Shin ko mene ne abun da ya hana nahiyar Afirka samun ci gaban tattalin arziki mai dorewa? Amsa a nan ita ce tsarin hada-hadar kudi na duniya da ya kasance karkashin jagorancin kasashen yamma, kamar yadda dimbin shugabannin kasashen Afirka suka bayyana, wajen wani taron kolin da ya gudana a kasar Kenya a kwanan baya.
A wajen taro mai taken “ciyar da Afirka gaba”, da shugabanni da manyan jami’ai na kasashe fiye da 30 dake nahiyar Afirka suka halarta, shugaban kasar Kenya William Ruto, ya fara da gabatar da ra’ayinsa cewa, tsarin hada-hadar kudi da ake amfani da shi a duniya yana hana jari shiga cikin nahiyar Afirka.
Sa’an nan, a nasa jawabi, shugaban kasar Najeriya Bola Tinubu shi ma ya ce, tsarin hada-hadar kudi na duniya yana taimakawa durkushewar masana’antu a nahiyar Afirka.
Shugaban ya yi tambaya cewa, “Yayin da kasashen Afirka ke neman cin bashi, a kan bukace su da su biya kudin da ya ninka na yankunan Turai, da Asiya, da arewacin Amurka, har da ninki 5 zuwa 10, to, ta yaya masana’antun kasashen Afirka za su iya takara da takwarorinsu na wadannan yankuna a karkashin wannan yanayi?”Batun da shugabannin suka ambata na nufin wahalar samun bashi da kasashen Afirka ke fuskanta, sakamakon yadda hukumomin tantance matsayin lamuni na kasasashen yamma, suka bayyana nahiyar Afirka a matsayin “Mai hadarin gamuwa da matsala wajen biyan bashi”.
Hakika kasar Amurka da sauran kasashen dake yammacin duniya sun tsara tsarin nan na tantance matsayin lamuni ne don tabbatar da moriyar kansu, inda suka ba kansu makin lamuni da ya fi na kasashe masu tasowa, ta yadda jari da riba za su rika kwarara zuwa cikin kasuwannin cikin gidansu, tare da lahanta moriyar kasashe masu tasowa, ta hanyar jefa su cikin “tarkon bashi”.
A cewar shugaba Tinubu na Najeriya, a shekarar 2026 da muke ciki, kasarsa za ta kashe dalar Amurka kimanin biliyan 11.6 wajen biyan bashin da ake binta, adadin da zai kai rabin yawan kudin da kasar za ta iya samu a duk shekara.
Ra’ayi daya da shugabannin kasashen Afirka suka cimma a wannan karo, dangane da tsarin hada-hadar kudi na duniya, shi ma ya nuna cewa, maganar “tarkon cin bashin kasar Sin”, da kafofin yada labarai na kasashen yamma ke kokarin yayatawa a duniya karya ce. Saboda a zahiri, dalilin da ya sa ake samun “tarkon bashi” shi ne tsarin hada-hadar kudi na duniya, wanda ya shafi ikon hukumomin kasashen yamma na tantance matsayin lamuni, maimakon wata kasa da ke son samar da rance ga kasashen Afirka.
Alal hakika, shi ma hamshakin dan kasuwar Najeriya Aliko Dangote, ya yabawa kasar Sin bisa saukin kai a fannin samar da rance, lokacin da ya yi hira da manema labaru a kwanan baya.
Ya ce, kamfanonin kasar Sin masu samar da injuna sun yarda da kamfanonin Afirka su samu injunan da suke bukata, bisa biyan wani bangare na kudin injuna, daga baya su biya bashi cikin lokaci daban daban, maimakon tsarin kamfanonin kasashen yamma na biyan dukkan kudi nan take ba tare da wani jinkiri ba.
A cewar Dangote, hakan ya sa kasar Sin samar da mafi yawan gudunmowa ga ci gaban masana’antu da kasuwanci na kasashen Afirka.Ta haka muna iya gane cewa, cin bashi mataki ne da ya wajaba ga yunkurin ciyar da masana’antu da kasuwanci gaba.
Sai dai ko za a fada cikin “tarkon bashi” ya danganta da niyyar samar da bashi: Ana samar da bashi ne don kwace dukiya da samun riba fiye da kima.
Ko kuma ana samar da kudin bashi a matsayin wani taimako, sakamakon yadda ake neman kulla huldar hadin gwiwa ta dogon lokaci, da tabbatar da cin moriyar juna da damar samun ci gaba tare.
A zahiri, tsarin hada-hadar kudi na duniya karkashin jagorancin kasashen yamma ya nuna wani yanayi na neman kwace kudi daga kasashe masu tasowa, kuma wannan ya sa kasashen Afirka fara mayar da martani.
A wajen taron koli na wannan karo, kasashen Afirka sun sanar da cewa, za a rage dogaro kan kudaden dalar Amurka, da Euro, gami da tsarin hada-hadar kudi na kasashen yamma, tun kafin shekarar 2029.
Inda matakan da suka tanada sun hada da kafa wani kawance na tantance matsayin lamuni na nahiyar Afirka kafin shekarar 2027, da neman cimma burin yin amfani da kudin na kashin kai wajen gudanar da kaso 50% na cinikin da ake yi tsakanin kasashen Afirka, da kaso 30% na cinikin da kasashen Afirka suke yi da kasashe na sabbin kasuwanni, ciki har da kasar ta Sin a shekarar 2029.
Ta hanyar kara dogaro da kai a fannin hada-hadar kudi, kasashe Afirka sun bayyana niyyarsu ta kawar da shingen da ya hana su samun ci gaba daga tushe.
Batun nan ya yi daidai da maganar da shugaba Tinubu ya fada wajen taron wannan karo, inda ya ce, “Dole ne a daidaita tsarin hada-hadar kudi na duniya, in ba haka ba za a kauce masa.” (Bello Wang)














Discussion about this post