ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Thursday, June 4, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Achraf Hakimi: Sabon Angon Afrika A Harkar Ƙwallon Ƙafa

by Sadiq
6 months ago
Hakimi

Achraf Hakimi ba ɗan wasan baya ba ne kaɗai, fitaccen ɗan wasan Afrika ne wanda tauraronsa ya haska a duniya. A makon da ya gabata ne, ya lashe Gwarzon Ɗan Ƙwallon Afrika na 2025, wanda ya zama ɗan baya na farko cikin shekaru 52 da ya samu wannan lambar yabo.

Tarihin Rayuwarsa

An haifi Hakimi a Birnin Madrid na ƙasar Sifaniya a shekarar 1998, asalin iyayensa ‘yan ƙasar Maroko ne. Ya taso a unguwar talakawa da ke Getafe. Tun farkon ƙuruciyarsa yaro ne mai son taka leda, kuma bai daɗe ba ƙwarewarsa ta kai shi ƙungiyar matasa ta Real Madrid. A nan ne ya fara samun horo da gogewa.

  • Dalilin Da Ya Sa Muka Tafi Amurka Don Taron Tsaro – Gwamna Radda
  • Gwamnatin Tarayya Ta Umarci A Fara Karatun Digiri Da Yaren Tibi Da Nupe A Jami’o’i

Tauraronsa Ya Haska A Turai

Hakimi ya yi fice sosai lokacin da Real Madrid ta kai shi aro zuwa Borussia Dortmund. A nan ne ya nuna kalar ƙwarewarsa wajen murza leda: tare ƙwallo a matsayin ɗan wasa baya tare da kai-hari, gudu, da iya sarrafa kwallo.

ADVERTISEMENT

Daga Dortmund ya koma Inter Milan, inda ya samu sabbin dabarun sarrafa ƙwallo a fili, ya kuma taimaka wa ƙungiyar wajen samun manyan nasarori. Daga bisani ya koma Paris Saint-Germain (PSG), inda ya tauraronsa ya ƙara haskakawa sosai.

A PSG, Hakimi bai tsaya taka ƙwalla a matsayin ɗan baya ba kaɗai, yana taimakawa wajen zura ƙwallaye a ragar abokan hamayya, yana kai farmaki, kuma ya kasance ɗaya daga cikin manyan taurarin ƙungiyar.

LABARAI MASU NASABA

Arsenal Na Dab Da Ɗaukar Jeremy Monga Daga Leicester City

Za A Fara Buga Gasar Kofin Sarkin Gombe Bayan Masu Ruwa Da Tsaki Sun Cimma Matsaya

Ɗaga Martabar Tawagar ‘Yan Wasan Maroko

Hakimi na taka leda ne a tawagar ‘yan wasan Maroko, kuma wannan shi ne abin da ya fi alfahari da shi. A Gasar Cin Kofin Duniya ta 2022, ya taka muhimmiyar rawa da ta kai Maroko zuwa matakin kusa da na ƙarshe, wanda babban abun alfahari ne ga ƙasar da kuma Afrika.

Hakimi kuma mutum ne mai matuƙar son kasancewa iyayensa. Bayan buga wasanni, ya kan tafi ya rungumi mahaifiyarsa a filin wasa, wanda hakan ya a taɓa zuciyar masoyansa sosai.

Shekarar Da Ya Kafa Tarihi A PSG

A 2025, Hakimi ya taka wasa mai ban mamaki tare da PSG. Ya lashe gasar zakarun Turai ta Champions League, Ligue 1, Coupe de France, da UEFA Super Cup. Wannan gagarumar nasara ta sa ya doke fitattun ‘yan wasa kamar Mohamed Salah da Victor Osimhen, wajen lashe Gwarzon Ɗan Ƙwallon Afrika na 2025.

A jawabin karɓar kyautarsa, ya ce wannan lambar yabo “ba tawa ba ce ni kaɗai, ta dukkanin matasa maza da mata masu mafarkin zama ‘yan wasa a Afrika ce.”

Halayyarsa A Wajen Filin Wasa

A zahiri, Hakimi mutum ne mai nutsuwa da ladabi. Abokan wasansa suna yaba masa kan yadda halinsa da aiki tuƙuru yake. Ba ya son hayaniya ko jita-jita, aikinsa a fili shi ne yake bayyana wanw irin mutum ne.

Burin Da Ya Cimma

Zama Gwarzon Ɗan Ƙwallon Afrika a matsayin ɗan baya babban tarihi ne. Ya nuna irin ci gaban da Hakimi ya yi fatan samu a harkar ƙwallon ƙafa. Ya nuna cewa ko a ɓangaren ‘yan wasan baya, akwai gurbin taurari kamarsa.

