Isa Ashiru, tsohon ɗan takarar gwamna a jam’iyyar PDP, ya lashe tikitin takarar gwamna na jam’iyyar ADC a Jihar Kaduna gabanin zaɓen 2027.
Ya samu ƙuri’u 86,113 inda ya doke abokin takararsa, Jafaru Sani, wanda ya samu ƙuri’u 29,580.
Sauran ‘yan takara da suka shiga zaɓen, ciki har da Muhammad San-Bello, Ahmed Tijjani da Shuaibu Mikati.
Ashiru ya taɓa tsayawa takarar gwamna a 2019 da 2023 a jam’iyyar PDP, amma ya sha kaye a duka zaɓukan biyu.
Wasu ‘yan takarar Majalisar Wakilai na ADC a Kaduna sun ƙi amincewa da sakamakon zaɓen fidda-gwanin, suna zargin rashin gaskiya tare da neman a sake duba tsarin.
Da wannan nasara, Ashiru zai wakilci ADC a zaɓen gwamnan Kaduna na 2027.















Discussion about this post