ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Thursday, June 25, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Achraf Hakimi: Sabon Angon Afrika A Harkar Ƙwallon Ƙafa

by Sadiq
7 months ago
Hakimi

Achraf Hakimi ba ɗan wasan baya ba ne kaɗai, fitaccen ɗan wasan Afrika ne wanda tauraronsa ya haska a duniya. A makon da ya gabata ne, ya lashe Gwarzon Ɗan Ƙwallon Afrika na 2025, wanda ya zama ɗan baya na farko cikin shekaru 52 da ya samu wannan lambar yabo.

Tarihin Rayuwarsa

An haifi Hakimi a Birnin Madrid na ƙasar Sifaniya a shekarar 1998, asalin iyayensa ‘yan ƙasar Maroko ne. Ya taso a unguwar talakawa da ke Getafe. Tun farkon ƙuruciyarsa yaro ne mai son taka leda, kuma bai daɗe ba ƙwarewarsa ta kai shi ƙungiyar matasa ta Real Madrid. A nan ne ya fara samun horo da gogewa.

  • Dalilin Da Ya Sa Muka Tafi Amurka Don Taron Tsaro – Gwamna Radda
  • Gwamnatin Tarayya Ta Umarci A Fara Karatun Digiri Da Yaren Tibi Da Nupe A Jami’o’i

Tauraronsa Ya Haska A Turai

Hakimi ya yi fice sosai lokacin da Real Madrid ta kai shi aro zuwa Borussia Dortmund. A nan ne ya nuna kalar ƙwarewarsa wajen murza leda: tare ƙwallo a matsayin ɗan wasa baya tare da kai-hari, gudu, da iya sarrafa kwallo.

ADVERTISEMENT

Daga Dortmund ya koma Inter Milan, inda ya samu sabbin dabarun sarrafa ƙwallo a fili, ya kuma taimaka wa ƙungiyar wajen samun manyan nasarori. Daga bisani ya koma Paris Saint-Germain (PSG), inda ya tauraronsa ya ƙara haskakawa sosai.

A PSG, Hakimi bai tsaya taka ƙwalla a matsayin ɗan baya ba kaɗai, yana taimakawa wajen zura ƙwallaye a ragar abokan hamayya, yana kai farmaki, kuma ya kasance ɗaya daga cikin manyan taurarin ƙungiyar.

LABARAI MASU NASABA

Trump Ne Zai Jagoranci Bayar Da Kofin Duniya A Wasan Ƙarshe – Infantino

Lionel Messi Ya Kafa Tarihin Wanda Yafi Kowa Zura Kwallaye A Tarihin Gasar Cin Kofin Duniya

Ɗaga Martabar Tawagar ‘Yan Wasan Maroko

Hakimi na taka leda ne a tawagar ‘yan wasan Maroko, kuma wannan shi ne abin da ya fi alfahari da shi. A Gasar Cin Kofin Duniya ta 2022, ya taka muhimmiyar rawa da ta kai Maroko zuwa matakin kusa da na ƙarshe, wanda babban abun alfahari ne ga ƙasar da kuma Afrika.

Hakimi kuma mutum ne mai matuƙar son kasancewa iyayensa. Bayan buga wasanni, ya kan tafi ya rungumi mahaifiyarsa a filin wasa, wanda hakan ya a taɓa zuciyar masoyansa sosai.

Shekarar Da Ya Kafa Tarihi A PSG

A 2025, Hakimi ya taka wasa mai ban mamaki tare da PSG. Ya lashe gasar zakarun Turai ta Champions League, Ligue 1, Coupe de France, da UEFA Super Cup. Wannan gagarumar nasara ta sa ya doke fitattun ‘yan wasa kamar Mohamed Salah da Victor Osimhen, wajen lashe Gwarzon Ɗan Ƙwallon Afrika na 2025.

A jawabin karɓar kyautarsa, ya ce wannan lambar yabo “ba tawa ba ce ni kaɗai, ta dukkanin matasa maza da mata masu mafarkin zama ‘yan wasa a Afrika ce.”

Halayyarsa A Wajen Filin Wasa

A zahiri, Hakimi mutum ne mai nutsuwa da ladabi. Abokan wasansa suna yaba masa kan yadda halinsa da aiki tuƙuru yake. Ba ya son hayaniya ko jita-jita, aikinsa a fili shi ne yake bayyana wanw irin mutum ne.

Burin Da Ya Cimma

Zama Gwarzon Ɗan Ƙwallon Afrika a matsayin ɗan baya babban tarihi ne. Ya nuna irin ci gaban da Hakimi ya yi fatan samu a harkar ƙwallon ƙafa. Ya nuna cewa ko a ɓangaren ‘yan wasan baya, akwai gurbin taurari kamarsa.

