Gwamna Yusuf Ya Bai Wa Masu Kula Da Akwatinan Zaɓe Na APC Filaye 1,540 Da Tallafin Miliyan 100

July 15, 2026
Sabbin Ministoci

Rashin Tsaro: Majalisar Dattawa Ta Bukaci A Tura Ƙarin Sojoji da ’Yansanda Zuwa Benuwe

July 15, 2026
GDPn Sin A Rabin Farko Na Shekarar 2026 Ya Karu Da Kashi 4.7% Idan Aka Kwatanta Da Na Kwatankwacin Lokacin Bara

GDPn Sin A Rabin Farko Na Shekarar 2026 Ya Karu Da Kashi 4.7% Idan Aka Kwatanta Da Na Kwatankwacin Lokacin Bara

July 15, 2026
‘Yansanda Sun Tsaurara Tsaron Iyakokin Kano Bayan Hare-haren ‘Yan Bindiga 

Atiku Ya Nuna Damuwa Kan Kasafin Naira Biliyan 6.44 Don Gasar Cin Kofin Duniya ta 2026

July 15, 2026
Masana Kandagarkin Cututtuka Na Sin Sun Tashi Zuwa Kasar Uganda Don Aikin Hadin Gwiwar Magance Cutar Ebola

Masana Kandagarkin Cututtuka Na Sin Sun Tashi Zuwa Kasar Uganda Don Aikin Hadin Gwiwar Magance Cutar Ebola

July 15, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.