Tsohon Daraktan Yaɗa Labarai na Rundunar Sojin Nijeriya, Manjo Janar Rabe Abubakar (mai ritaya), ya rasu yayin da yake tsare a hannun ‘yan bindiga bayan sace shi tare da matarsa a Jihar Katsina. An sace Manjo Abubakar ne a ranar 30 ga Mayu a kan hanyar Katsina–Matazu yayin da yake tafiya zuwa garinsu tare da matarsa.
Rahotanni sun nuna cewa ‘yan bindigar sun tare motarsu ne a yankin Matazu tare da yin awon gaba da su zuwa cikin daji, yayin da direbansu ya tsira duk da samun raunin harbi. Bayan sace su, maharan sun fitar da bidiyo suna neman a sako wasu mutane uku da aka kama tare da mayar musu da shanunsu a matsayin sharaɗin sakin Manjon da matarsa.
Kafin rasuwarsa, Abubakar ya taɓa zama ɗaya daga cikin fitattun kakakin rundunar soji, inda ya taka muhimmiyar rawa wajen isar da bayanan tsaro ga jama’a. Rasuwarsa ta sake jaddada yadda matsalar tsaro ke ci gaba da barazana ga rayukan jama’a har da manyan tsofaffin jami’an tsaro.
Lamarin ya sake tayar da hankalin al’umma kan ƙaruwar hare-haren ‘yan bindiga a Arewa maso Yamma, musamman a Katsina, inda garkuwa da mutane da hare-hare a kan manyan hanyoyi ke ci gaba da yawaita.















Discussion about this post