Yanzu Hakimi yana da shekaru 27 kacal a duniya, amma ya kafa tarihin da zai daɗe ana tunawa da shi. Ɗan wasa ne da ke tsakanin Turai da Afrika, wanda ke nuna ƙwarewarsa a kowace nahiya ya tsinci kansa. Kuma babu shakka, labarinsa ya nuna yadda jajircewa da himma suka kai shi ga zama tauraro.

MASU ALAKA

Trump Ne Zai Jagoranci Bayar Da Kofin Duniya A Wasan Ƙarshe – Infantino
Wasanni

Trump Ne Zai Jagoranci Bayar Da Kofin Duniya A Wasan Ƙarshe – Infantino

June 24, 2026
Lionel Messi Ya Kafa Tarihin Wanda Yafi Kowa Zura Kwallaye A Tarihin Gasar Cin Kofin Duniya
Wasanni

Lionel Messi Ya Kafa Tarihin Wanda Yafi Kowa Zura Kwallaye A Tarihin Gasar Cin Kofin Duniya

June 22, 2026
Ɗanwasa Thomas Partey Ya Yi Rashin Nasara A Kotun Canada
Wasanni

Ɗanwasa Thomas Partey Ya Yi Rashin Nasara A Kotun Canada

June 21, 2026
Next Post
An Bude Dandalin Tunis Na Bunkasa Hadin Gwiwar Ayyukan Likitanci Tsakanin Sin Da Afirka

An Bude Dandalin Tunis Na Bunkasa Hadin Gwiwar Ayyukan Likitanci Tsakanin Sin Da Afirka

LABARAI MASU NASABA

Zan Ware 10bn Don Inganta Ilimin Matasa Idan Na Ci Zabe – Atiku

‘Yan Nijeriya Ba Sa Bukatar ‘Yan Jarida Su Faɗa Musu Suna Jin Yunwa’ — Atiku

June 25, 2026
Dokar Sin Ta Gurfanar Da Masu Rajin Ballewar Kabilun Kasar Da Ke Kasashen Waje Ta Dace

Dokar Sin Ta Gurfanar Da Masu Rajin Ballewar Kabilun Kasar Da Ke Kasashen Waje Ta Dace

June 24, 2026
’Yan Kasuwa Na Kasashen Waje Sun Yaba Wa Yanayin Kasuwanci Na Sin

’Yan Kasuwa Na Kasashen Waje Sun Yaba Wa Yanayin Kasuwanci Na Sin

June 24, 2026
Yadda Uba Sani Ya Farfaɗo Da Asibitin Da Aka Yi Watsi Da Shi Tsawon Shekaru 40 – Hakimin Makarfi

Yadda Uba Sani Ya Farfaɗo Da Asibitin Da Aka Yi Watsi Da Shi Tsawon Shekaru 40 – Hakimin Makarfi

June 24, 2026
Dandalin DAVOS Na Bana: Fage Ne Da “Kirkire-Kirkiren Sin” Ya Sadu Da “Kyakkyawan Fatan Afirka”

Dandalin DAVOS Na Bana: Fage Ne Da “Kirkire-Kirkiren Sin” Ya Sadu Da “Kyakkyawan Fatan Afirka”

June 24, 2026
Binciken CGTN: Amfanarwa A Aikace Shi Ne Nagartaccen Ma’aunin Tantance Ainihin Kimar Sabbin Fasahohi

Binciken CGTN: Amfanarwa A Aikace Shi Ne Nagartaccen Ma’aunin Tantance Ainihin Kimar Sabbin Fasahohi

June 24, 2026
Kasar Sin Na Kara Zama Babban Ginshikin Ci Gaban Tattalin Arzikin Duniya Na Gaba

Kasar Sin Na Kara Zama Babban Ginshikin Ci Gaban Tattalin Arzikin Duniya Na Gaba

June 24, 2026
Tsaro: Dasuki Ya Bukaci Tinubu Ya Gyara Alaka Da Nijar Domin Kare Iyakokin Arewa-Maso-Yamma

Tsaro: Dasuki Ya Bukaci Tinubu Ya Gyara Alaka Da Nijar Domin Kare Iyakokin Arewa-Maso-Yamma

June 24, 2026
Sabbin Ministoci

Kafa ‘Yansandan Jihohi: Majalisa Ta Amince Da Tsarin ‘Yar Tinƙe Wajen Kaɗa Ƙuri’a 

June 24, 2026
Sin Ta Gabatar Da Tsarin Karfafa Kwarin Gwiwar Kamfanoni Masu Jarin Waje

Sin Ta Gabatar Da Tsarin Karfafa Kwarin Gwiwar Kamfanoni Masu Jarin Waje

June 24, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.