Yanzu Hakimi yana da shekaru 27 kacal a duniya, amma ya kafa tarihin da zai daɗe ana tunawa da shi. Ɗan wasa ne da ke tsakanin Turai da Afrika, wanda ke nuna ƙwarewarsa a kowace nahiya ya tsinci kansa. Kuma babu shakka, labarinsa ya nuna yadda jajircewa da himma suka kai shi ga zama tauraro.

MASU ALAKA

Arsenal Na Dab Da Ɗaukar Jeremy Monga Daga Leicester City
Wasanni

Arsenal Na Dab Da Ɗaukar Jeremy Monga Daga Leicester City

June 4, 2026
Za A Fara Buga Gasar Kofin Sarkin Gombe Bayan Masu Ruwa Da Tsaki Sun Cimma Matsaya
Wasanni

Za A Fara Buga Gasar Kofin Sarkin Gombe Bayan Masu Ruwa Da Tsaki Sun Cimma Matsaya

June 3, 2026
Galatasaray Ta Sanya Farashin Yuro Miliyan 150 Kan Osimhen, Chelsea Ta Nuna Sha’awar Ɗaukarsa
Wasanni

Galatasaray Ta Sanya Farashin Yuro Miliyan 150 Kan Osimhen, Chelsea Ta Nuna Sha’awar Ɗaukarsa

June 2, 2026
Next Post
An Bude Dandalin Tunis Na Bunkasa Hadin Gwiwar Ayyukan Likitanci Tsakanin Sin Da Afirka

An Bude Dandalin Tunis Na Bunkasa Hadin Gwiwar Ayyukan Likitanci Tsakanin Sin Da Afirka

LABARAI MASU NASABA

Takunkumin Amurka Ya Haifar Da Mummunan Tasiri Ga Tsarin Samar Da Kayan Latironi Na Duniya

Takunkumin Amurka Ya Haifar Da Mummunan Tasiri Ga Tsarin Samar Da Kayan Latironi Na Duniya

June 4, 2026
Rikicin Manoma Da Makiyaya Ya Kashe Mutane 7, Ya Jikkata 6 A Bauchi

Rikicin Manoma Da Makiyaya Ya Kashe Mutane 7, Ya Jikkata 6 A Bauchi

June 4, 2026
Rikicin Manoma Da Makiyaya Ya Yi Sanadin Mutuwar Mutane 7 A Bauchi

Rikicin Manoma Da Makiyaya Ya Yi Sanadin Mutuwar Mutane 7 A Bauchi

June 4, 2026
Mun Kaɗu Matuƙa Kan Labarin Mutuwar ‘Yan Mauludi A Hanyar Saminaka – Gwamnan Kaduna

Gwamna Sani Ya Kashe Sama Da Naira Biliyan Ɗaya Kan Tallafin Ɗalibai A Kaduna – Kwamishina

June 4, 2026
Sin Ta Ware Kudi Har Yuan Biliyan 99.9 Domin Tallafawa Kula Da Lafiyar Yara A 2026

Sin Ta Ware Kudi Har Yuan Biliyan 99.9 Domin Tallafawa Kula Da Lafiyar Yara A 2026

June 4, 2026
Tasirin Nasarar Da Kasar Sin Ta Cimma A Fannin Kakkabe Matsanancin Talauci

Tasirin Nasarar Da Kasar Sin Ta Cimma A Fannin Kakkabe Matsanancin Talauci

June 4, 2026
Sabbin Ra’ayoyin Ci Gaba: Manufofin Zamani Na Zamanantarwa

Sabbin Ra’ayoyin Ci Gaba: Manufofin Zamani Na Zamanantarwa

June 4, 2026
Fargabar Satar Mutane Ya Sa An Rufe Makarantu A Abuja Da Mararaba

Fargabar Satar Mutane Ya Sa An Rufe Makarantu A Abuja Da Mararaba

June 4, 2026
Ana Gudanar Da Taron Masana Ilmin Harkokin Kasar Sin Karo Na Uku

Ana Gudanar Da Taron Masana Ilmin Harkokin Kasar Sin Karo Na Uku

June 4, 2026
Sin: Ya Kamata Tarayyar Turai Ta Dubi Huldar Tattalin Arziki Da Ciniki Tsakaninta Da Sin Bisa Daidaito

Sin: Ya Kamata Tarayyar Turai Ta Dubi Huldar Tattalin Arziki Da Ciniki Tsakaninta Da Sin Bisa Daidaito

June 4, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.