Tsohon Mataimakin Shugaban Ƙasa, Atiku Abubakar, ya lashe zaɓen fidda-gwani na jam’iyyar ADC gabanin zaɓen 2027.
Jam’iyyar ta ce Atiku ya samu ƙuri’u 1,846,370, inda ya doke tsohon gwamnan Jihar Ribas, Rotimi Amaechi, wanda ya samu 504,117.
Ɗan kasuwa Mohammed Hayatu-Deen ya zo na uku da ƙuri’u 177,120.
A jawabinsa bayan sanar da sakamakon, Atiku ya yaba wa ADC kan gudanar da zaɓe bisa dimokiraɗiyya, yana mai cewa dimokiraɗiyya na ci gaba da da samu waje a cikin jam’iyyar.
Shugaban ADC na ƙasa, Sanata David Mark, ya ce an gudanar da zaɓen cikin gaskiya da adalci, duk da cewa akwai buƙatar ƙara yin gyara.
Sai dai Amaechi ya ƙi amincewa da sakamakon, yana zargin an tauye wa wasu masu jefa ƙuri’a haƙƙinsu na yin zaɓi, yayin da Hayatu-Deen shi ma ya nuna damuwa kan zargin maguɗin zaɓe.
Bayan kammala zaɓen, Atiku ne zai wakilci ADC a zaɓen shugaban ƙasa na 2027.














Discussion about this post